Sashe 210
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A bangaren Haisam kuwa tuni Kamfaninshi ya ƙara ha6aka sosae yanzu ana ƙera wasu abubuwan ba iya kwamfutoci ba yanzu harda su Tv da kuma wayoyi, a lokacin arzuƙin shi ya ƙaru sosae don har ya ƙara buɗe wasu rassa na Kamfaninshi a Lagos, PortHarcourt, Kano da kuma Sokoto yana da kuma burin ƙara buɗewa a wasu States ɗin in Allah ya yarda, a yanzu Haisam ya zama Billionaire wanda yana ɗaya daga cikin Manyan masu kuɗin ƙasa don har private jet ya mallaka wato jirgin kanshi wanda ake hidimar iyalinshi da kuma Kamfanoninshi, daga baya aka fara yin hayar jirgin ganin akwae riba yasa Haisam ɗin yayi ma Dad dinshi Magana kan su haɗa su sayi wani jirgin na haya ya amince da hakan koda Sameer yaji zancen siyan jirgin hayar shima sai ya nuna yana ra'ayin saka hannun jari haka Hajiya Maryam ma dama duk suna da hannayen jari a Kamfanin shi na Technology, daga baya suka buɗe kamfanin sufurin jirage mai suna HaiFat Air wanda a yanzu suke da jirage guda ukku biyu manya wanda har yan Hajji ake kaiwa dasu sai ɗaya ƙarami wato private jet suma jiragen suna niyyar ƙara wasu da yardar Allah, A cikin shekaru biyar ɗin nan a duk shekara Haisam sai ya kai wasu a cikin dangi Makka, a shekarar farko daya fara kai mutane makka ne yace ma Fatuu ta bada mutum biyu cikin danginta ta bada sunan Gwaggo da kuma Kawu Amadu su Gwaggo za'a sake sauke farali sosae tayi farinciki, Hajiya na jin zancen tafiyar Amadu Hajji itama ta biya ma Tukur wato Tk Har Haisam yace ta bari shekara mai zuwa zai biya mashi tace ai shida Amadu kamar yan biyu suke bai ga ko aure tare sukai ba ya bari ta biya mashi ai duk ɗaya ne, da wata shekara ta zagayo ya sake cewa ta bada mutum biyu sai ta bada Yaya da kuma kishiyarta Mairo sannan ita kuma da kuɗinta ta biya ma Aminiyarta Haulat, da rabon dai Fatuu ita zata kai Yaya Makka a lokacin ƙurucyarta ta ta6a ce ma Haisam in ta girma tayi kuɗi zata kai kowa Makka amman banda Yaya saboda ta tsaneta har yayi mata Nasiha kan muhimmancin yafiya, Sosae su Mero sukai farincikin biya masu Makka saidai ita Yaya akwae abunda ke damunta a cikin rai shine hakkin Mahaifiyar Baffan su Fatuu dake a kanta don tun Maganar da Mero ta ta6a yi mata a Abuja kan hakan bata manta ba, ƙarshe samun Mairo tayi ɗakinta cike da damuwa tace mata ita tana tsoron taje tayi aikin Hajjin Allah yaƙi kar6a saboda hakkin A'isha dake kanta, shawara Mairo ta bata kan taje ta samu Baffansu Fatuu ta roƙe shi yafiya ta roƙeta kan ta rakata, tare suka iske Mahaifinsu Fatuu a bangarenshi wanda yanzu ya koma babban falo da Bedroom da suka sha kayan alatu don Haisam ya bashi kuɗi masu yawa Fatuu ma ta ƙara mashi an gyara part ɗin nasu ya koma babban Flat saida aka ƙara faɗaɗa shi, sauran bangarorin ma anyi gyare gyare don yanzu gaba ɗayan tsakar gidan siminti ne ko ina sannan an zagaye gidan da katangar bulon siminti haka gaban gidan ma ya koma irin na yan birni harda gate, fadar da Baffa ke zama itama ta koma irin ta zamani, bayan sun zauna anyi gaishe gaishe shiru Yaya tayi ta rasa ta ina zata fara sai Mairo ce ta fara magana tace mashi dama Yaya ce tazo neman yafiya a wurinshi kan abubuwan da suka faru a baya ta juya kan Yaya tace tayi magana, cikin karyayyar