Sashe 52
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Gwaggo miya same ni ne har aka kawo ni Asibiti?" Fatuu ta fad'a tana ta kallonta, tana murmushi tace mata ta fad'i ne a wurin hidimar da akayi shine aka kawo ta, shiru Fatuu tay lokacin komai ya shiga dawo mata na lokacin data fad'i,
"To mi akace yake damuna?" ta sake tambaya gwaggo dake ta murmushi tay d'an shiru idonta akanta can tace mata gajiya ce tayi mata yawa anata zirga zirgar hidima, shiru Fatun tay bata kawo komai a ranta ba don tasan hakan na faruwa, mik'ewa gwaggon tayi tace bari ta fad'i ma nurse ta tashi koda abunda za'a mata ta d'aga mata kai, bayan fitar gwaggo maida idonta tay tana Kallon sama ta shiga tunano komai daya faru a wurin dinner, tuno da lokacin da Haisam ya bi Wak'a yayi mata tay nan take ta fad'ad'a murmushi sosae taji dad'in hakan da yayi mata don ya nuna zai iya yin komai don son da yake mata, gwaggo ce ta dawo tare da nurse suka nufo gadon, sannu nurse d'in tayi mata tana murmushi Fatun ta d'aga mata kai, tambayar ta tayi ba abunda ke mata ciwo nan ma ta d'aga mata kai alamar eh, cire mata oxygen mask d'in tayi da drip d'in da aka saka mata bayan ta gama yi mata abunda zata yi mata ta k'ara mata sannu sannan ta tafi, bayan fitar ta Fatun ta fara k'ok'arin tashi zaune cike da kulawa gwaggo ke mata sannu, zuru k'afafunta tay gwaggo ta tambayi ina zata tace fitsari take ji ta mik'e ta taimaka mata, nad'e mata rigar tayi ta baya kafin ta kamata Fatun na murmushi tace mata zata iya, cewa tay bari dai ta taimaka mata, a bakin toilet d'in ta saketa ta bud'e mata kopar Fatun ta shiga gwaggo na fad'in tabi a hankali don Allah ta d'aga mata kai kafin ta maido kopar ta rufe, cikin d'akin gwaggo ta koma ta gyara mata gadon bayan ta gama ta nufi inda kayan da su Haisam suka kawo suke ta bud'e ledar, fiddo robobin take aways d'in da ke ciki tayi, bayan Fatuu ta fito tace mata tazo to ta ci Abinci ta d'aga mata kai don kuwa yunwa take ji, a saman kujera ta zauna gwaggo ta bud'e robobi biyu fried rice ce da naman kaza sai guda biyu kuma na sakwara ne gwanin sha'awa a ido da gani ta daku sosae, da murmushi ta tambayi to mi zata fara da shi ta nuna mata sakwara gwaggon tace dama tayi tunanin ita zata ce Fatun tay murmushi, bayan ta fara cin Abincin gwaggo ta mik'e tana fad'in bari a cire wannan d'aurin ko ta sha iska, bayan ta cire head d'in gado ta nufa ta d'aukko net d'in data yafa tazo ta d'aura mata akan Fatun nata murmushin jin dad'in yadda gwaggon ke ta bata kulawa, bayan ta zauna a gefen ta Fatun ta kalleta tace itama taci Abincin mana tace mata taci dai, tura baki Fatun tayi a shagwabe tace "Don Allah ki ci, in baki ci ba zan aje nima in daina ci" dariya gwaggo tay ta d'an girgiza kai tace mata wai sai yaushe ne zata girma ta daina shagwaba tafa girma yanzu, tana murmushi tace mata ba rana kuwa, gwaggo da har lokacin dariya take tace lallai kam za'a rinka abun kunya in ta haihu uwa na shagwa6a d'a na shagwa6a Fatuu dake dariya tace kyau kenan ai, daga baya gwaggon ta fara ci, sosae Fatuu taci Abincin don saida ta cinye sakwarar tass gwaggo tace ta k'ara ta d'ayar robar dama Saboda ita yasa bata ta6a ba ita ta d'auki shinkafa tana ci, ce mata tay bari taci shinkafar itama, sai gashi itama ta cinyeta ganin gwaggo na kallonta tana murmushi yasa tace "Gwaggo ko dai hada ciwon cin Abinci nike yi" yar dariya tay tace waya sani, mik'a mata robar sakwara d'in tay tace ta k'ara da sauri ta girgiza mata kai tace cikinta fashewa zai yi in ta k'ara, leda mai kyallin data gani a ciki ta fiddo ta fara warwarewa tana fad'in bari taga minene a ciki, bayan ta bud'e tsire ta gani yasha kayan had'i su tumatir da koran tattasai da albasa tun kafin ta fara ci ta hau had'iye miyau kallon gwaggo tayi tace wai ta ci tana dariya tace to dama ai don aci aka kawo ko, sosae yayi mata dad'i tace ma gwaggo su ci tace taci ta rage mata in ma duka zata cinye ta cinye da sauri tace a'a zata rage mata, sai ga wadda tace cikinta zai fashe sai faman cin tsire take tana zuba har da tambayar yadda aka kawo ta Asibiti gwaggon ta shiga bata labari don dad'i take ji ganin ta haka saidai bata fad'i mata ainihin abunda ya ja komai ba, tambayar gwaggon tay ina wayar ta tace mata ta barota gida bata ji dad'in hakan ba don tana son jin muryar mijin ta.
