← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 119 OF 211

Sashe 119

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan sallar isha Aunty Mareeya na gama salla jikinta sanye da Hijab ta nufi part d'in Mom don amsa neman da Her Excellency ke mata, lokacin da ta shiga cikin Bedroom d'in da sallama ba kowa a ciki sai su biyu duk suna zaune a saman gado jikinsu sanye da dogayen riguna kowannen su ba kallabi a kan shi suna ruk'e da glass cups mai d'auke da ruwan lemu mai sanyi da gani hira suke suna sha, da murmushi gaba d'ayan su akan fuskokin su suka amsa mata Sallamarta ta nufi gadon, daga gaban gadon ta tsaya tana kallon su don kuwa sun rud'a ta bazata iya gane wacece Her Excellency d'in ba a ciki, Mom ce tace mata sannu da zuwa ta amsa ba tare data gane wacece ba tana d'an murmushi tace masu dama tazo wurin Her Excellency ne daga yanayin yadda tayi Maganar suka fahimci bata gane su ba Hajiya Zainab d'in ce tace mata "Ok, ki ganta" jin haka yasa Aunty tayi tunanin Mom ce tayi Maganar don haka sai ta juya kan Mom da tayi tunanin itace Hajiya Zainab tace "ranki ya dad'e gani na dawo kamar yadda kika ce" kasa daurewa Mom tayi ta saki dariya haka Hajiya Zainab d'in ma yar dariyar tayi ganin haka yasa Aunty Mareeya d'an waro ido tana masu kallon rashin fahimta Mom ta nuna mata Her Excellency tace mata gata nan itace tayi mata Magana, d'an bud'a baki Aunty tay sai kuma ta saki dariya don ta gane wasa da hankalinta tayi, saukkowa daga saman gadon Hajiya Zainab tayi still tana yar dariya hannunta ruk'e da cup d'in lemun tayi ma Aunty Mareeya alamar su je da hannu ta nufi doguwar kujerar cikin d'akin tana bata hakurin abunda tayi mata tace it's just for fun Auntyn ma dariya take tace ai ba komai, zama tayi kan kujerar ganin tayi tsaye tace mata ga wuri nan ta zauna, daga d'an can gefenta Aunty ta zauna ta kai cup d'in hannunta baki tay sipping lemun Aunty nata kallonta a cikin ranta tana raya sai kace ba ita ta haifi Sameer ba don sam jikinta bai nuna hakan ba, d'aura cup d'in tayi saman d'an table dake a gefen kujerar kafin ta juyo suka had'a ido da Aunty a nutse cikin girma ta fara magana "amm, dama ba wani abu bane inason muyi magana ne akan shiryen shiryen biki nasan kun fara ko?" Da sauri Aunty tace mata eh tuni anata yi, jinjina kai tayi taci gaba "Yayi kyau, game da kaya da za'ayi nike son sanar dake ba'a buk'atar komai don shi wanda zata auran ba zaune yake anan ba koda yaushe, zai tafi da ita can ne kuma yana da gida da komai haka anan ma so ko anyi su ba wani amfani da zasu yi don haka sai a barshi ba sai anyi komai ba wani abu na al'ada da komai dai duk a barshi ayi Addu'ar Allah ya tabbatar da Alkhairi" wani irin dad'i ne ya cika Aunty sai dai bata nuna ba sosae kawae dai faffad'an murmushi tayi tace "Ma sha Allah, Mun gode, mun gode kwarae your Excellency Allah ubangiji ya saka da Alkhairi ya k'ara girma da daukaka, hak'ik'a wannan ya tabbatar da ku d'in masu tausayin talakawa ne kuma duk d'aya kuka d'auke mu da ku, irin ku K'asar mu ke buk'ata ina Addu'ar Allah ubangiji yayi maku President ko mun amfana" wata irin dariya Hajiya Zainab tayi ta amsa da "Ameen ya Rabbi, in Alkhairi ne amman yanzu su Sis ne akan layi sai mu taya su da Addu'a" kai Aunty ta jinjina "Allah ya tabbatar da Alkhairi, ai your Excellency duk d'aya kuke wllh in Allah ya baku K'asar nan tamu nasan zamu more don irin ku take buk'ata bama kamar mu talakawa tabbas zamu ji dad'i, in Allah ya basu suna gamawa sai kuma ku dasa Allah ya amince" fad'ad'a dariyar ta Hajiya Zainab tayi tace mata hakan kuwa bazai zama son kai ba Aunty na dariya tace a'a wllh ai dama Ana cewa da yuyuyu gwamma d'aya kwakkwara jinjina kai Hajiya Zainab tayi tace Allah dai ya tabbatar da Alkhairi ya za6a mana Shuwagabanni nagari Aunty ta amsa da Amin, hannu ta kai ta d'aukko lemunta ta kur6a bayan ta cire Cup d'in cikin girmamawa Aunty Mareeya tace mata ko zata iya kiran Mahaifiyarsu su gaisa ta jinjina mata kai tace eh lafiya lou ai tuni ma yakamata ace sunyi hakan to ita abubuwane ke mata yawa don ko ita Daughter Fauziyya basu ta6a Magana ba sai yau, kiran Maman tasu ta shiga yi bayan ta d'auka suka gaisa ta tambayi ya Abuja da masu jego tace mata duk suna lafiya nan ta sanar mata dama zasu gaisa da Her Excellency ne, cikin alamun rashin fahimta Maman tasu ta tambayi wacece nan ta sanar mata Mahaifiyar wanda Fauziyya zata aura ai tana jin hakan ta yunk'ura dama a kwance take ta tashi zaune ta shiga daidaita zamanta Aunty Mareeya ta k'ara cewa in sun gaisa sai tayi mata godiya don tace ba sai anyi ma Fauziyya komai ba na kayan d'aki, jin hakan yasa Maman tasu kai hannu ta rufe baki alamar Al'ajabi, bayan ta ba Hajiya Zainab wayar cike da girmamawa Maman tasu ta shiga gaishe da ita duk da kuwa ta girmeta nesa ba kusa ba itama Hajiya Zainab a mutunce take gaisawa da ita, sosae Maman tasu tayi mata godiya da kuma Addu'oi fuskarta da murmushi take amsawa, bayan sun gama wayar ne tace ma Aunty Mareeya Shikenan zata iya tafiya in kuma da wani abu sai tayi magana tace mata ba komai wllh ta k'ara mata godiya har zata tashi sai kuma ta dakata cikin yar ina ina tace don Allah in ba damuwa ko zata bata lambar ta don a rink'a gaisawa tace sure bari ta bata ta amshi wayar tata ta rubuta mata daga haka sukai sallama, wurin gadon Aunty ta nufa don tayi ma Mom sallama, da murmushi Mom tace mata har an gama tattaunawar Aunty tace mata eh sai kuma tace "Don Allah Mom a k'ara taya mu godiya wurin Her Excellency tace ba sai anyi ma Fauziyya komai ba naji dad'i wllh Allah ya k'ara maku girma da d'aukaka" tana murmushi ta amsa da Amin tace mata ai ba wani abu bane duk an zama d'aya tayi Addu'ar Allah ya bar zumunci Aunty ta amsa da Amin kafin tayi mata sallama ta tafi.