murya ta shiga roƙonshi akan abubuwan data yi masu a baya ta bayyana mashi ta zalunci mahaifiyarshi don ita tayi mata asiri duk gidan aka tsaneta harda arɗo wannan ne yay silar ta kamu da ciwon zuciya har ta mutu haka shima tay ta zaluntar shi bayan rasuwarta ganin arɗo ya damu dashi shima tayi mashi asiri ya daina ji da shi sai bayan daya girma ne da yake shi mai yawan ibada ne sosae sai ya zama ko tayi asirin bai kamashi hakan yasa soyyyarshi ta dawo ma arɗo sai kuma ta rinƙa yi mashi makirci haka iyalinshi ma ta ɗauki karan tsana ta ɗaura masu, shiru Baffa yayi kan shi a ƙasa yayinda ƙwaƙwalwarshi ta shiga dawo mashi da lokacin don bazai ta6a mantawa da irin rayuwar ƙuncin da mahaifiyarshi tayi ba a gidan lokacin yanada ƙuruciya har zuwa mutuwarta lokacin haka ya rinƙa kuka yana roƙon shima Allah yasa ya mutu ya bita, kawai saboda yana da haƙuri sosae da kuma kawaici irin na fulani yasa bai nuna masu komai amman ba wai don ya manta ba, saukkowa Yaya tayi kan carpet ta duƙa cikin kuka ta shiga bashi haƙuri tana mashi magiyar ya yafe mata, Mairo ce da idanunta suka ciko da ƙwalla cikin kwantar da murya ta shiga roƙonshi ya yafe mata Don Allah duk irin abunda tayi mashi gashi nan bai hana rayuwarshi yin albarka ba ƙarshe ma gaba ɗayansu sun koma karkashin kulawarshi yayi koyi da mai sunan shi wato manzon Allah (S.A.W) wanda haƙuri da yafiya halin shi ne, ɗagowa yay idanunshi sun yi ja sun cika da ƙwalla cikin karyayyar murya yace shikenan ya yafe mata sai taita istigfari ta roƙi Allah ya yafe mata abunda tayi ma Mahaifiyar shi, godiya sosae ta shiga yi mashi fuska jage jage harda su majina ta shiga yi ma Mahaifiyar tashi Addu'o'i a hankali yake amsawa daga baya suka tafi, bayan tafiyarsu kuka sosae ya shiga yi yana tunawa da mahaifiyarshi tare da yi mata Addu'a, bayan Yaya ta koma ɗaki saida ta kira Fatuu a waya itama ta roƙeta yafiya kan abubuwan da tayi mata na tsanarta da tayi tana murmushi tace mata ba komai ai ya riga ya wuce ta yafe mata taita mata godiya da Addu'oi, sai lokacin Yaya taji hankalinta ya ɗan kwanta da tafiya Hajjin da zatayi tun daga ranar kullum da cazhaba zaka ganta tana ta istigfari.
Ta dalilin Fatuu yanzu yan ƙauyansu suna karatun boko sosae, a gidansu ma an daina yi ma mata auren wuri sai sunyi boko har Abuja yan'uwan nasu suke zuwa hutu wurinsu inda rabo ƙilan wasu su ƙara samun mazaje a can. A can Katsina yanzu Foundation ɗin su Fatuu ya ha6aka sosae anata taimakon mutane yanzu a unguwarsu Gwaggo ita ta koma matsayin Hajiyar Sanata sosae take taimakon Makwabtanta, rayuwa dai ta inganta ga dukkan bangarorin. Ta dalilin Addu'oin da wanda Haisam ke kaiwa Hajji ke mashi sosae hakan yake ƙara ha6aka arzukin shi wanda yanzu shi kanshi Haisam ɗin bai sai iya adadin dukiyarshi ba har gida ya gina ma Abbas ya kuma kaishi Makka harda Feenah sannan ya ɗauki nauyin karatun Abdul wanda yanzu ya girma, a bangaren Aunty Mareeya itama Sameer ya gina masu babban gida har sun koma kuma duk sunje Hajji suma. Bayan wani lokaci Haisam yasa aka fara gina ma su Fatuu Asibiti anan Abuja wato private Hospital ita da Fanan wanda aka yanke saka mashi HAIFAT SPECIALISTS HOSPITAL sai fatan Allah yasa a gama lafiya a kuma buɗeshi lafiya yasa kuma mutane su amfana, Amin.