Bayan su Haisam sun koma, wanka ya fara yi ya zura jallabiya Abbas ma ya shiga wankan, sallar Nafila yay ya kara godiya ga Allah da ni'imomin da yay mashi yayi ma Fatuu Addu'ar samun ingantacciyar lafiya harda Fanan ma yayi ma Addu'ar Allah ya k'ara bata lafiya, sosae yayi Addu'oi lokacin daya gama tuni Abbas ya kwanta Sameer yau ba anan zai kwana ba dama shi Abbas ranar da suka zo ne kawai ya kwana a wurin Salim yake kwana, bayan ya gama zaune yay yana ta tunanin ko zuwa yanzu Fatuu ta farka, sosae yake jin kewarta yana son jin muryar ta amman yasan ba waya a hannun ta daga baya ya mik'e yaje ya kwanta fuskar shi cike da annuri, ya d'auki lokaci idanun shi lumshe yana tunanin baby d'in shi a haka bacci yay awon gaba da shi..........
_Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268
*ASM 084*
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
............Washe gari bayan Haisam ya dawo daga sallar Asuba a main parlor ya tsaya ya kira Jidderh a waya, lokacin tana akan abun salla kiran ya shigo, mik'ewa tay ta nufi bakin gado ta zauna sannan ta d'aukko wayar, picking tay tun kafin tace wani abu taji yace ta same shi a parlor ta furta Ok, mik'ewa tay dama jikinta tana sanye da hijab ta nufi hanyar fita, yana zauna akan kujera one seater hannun shi ruk'e da waya ta iso wurin a kujerar kusa dashi ta zauna ya d'ago ya kalleta da fara'a ta gaishe da shi bayan ya amsa ta sake cewa "ya kwanan farin ciki" murmushi yayi ya amsa da Alhamdulillah, Addu'ar Allah ya bata lpy tayi bayan ya amsa yace mata so yake ta shiga Kitchen ta had'a mashi breakfast ba mai taking time sosae ba, tambayar shi tayi Asibitin zai kai ya d'aga mata kai, cike da zumud'i ta mik'e tana fad'in to yanzun nan zata had'a. Fauzy na gama sallar Asuba ta nufi d'akin su Aunty Mareeya lokacin data shiga a zaune kan abun salla ta iske ta da Saude Feenah na kwance kan gado don bata salla Abdul kuma dama tunda suka zo yana wurin su twins, da fara'a ta k'arasa cikin d'akin ta zauna daga gaban Aunty Mareeya, gaishe da Saude tay ta amsa tana murmushi ta maida idonta kan Aunty Mareeya dake bin ta da kallo, ganin tana ta faman zabga murmushi yasa tace ya zata zo tunda safe ta tasa su a gaba tana faman yi masu murmushi kamar wata zautatta, yar dariya Fauzy tay kafin tace Albishirinta da sauri tace goro harda su gyara zama shiru Fauzy tay Aunty Mareeyar duk ta k'agara ta ji miye har sai da ta kai hannu ta bugi shoulder d'inta tace dalla miye wai, fad'i masu abunda ya faru jiya ta shiga yi tana rufe baki Aunty Mareeya ta buga wata uwar shewa ta furta "Da kyau yar gidana Zarah, kwalliya ta biya kudin sabulu wllh wannan iya biyan bashi haka, kai Alhamdulillah Wllh naji dad'i nayi farincikin jin Maganar nan" Saude ma Alhamdulillah ta shiga fad'i, shewar da Aunty Mareeya tayi ce ta tashi Feenah ta bud'e ido, jin abubuwan da take fad'i yasa ta d'ago kai tana tambayar abunda ke faruwa cike da Farinciki Aunty Mareeya ta hau bata labari, jinjina kai Feenah ta hau yi fuskarta da faffad'an murmushi tace kai ma sha Allah abu yayi dad'i Allah ya bata lafiya ya inganta, amsawa sukai da Amin Aunty Mareeya tace ana ta shan Dinner d'in biki ashe Amarya da juna biyun ta mak'ale,
labarin yadda likita ya kasa fad'a Fauzy ta shiga basu sukai ta dariya suna fad'in ai dole ya kasa fad'a don wannan ba K'aramin Al'amari bane.
