← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 211

Sashe 49

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

...........Cikin tashin hankali yake jijjigata yana kiran sunanta, Abbas ne ya d'aukko robar ruwa bayan ya bud'e ya mik'a ma Haisam ya tara mashi hannun shi ya zuba mashi, sau biyu ya shafa mata amman ba alamar zata farfad'o, Najeeb ne da shima fuskar shi ta nuna tashin hankali yace bai kamata su tsaya suna wasting time ba ai rushing d'in ta hospital, Na'eem ne yace akwae wani private hospital daya sani bada nisa sosae ba, yana rufe baki Abbas yace ma Haisam ya d'aukko ta ya nufi hanyar fita Hall d'in da sauri sauri gudu gudu, d'agota Haisam yay ya d'auketa suka nufi hanyar fita dasu Najeeb, suna fita Abbas ya iso da Mota bakin wurin Najeeb ya bud'e baya Haisam ya saka ta ciki shima ya fara k'ok'arin shiga lokacin Laila ta k'araso hankali a tashe ta shiga tambayar wai mi ya faru da ita don Abbas ya sanar mata game da fad'uwar da tayi da ya fito, Najeeb ne yace hakanan suka ga ta fad'i, Na'eem ne ya shiga driver seat Saboda shi yasan Asibitin Najeeb da Abbas suka nufi inda Motocin su suke Abbas ya shiga Motar Na'eem haka Laila ma da gaba d'aya ta gama rud'ewa, a saman cinyoyin shi ya d'aura kan ta ya shiga shafa face d'inta yana kiran sunanta duk hankalin shi ya tashi, tashin Motar Na'eem yay bayan ya juya ya tunkari gate d'in wurin da gudu Motocin su Najeeb suka rufa masu baya, suna a kan hanya Laila ta d'aukko wayarta ta shiga kiran Mom d'in su, bayan tayi picking tun kan tayi magana cikin Muryar rud'u tace mata gasu a hanyar Asibiti, tambayar ta tay mi zasu je yi Asibiti tace mata Bride d'in Big bro ce hakanan ta yanke jiki ta fad'i, daga muryar Mom d'in zaka fahimci ba k'aramar razana tayi ba lokacin da ta sake maimaita abunda Lailar tace mata, tambayar ta tayi to miya faru da ita ne Fuskar Laila a yamutse kaman zatai kuka tace "Wllh ba abunda ya same ta kawae ta mik'e za'a taho gida ne aka ga ta yanke jiki ta fad'i" tambayar ta tayi an yayyafa mata ruwa tace mata eh an shafa mata har sau biyu amman bata ko motsa ba, salati Mom ta rafka a kid'ime ta tambayi wane Hospital zasu tace mata itama bata sani ba Abokin big bro ne yake jagorantar su shine yasan Asibitin, tun kafin ta rufe baki Mom d'in ta katse Wayar, hannu ta kai ta dafe gaban kanta tana salati Hajiya Zainab dake zaune duk taji abunda suke Magana akai itama daga yanayin fuskarta akwae alamun tashin hankali, tambayarta tayi miya faru da matar Son d'in tayi mata bayanin da Laila tayi mata, jinjina kai tayi tace to Allah yasa lafiya ta yuwu stress ne ya mata yawa Mom dake kallon ta tace to Allah yasa,

kiran Senator tayi a waya saida ta kusa katsewa sannan yay picking, saida ta bashi hak'uri na tashin shi da tayi don tasan in ba bacci yake ba wayar bazata dad'e tana ringing ba batare da ya d'auka ba, ce mata yay ba komai Allah yasa dai lafiya cikin yar rawar murya ta sanar dashi abunda ke faruwa cikin daidaita natsuwa don kada ta tada mashi hankali, salati shima yayi ya tambayi asibitin da suka tafi ta fad'i mashi yadda Lailan tace yace Ok bari ya kira Son d'in, kiran Nameer Laila tayi a tunaninta ko basu kai gida ba don basu dad'e da rabuwa ba, ya tsayar da Motar kenan gaban Entry Hall kiran ya shigo, yana yin picking ta sanar dashi abunda ya faru cike da Al'ajabi ya maimata abunda tace su Fauzy dake niyyar fita daga cikin Motar cak suka tsaya suna sauraren shi, bayan ya gama wayar har suna had'a baki wurin tambayar shi abunda ke faruwa ya sanar masu, gaba d'ayan su razana sukai kar ma Mino taji gaba d'aya ta zaro ido kirjinta na mata wani irin bugu jin Adda Fatuu d'inta ta fad'i, Jidderh ce ta rok'e shi suje Hospital d'in yace Ok duk suka rufe kopopin Motar yaja suka tafi, tuni Mino ta fara kuka tana fad'in Allah yasa Adda Fatuu ba mutuwa tayi ba irin na mamanta, duk da su Fauzy na cikin tashin hankali haka suka shiga rarrashinta harda Nameer yace mata ta kwantar da hankalinta in sha Allah ba abunda zai sameta suyi mata Addu'a duk suka jinjina kai, nan fa Mino ta shiga yin Addu'oin a bayyane suna amsawa da Amin can ta kai hannu cikin jakarta ta fiddo wayarta ta shiga kiran gwaggo, lokacin da kiran ya shiga su gwaggon duk sunyi bacci, saida ya kusa katsewa ta farka lokacin data d'auki wayar kiran ya yanke, ganin mai kiran nata ta ambaci Mino to lafiya kira a wannan lokacin, tana niyyar kira saiga wani kiran ya shigo da sauri ta d'aga tun bata ji mi zata ce ba saida gabanta ya fad'i, cikin kuka ta sanar mata Gwaggon ta saka salati hakan ne ya tada Hajiya ta bud'e ido, bayan gwaggo ta gama wayar Hajiya dake kallonta ta hasken bedside lamps tace "Ya ya Mike faruwa ne miya samu Fateemar ne?" Cikin tashin hankali Gwaggo ta sanar mata ai ba shiri ta idasa tashi zaune, hannu ta kai ta d'aukko wayarta ta shiga kiran Haisam lokacin da kiran ya shigo mashi ya kife fuskar shi data Fatuu idanun shi a rufe sai Addu'oi yake mata, yana jin wayar na ringing amman a halin da yake ciki bai jin zai iya d'aukar waya, k'in d'aga wayar da yayi ya k'ara tada ma Hajiya da gwaggo dake kallon ta hankali, kiran layin Senator tayi tana fara yin ringing ya d'aga Hajiya tace mashi yaji abunda ke faruwa yace eh gashi nan ma zasu je Asibitin tace to bari su fito yace a'a ta yi baccinta in sha Allah ba abunda zai faru tace "taya wani bacci zai yuwu hankula duk sun tashi kaga uwar ta nan cikin tashin hankali gara dai muje da mu zauna zaman jiran tsammani" amsa mata yay da to,

