Sashe 106
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 3 min read
"Nurse Haleema pls where is your phone?" Aunty ta tambayi d'aya daga cikin nurse d'in cikin girmamawa tace mata tana a station tasa caji tace mata in ba damuwa ta d'an aro mata da sauri tace to, har ta nufi kopar fita Aunty ta dakatar da ita ta tambayi akwae karatun Qur'ani a ciki da sauri tace eh sosae tace to ta kawo mata, bada jimawa ba ta dawo lokacin Haisam nata yi ma Fatun Addu'o'i ya rurruk'e ta, bayan ta kawo wayar Aunty tasa ta kunna karatu tace to, a saman drawer din gadon Fatun aka d'aura wayar karatun ya fara tashi daga Fatiha bayan ta k'are ya shiga baqara Aunty ta tambayi Fatun ta iya surar da ake yi tun kafin ta bada amsa Haisam yace mata eh ta jinjina kai,matsowa tayi ta kai hannu ta dafa goshin Fatun tace mata ta daure su rink'a bi tare ta jinjina mata kai tana ta nishin ciwo idanunta sunyi ja luhu luhu kanta a bud'e manyan kitson da Iya tayi mata guda goma sun bayyana, sosae tayi k'arfin halin bin karatun tana yi tana tsayawa sai kuma taci gaba Aunty ma na bi haka Nurse Haleema, zuciyar Haisam ce ta raya mashi ya tashi yayi sallar Nafila tunda lokacin kar6ar Addu'a ne, yin tunanin yasa shi mik'ewa da sauri Fatuu na ganin tafiya zai yi ta k'ank'ame hannun shi ya juyo ya kalleta cikin muryar wanda ke cikin rad'ad'in ciwo ta fara fad'in "Don Allah Ya Haisam kada ka tafi ka barni....ka tsaya in ma Mutuwa zan yi in mutu a gaban ka don Allah" sosae Maganar tata ta k'aryar mashi da zuciya amman sai yay k'arfin halin komawa ya zauna yasa hannun shi guda yana shafa kanta ta sigar lallashi yace ta daina fad'in hakan ta kwantar da hankalinta in sha Allahu ba abunda zai same ta zata haihu lafiya yanzu so yake yaje yayi salla sai yayi mata Addu'a sosae he's sure in sha Allah Allah zai amsa, shiru tay tana cigaba da nishi yace bari yace ta daure taci gaba da bin karatun ta d'aga mashi kai, mik'ewa yay slowly ya zame hannun shi daga cikin nata ya juya zai tafi Aunty tace mashi yaje Office d'inta sai yayi sallar acan ya d'aga mata kai, har ya kai k'opa idanun Fatuu na akan shi yana kama handle zai bud'e ya dakata ya juyo ya kalleta idanun su suka shiga cikin na juna gaba d'aya abu iri d'aya zuciyoyin su ke ayyana masu, tunda Fatuu ta fara ciwon bata yi k'walla ba sai yanzu suka zubo mata sharr ta fara yamutsa fuska tana kuka still kallonta Haisam ke yi shima kawai sai jin k'walla yay sun zobo mashi a tashi Fuskar da sauri ya juya ya bud'e kopar ya fice,