"To mi akace yake damuna?" ta sake tambaya gwaggo dake ta murmushi tay d'an shiru idonta akanta can tace mata gajiya ce tayi mata yawa anata zirga zirgar hidima, shiru Fatun tay bata kawo komai a ranta ba don tasan hakan na faruwa, mik'ewa gwaggon tayi tace bari ta fad'i ma nurse ta tashi koda abunda za'a mata ta d'aga mata kai, bayan fitar gwaggo maida idonta tay tana Kallon sama ta shiga tunano komai daya faru a wurin dinner, tuno da lokacin da Haisam ya bi Wak'a yayi mata tay nan take ta fad'ad'a murmushi sosae taji dad'in hakan da yayi mata don ya nuna zai iya yin komai don son da yake mata, gwaggo ce ta dawo tare da nurse suka nufo gadon, sannu nurse d'in tayi mata tana murmushi Fatun ta d'aga mata kai, tambayar ta tayi ba abunda ke mata ciwo nan ma ta d'aga mata kai alamar eh, cire mata oxygen mask d'in tayi da drip d'in da aka saka mata bayan ta gama yi mata abunda zata yi mata ta k'ara mata sannu sannan ta tafi, bayan fitar ta Fatun ta fara k'ok'arin tashi zaune cike da kulawa gwaggo ke mata sannu, zuru k'afafunta tay gwaggo ta tambayi ina zata tace fitsari take ji ta mik'e ta taimaka mata, nad'e mata rigar tayi ta baya kafin ta kamata Fatun na murmushi tace mata zata iya, cewa tay bari dai ta taimaka mata, a bakin toilet d'in ta saketa ta bud'e mata kopar Fatun ta shiga gwaggo na fad'in tabi a hankali don Allah ta d'aga mata kai kafin ta maido kopar ta rufe, cikin d'akin gwaggo ta koma ta gyara mata gadon bayan ta gama ta nufi inda kayan da su Haisam suka kawo suke ta bud'e ledar, fiddo robobin take aways d'in da ke ciki tayi, bayan Fatuu ta fito tace mata tazo to ta ci Abinci ta d'aga mata kai don kuwa yunwa take ji, a saman kujera ta zauna gwaggo ta bud'e robobi biyu fried rice ce da naman kaza sai guda biyu kuma na sakwara ne gwanin sha'awa a ido da gani ta daku sosae, da murmushi ta tambayi to mi zata fara da shi ta nuna mata sakwara gwaggon tace dama tayi tunanin ita zata ce Fatun tay murmushi, bayan ta fara cin Abincin gwaggo ta mik'e tana fad'in bari a cire wannan d'aurin ko ta sha iska, bayan ta cire head d'in gado ta nufa ta d'aukko net d'in data yafa tazo ta d'aura mata akan Fatun nata murmushin jin dad'in yadda gwaggon ke ta bata kulawa, bayan ta zauna a gefen ta Fatun ta kalleta tace itama taci Abincin mana tace mata taci dai, tura baki Fatun tayi a shagwabe tace "Don Allah ki ci, in baki ci ba zan aje nima in daina ci" dariya gwaggo tay ta d'an girgiza kai tace mata wai sai yaushe ne zata girma ta daina shagwaba tafa girma yanzu, tana murmushi tace mata ba rana kuwa, gwaggo da har lokacin dariya take tace lallai kam za'a rinka abun kunya in ta haihu uwa na shagwa6a d'a na shagwa6a Fatuu dake dariya tace kyau kenan ai, daga baya gwaggon ta fara ci, sosae Fatuu taci Abincin don saida ta cinye sakwarar tass gwaggo tace ta k'ara ta d'ayar robar dama Saboda ita yasa bata ta6a ba ita ta d'auki shinkafa tana ci, ce mata tay bari taci shinkafar itama, sai gashi itama ta cinyeta ganin gwaggo na kallonta tana murmushi yasa tace "Gwaggo ko dai hada ciwon cin Abinci nike yi" yar dariya tay tace waya sani, mik'a mata robar sakwara d'in tay tace ta k'ara da sauri ta girgiza mata kai tace cikinta fashewa zai yi in ta k'ara, leda mai kyallin data gani a ciki ta fiddo ta fara warwarewa tana fad'in bari taga minene a ciki, bayan ta bud'e tsire ta gani yasha kayan had'i su tumatir da koran tattasai da albasa tun kafin ta fara ci ta hau had'iye miyau kallon gwaggo tayi tace wai ta ci tana dariya tace to dama ai don aci aka kawo ko, sosae yayi mata dad'i tace ma gwaggo su ci tace taci ta rage mata in ma duka zata cinye ta cinye da sauri tace a'a zata rage mata, sai ga wadda tace cikinta zai fashe sai faman cin tsire take tana zuba har da tambayar yadda aka kawo ta Asibiti gwaggon ta shiga bata labari don dad'i take ji ganin ta haka saidai bata fad'i mata ainihin abunda ya ja komai ba, tambayar gwaggon tay ina wayar ta tace mata ta barota gida bata ji dad'in hakan ba don tana son jin muryar mijin ta.