Fatuu zaune a gaban madubi da daddare tana yin shafa bayan ta fito daga wanka yayin da Haisam ke zaune a saman gadonta ya ɗaura Laptop a saman table ɗin gaban gado yana daddanawa da alama wani aikin yake jikinshi sanye da robe haka idanunshi na sanye cikin glass ya ƙara manyanta saidai duk da haka ba sosae jikinshi ya nuna ba saboda har yanzu yana motsa jiki sosae, kamar an jefo Esha ta faɗo cikin ɗakin tana ƙwala ma Fatuu kira tana faɗin "Auntyyy!" itama yanzu ta ƙara girma don tana shekara ta sha huɗu duk da bata da tsawo sosae sak irin jikin Fatuu tana yarinya gareta,
"Esha! Wai sai yaushe zaki hankali ne, didn't i warn you to always say salaam before entering into a place???" a fusace Fatuu tay mata Maganar ta ɗaure fuska, tura baki Esha ɗin tayi tana ɗan murmushi tare da noƙe kai tace "to Sorry Aunty mantawa nike bari inje inyi salaam ɗin" tayi maganar tare da juyawa ta nufi kopa, bayan ta fita daddagewa tayi ta kwaɗa wata uwar sallama har saida Haisam ya ɗan yamutsa fuska Fatuu kuma ta girgiza kai kafin tace wani abu Esha ɗin ta ƙara kware baki ta rafko wato sallamar tare da faɗin "Aunty in shigo???" ba arzuƙi gudun ta sake yin wata da sauri Fatun tace mata ta shigo, shigowa tayi tana dariya Fatuu ta wurga mata harara, bayan tazo gabanta tace mata miya kawota ɗakinta yanzu cikin zazzaƙar muryarta tace "Momy ce tace ki bata charger ɗin phone en ki in baki using dashi mun shanye mata caji zata saka nata ya ƙiya kafin tomorrow Dad ya kawo mata wani" yadda kasan abun faɗa yadda tayi Maganar, maida kanta tayi kan madubi tana cigaba da shafar ta tace mata gata can jikin socket wurin bedside drawer taje ta ɗauka, maimakon taje ta ɗaukan sai ta tsaya tana kallon fuskar Fatun ta cikin madubi tana wani murmushi tace "Aunty Daddy kike ma makeup?" dakatawa Fatuu tay ta watsa mata harara, dariya Esha ɗin tayi tace "ai nasan Dad kike mawa don ke Babynshi ce....." tsawa Fatun ta daka mata "Esha! Will you go and take the charger ko zaki tsaya kina surutun banza ne!!" da sauri ta wuce tana dariya, tana zuwa saitin Haisam ta furta "My lovely Dad" dagowa yay ya kalleta yay mata murmushi tare da miƙa mata hannu suka kashe yace taje ta ɗauki charger din ana jiranta tace to, bayan ta ɗauko cazar ta nufi hanyar fita, har ta kusa fita ta tsaya da ƙarfi ta furta "Babyn Daddy kin yi kyau...." robar mai Fatuu ta wawuro Esha na ganin haka ta fice da gudu tana dariya, tsoki Fatuu tayi tare da girgiza kai idonta akan madubi ta furta "i think Aisha needs to see a psychiatrist gaskiya" murmushi Haisam yay ba tare daya kalleta ba can idonshi akan screen ɗin kwamfuta yace mata saboda mi, juyawa tay da sauri ta kalleshi tace "baka ga yadda take behaving abnormal bane, wataƙil in aka kaita aka binciki ƙwalwarta aga tana da problem",
Ta dalilin Fatuu yanzu yan ƙauyansu suna karatun boko sosae, a gidansu ma an daina yi ma mata auren wuri sai sunyi boko har Abuja yan'uwan nasu suke zuwa hutu wurinsu inda rabo ƙilan wasu su ƙara samun mazaje a can. A can Katsina yanzu Foundation ɗin su Fatuu ya ha6aka sosae anata taimakon mutane yanzu a unguwarsu Gwaggo ita ta koma matsayin Hajiyar Sanata sosae take taimakon Makwabtanta, rayuwa dai ta inganta ga dukkan bangarorin. Ta dalilin Addu'oin da wanda Haisam ke kaiwa Hajji ke mashi sosae hakan yake ƙara ha6aka arzukin shi wanda yanzu shi kanshi Haisam ɗin bai sai iya adadin dukiyarshi ba har gida ya gina ma Abbas ya kuma kaishi Makka harda Feenah sannan ya ɗauki nauyin karatun Abdul wanda yanzu ya girma, a bangaren Aunty Mareeya itama Sameer ya gina masu babban gida har sun koma kuma duk sunje Hajji suma. Bayan wani lokaci Haisam yasa aka fara gina ma su Fatuu Asibiti anan Abuja wato private Hospital ita da Fanan wanda aka yanke saka mashi HAIFAT SPECIALISTS HOSPITAL sai fatan Allah yasa a gama lafiya a kuma buɗeshi lafiya yasa kuma mutane su amfana, Amin.
