← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 152 OF 211

Sashe 152

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Alhamdulillah Allah ya kawo mu ranar ɗaurin aure, ana tashi aka shiga yin hidima ba kama hannun yaro, tunda safe jirgin yan ɗaurin aure ya sauka daga nan gidan su na G.R.A suka wuce kafin lokacin ɗaura auren yayi, suna isa gidan ango Nameer ya kira amaryar tashi ya sanar mata gasu sun iso yana son yaga fuskar kyakkyawar amaryarshi ta sanar mashi tana gidan Hajiya part ɗin su Adda Fatuu yace Ok gashi nan zuwa, yan Abuja basu daɗe da zuwa ba suma 6angaren angon Laila convoy ɗin su ya iso daga Kano, jerin danƙara danƙaran motoci ne masu numfarfashi tare da na security a gaba da baya da yake wanda zata auran wato bashir ɗan sanannan mai kuɗi ne a Nigeria, a Vip na haɗadɗan hotel Hillside Royal Suites suka sauka kafin lokacin ɗaura auren yayi, tunda wuri Aunty Mareeya ta taho gidan bikin saida ta biya ta ɗaukko Feenah kamar yadda sukai da ita, bayan isowarsu aka shiga yin aiki ba kama hannun yaro don ma Abincin wasu ba anan za'ai ba abunda za'ai a nan gidan kaɗan ne, ganin yadda Fatuu ke ta kujiba kujiba yasa aka fara mata magana kan ta rinƙa hutawa saboda halin da take ciki sai lokacin wasu da yawa suka san da ciki gareta har Haulat da Feenah basu gane ciki gareta ba duk an zata ƙibar da ta ƙara ne yasa ta ɗan yi tumbi, wuraren ƙarfe sha ɗaya Hajiya ta kira Gwaggo tace a fiddo da sauran kayan Minon ga wanda zai ɗauka nan yazo Gwaggo tace to ta sanar da ita akwae wanda zasu bisun sannan akwatunan na nan part ɗin su Fatuu aka maido su bari tayi mata magana sai tazo a fiddo su Hajiyar tace to ayi ma mutanen magana su fito kar a 6ata lokaci don tafiyar bata kusa bace, suna gama wayar tayi ma su Yaya da sauran wanda Yadikko tace aje dasu magana dama tun jiya ta sanar masu zasu tafi da safe, zo kaga rawar jiki wurin Yaya anji zanjen tafiya Abuja ita kuwa innarsu Altine kamar zata saka kuka tsabar takaici ita bama don yaran yan matan da suka kwaso da baza'a tafi dasu ba ita kanta da bazata ba yasa ta shiga matsananciyar damuwa sai faman roƙon a tafi da ita take Gwaggo tace ta bari aga Motar inda wuri sai ta bi su, cikin sa'a sai gashi Motar yar babba ce mai seat ukku a boot da bayan Motar aka saka akwatunan da kwalayen sauran kayan ba'asa kayan gara ko ɗaya ba tunda Hajiya ta hana, a layin tsakiya Mutum huɗu suka zauna harda innar su Altine data kasa rufe baki don murnar za'a da ita a gaba Mero ta zauna wasu harda cewa ai za'a iya ƙara mutum guda a gaban Driver ɗin yace a'a zai takura a bar mutum ɗaya yayi, Altine na tsaye bakin ƙopar Motar harda ƙwallarta tana roƙon aje da ita don Allah kofa da bikin Fatuu ba'a je dasu ba, daga cikin Motar innarsu ta wurgo mata harara tace ina za'a je da ita ra6e ra6e da Y'ay'a ko an gaya mata Abujar ruga ce Gwaggo ce ta rarrasheta tace tayi haƙuri watarana zasu je ko in Minon ta haihu fuska a yamutse tace ai ana iya ƙin zuwa da ita Gwaggon tace in sha Allahu in Allah ya kaisu lokacin ita zata sa aje da ita sannan ta ɗan kwantar da hankalinta, har Driver zai tada Motar Fatuu ta nufo Motar da yar sassarfa tana ruƙe da hannun ƙanwar su Aysha ganin tana ɗaga hannu yasa aka yi mashi magana ya dakata, bayan ta ƙaraso roƙon shi tay kan a bari ta zauna a gaban jikin inna mero da yake yasan wacece Fatun cikin kwantar da murya yace abunda yake gani Abuja ba kusa bace da za'a ce ta zauna a jikinta har suje dole su duka su gaji da alamun damuwa Fatun tace mashi to ya za'a yi don Allah ƙanwar amaryar ce gashi ta ƙwallafa rai sai Kuka take jin baza'a da ita ba, fitowa yay daga cikin motar yace bari yaga in zai iya samar mata wuri, kayan cikin boot ɗin ya gyaggyra haka akwatunan dake seat ɗin baya suma ya gyara tsarinsu ya rago guda biyu ya maido boot sai gashi an ɗan samu wuri a bayan yace ma innar su Altine tunda ita bata da jiki ta dawo nan baya sai ita yarinyar ta zauna a wurinta mutanen seat ɗin ma sun fi sakewa da sauri tace to ai ita ko a cikin boot ne indai za'a je da ita to zata shiga har saida ta ɗan ba Drivern dariya, bayan ta koma Aysha ta zauna a wurin ya rufe masu kopar kafin ya koma driver seat ya zauna saida yay Addua sannan ya tashi Motar aka shiga ɗaga masu hannu ana masu Addu'oin Allah ya tsare daga haka suka tafi.
Chapter 152 · 0% Book details