Gaba d'aya Haisam ya rasa inda zai tsoma ran shi, fargaba ta cika shi zuciyar shi sai raya mashi abubuwa take, bawan Allah in ta raya mashi wani abun sai ya girgiza kai da sauri ya k'ara k'ank'ame Fatun, wani iri yake jin zuciyar shi gaba d'aya rayuwar shi da ita sai dawo mashi take ba abunda yake gani sai fuskar ta d'auke da Murmushinta mai burgewa, "ko dai dama Allah bai yi zaku rayu tare tsawon lokaci ba" zuciyar shi ce ke raya mashi hakan da sauri ya hau girgiza kai kawai sai jin kwalla yay suna zubo mashi bai ko yi yunkurin gogewa ba, gaba d'aya gani yake tafiyar tayi tsawo har saida yayi ma Na'eem magana yace sun kusa, bada jimawa ba suka k'araso Asibitin a Jere motocin nasu suka shigo cikin harabar, Laila ko inda aka tanada don parking motoci bata k'arasa ba ta parker Motar, da sauri ta bud'e k'opar ta fito lokacin cikin security guards d'in dake bakin gate da ya biyo bayan Motocinsu yace mata pls ta gyara fakin ba'a yi anan bata ko kalleshi ba ta furta mashi it's an emergency daga haka ta nufi cikin Asibitin ko rufe Motar ma bata yi ba, Na'eem na fakawa da sauri Haisam ya kai hannu ya bud'e kopar ya fara k'ok'arin fitowa da ita Na'eem ya zo wurin ya taimaka mashi su Najeeb ma da sauri suka k'araso, yana d'auke da ita suka nufi cikin Asibitin a bakin main entrance suka had'e da Laila ta taho da nurses sun turo gado, d'aurata akai nurses d'in suka turata ciki suma suka rufa masu baya, Amenity suka nufa da ita Lokacin Doctor da wata nurse taje tayi ma magana ya nufo su, yana zuwa wurin ya gaidasu su Abbas ne suka amsa mashi ya shiga tambayar su abunda ya faru da ita suna tafiya suke bashi amsa, bayan sun iso aka shiga da ita d'aki Dr yace su jira shi ya shige,

Shiru shiru tun bayan da likita ya shige bai fito ba sai nurses dake ta shige da fice cikin d'akin, can bayan kaman minti goma sai gashi ya fito nurse na biye dashi d'auke da sample na jini da gani na Fatun ne, tarar shi su Najeeb sukai suna tambayar ya ake ciki shi Haisam ido kawai ya bishi da shi don zuciyar shi tuni ta karye, ce masu yay in sha Allah she will be alright su d'an jira kad'an suna kan binciken dalilin sumar nata ne don da ran ta in sha Allah, har saida su Najeeb d'in sukai d'an murmushi tare da jinjina mashi kai ya wuce nurse d'in ta bi bayan shi, kallon Haisam daya jingina da bango Abbas yay fuskar shi tayi jajir haka idanun shi, dafa Shoulder d'in shi yay yace ya kwantar da hankalin shi in sha Allah ba wata babbar matsala bace da alama haka take suman ta don da ta yi miscarriage ma ai ta dad'e bata farfad'o ba duk da shi harda firgici yanzu kuma k'ilan gajiya ce tayi yawa,
Chapter 49 · 0% Book details