Tana fitowa baya ta tsaya ta shiga kiran Fauziyya, bayan ta d'aga tambayar ta tayi tana ina tace tana a inda suka sauka har ta kwanta ma tace to ta fito waje ta sameta tace to, bada jimawa ba Fauziyyar ta fito tana sanye da kayan bacci riga da wando sai hula a saman kanta, nufo Aunty tayi gabanta har d'an fad'uwa yake don tasan da Maganar cewa Hajiya Zainab na son ganin Auntyn tasan kuma bai wuce game da hakan yasa Auntyn kiranta, tana k'arasawa gabanta kawai sai gani tayi ta rungumota cike da Farinciki take fad'in "Fauziyya ki taya mu murna ance ba sai anyi maki komai ba wllh iya ke suke buk'ata, da sauri Fauzy ta d'ago daga jikinta ta waro ido da tsananin mamaki ta maimaita abunda Auntyn ta fad'a cikin washe baki tace mata Wallahi kuwa yanzun nan ta dawo daga wurin Hajiya Zainab din, nan ta shiga fad'i mata yadda suka tattauna harda gaisawar da sukai da Maman su ta shiga yabonta tana fad'in tana da kirki sosae tayi dacen suruka, shiru Fauzy tay ba baki sai murmushi kawai da take gaba d'aya ganin abubuwan take tamkar a mafarki,

"Ya naga kin yi shiru ne, ko baki farinciki bane yanzu fa Shikenan Baba ba sai ya sayar da gonakin shi ba hakan kuwa ai abun murna ne" yar dariya Fauzy tay a sanyaye tace "a'a Aunty naji dad'i sosae wllh, kawai abubuwan ne keta ban mamaki wllh duka yaushe akai Maganar gida yanzu kuma ga wannan",

"Ai kinsan haka abun Allah yake lokaci guda yake juya al'amurra, baki ji ana cewa dare d'aya Allah kan yi Bature ba to misalin hakan ne, ai tsakanin mu da Ubangiji wllh sai godiya Yar gidan Hajiya kin tako mana arzuki Allah yasa a wurin bikin wata ma cikin kannanmu ta samo mana wani irin Sameer d'in koma k'anin shi" dariya sosae Fauzy ta saka tana fad'in kai Aunty,

"Allah kuwa ai abun fata ne ke baki ji ana cewa da arzuki a garin wasu ba gara a naku a nakun ma a cikin gidan ku duk da bansan ma ko yana da K'ani babba ba k'ilan kuma wannan da na gani lokacin da suka zo shine ke bi mashi shima dai ai lafiya lou don ya isa Aure naga kamar Nameer yake, amman wannan ma anya zai iya Auren talaka shima naga alamun kamar Sameer d'in yake, koda yake shima Sameer d'in ba gashi ya fad'a komar yar manomi ba" Dariya kawai Fauzy ke yi Aunty ta shiga yin godiya ga Allah tana fad'in wllh har ta rasa ina zata sa kanta don farinciki Allah dai ya nuna masu bikin da rai da lafiya dole taci uwar sabada har ta hango shigar da zatayi, dariya kawai Fauzy ke yi suka nufi komawa part d'in da suka sauka, bayan Fauzy ta koma d'aki zama tayi a bakin gado tayi shiru ba komai take tunani ba face Sameer don a yanzu sosae take jin son shi duk in bata ji Muryar shi ba ko sukai Vedio call bata jin dad'i duk da har yanzu d'in ba wata soyayya suke ba amman ba laifi sun fi yin magana yanzu, ji tayi bazata iya kwanciya batare da taji muryar shi ba ta d'ago wayarta ta shiga kiran shi bayan ta yanke ta zauna tana dakon ya biyo kiran......

95

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
Chapter 119 · 0% Book details