Fatuu zaune a gaban madubi da daddare tana yin shafa bayan ta fito daga wanka yayin da Haisam ke zaune a saman gadonta ya ɗaura Laptop a saman table ɗin gaban gado yana daddanawa da alama wani aikin yake jikinshi sanye da robe haka idanunshi na sanye cikin glass ya ƙara manyanta saidai duk da haka ba sosae jikinshi ya nuna ba saboda har yanzu yana motsa jiki sosae, kamar an jefo Esha ta faɗo cikin ɗakin tana ƙwala ma Fatuu kira tana faɗin "Auntyyy!" itama yanzu ta ƙara girma don tana shekara ta sha huɗu duk da bata da tsawo sosae sak irin jikin Fatuu tana yarinya gareta,
"Esha! Wai sai yaushe zaki hankali ne, didn't i warn you to always say salaam before entering into a place???" a fusace Fatuu tay mata Maganar ta ɗaure fuska, tura baki Esha ɗin tayi tana ɗan murmushi tare da noƙe kai tace "to Sorry Aunty mantawa nike bari inje inyi salaam ɗin" tayi maganar tare da juyawa ta nufi kopa, bayan ta fita daddagewa tayi ta kwaɗa wata uwar sallama har saida Haisam ya ɗan yamutsa fuska Fatuu kuma ta girgiza kai kafin tace wani abu Esha ɗin ta ƙara kware baki ta rafko wato sallamar tare da faɗin "Aunty in shigo???" ba arzuƙi gudun ta sake yin wata da sauri Fatun tace mata ta shigo, shigowa tayi tana dariya Fatuu ta wurga mata harara, bayan tazo gabanta tace mata miya kawota ɗakinta yanzu cikin zazzaƙar muryarta tace "Momy ce tace ki bata charger ɗin phone en ki in baki using dashi mun shanye mata caji zata saka nata ya ƙiya kafin tomorrow Dad ya kawo mata wani" yadda kasan abun faɗa yadda tayi Maganar, maida kanta tayi kan madubi tana cigaba da shafar ta tace mata gata can jikin socket wurin bedside drawer taje ta ɗauka, maimakon taje ta ɗaukan sai ta tsaya tana kallon fuskar Fatun ta cikin madubi tana wani murmushi tace "Aunty Daddy kike ma makeup?" dakatawa Fatuu tay ta watsa mata harara, dariya Esha ɗin tayi tace "ai nasan Dad kike mawa don ke Babynshi ce....." tsawa Fatun ta daka mata "Esha! Will you go and take the charger ko zaki tsaya kina surutun banza ne!!" da sauri ta wuce tana dariya, tana zuwa saitin Haisam ta furta "My lovely Dad" dagowa yay ya kalleta yay mata murmushi tare da miƙa mata hannu suka kashe yace taje ta ɗauki charger din ana jiranta tace to, bayan ta ɗauko cazar ta nufi hanyar fita, har ta kusa fita ta tsaya da ƙarfi ta furta "Babyn Daddy kin yi kyau...." robar mai Fatuu ta wawuro Esha na ganin haka ta fice da gudu tana dariya, tsoki Fatuu tayi tare da girgiza kai idonta akan madubi ta furta "i think Aisha needs to see a psychiatrist gaskiya" murmushi Haisam yay ba tare daya kalleta ba can idonshi akan screen ɗin kwamfuta yace mata saboda mi, juyawa tay da sauri ta kalleshi tace "baka ga yadda take behaving abnormal bane, wataƙil in aka kaita aka binciki ƙwalwarta aga tana da problem",