Bayan su Haisam sun koma, wanka ya fara yi ya zura jallabiya Abbas ma ya shiga wankan, sallar Nafila yay ya kara godiya ga Allah da ni'imomin da yay mashi yayi ma Fatuu Addu'ar samun ingantacciyar lafiya harda Fanan ma yayi ma Addu'ar Allah ya k'ara bata lafiya, sosae yayi Addu'oi lokacin daya gama tuni Abbas ya kwanta Sameer yau ba anan zai kwana ba dama shi Abbas ranar da suka zo ne kawai ya kwana a wurin Salim yake kwana, bayan ya gama zaune yay yana ta tunanin ko zuwa yanzu Fatuu ta farka, sosae yake jin kewarta yana son jin muryar ta amman yasan ba waya a hannun ta daga baya ya mik'e yaje ya kwanta fuskar shi cike da annuri, ya d'auki lokaci idanun shi lumshe yana tunanin baby d'in shi a haka bacci yay awon gaba da shi..........
_Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268
*ASM 084*
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
............Washe gari bayan Haisam ya dawo daga sallar Asuba a main parlor ya tsaya ya kira Jidderh a waya, lokacin tana akan abun salla kiran ya shigo, mik'ewa tay ta nufi bakin gado ta zauna sannan ta d'aukko wayar, picking tay tun kafin tace wani abu taji yace ta same shi a parlor ta furta Ok, mik'ewa tay dama jikinta tana sanye da hijab ta nufi hanyar fita, yana zauna akan kujera one seater hannun shi ruk'e da waya ta iso wurin a kujerar kusa dashi ta zauna ya d'ago ya kalleta da fara'a ta gaishe da shi bayan ya amsa ta sake cewa "ya kwanan farin ciki" murmushi yayi ya amsa da Alhamdulillah, Addu'ar Allah ya bata lpy tayi bayan ya amsa yace mata so yake ta shiga Kitchen ta had'a mashi breakfast ba mai taking time sosae ba, tambayar shi tayi Asibitin zai kai ya d'aga mata kai, cike da zumud'i ta mik'e tana fad'in to yanzun nan zata had'a. Fauzy na gama sallar Asuba ta nufi d'akin su Aunty Mareeya lokacin data shiga a zaune kan abun salla ta iske ta da Saude Feenah na kwance kan gado don bata salla Abdul kuma dama tunda suka zo yana wurin su twins, da fara'a ta k'arasa cikin d'akin ta zauna daga gaban Aunty Mareeya, gaishe da Saude tay ta amsa tana murmushi ta maida idonta kan Aunty Mareeya dake bin ta da kallo, ganin tana ta faman zabga murmushi yasa tace ya zata zo tunda safe ta tasa su a gaba tana faman yi masu murmushi kamar wata zautatta, yar dariya Fauzy tay kafin tace Albishirinta da sauri tace goro harda su gyara zama shiru Fauzy tay Aunty Mareeyar duk ta k'agara ta ji miye har sai da ta kai hannu ta bugi shoulder d'inta tace dalla miye wai, fad'i masu abunda ya faru jiya ta shiga yi tana rufe baki Aunty Mareeya ta buga wata uwar shewa ta furta "Da kyau yar gidana Zarah, kwalliya ta biya kudin sabulu wllh wannan iya biyan bashi haka, kai Alhamdulillah Wllh naji dad'i nayi farincikin jin Maganar nan" Saude ma Alhamdulillah ta shiga fad'i, shewar da Aunty Mareeya tayi ce ta tashi Feenah ta bud'e ido, jin abubuwan da take fad'i yasa ta d'ago kai tana tambayar abunda ke faruwa cike da Farinciki Aunty Mareeya ta hau bata labari, jinjina kai Feenah ta hau yi fuskarta da faffad'an murmushi tace kai ma sha Allah abu yayi dad'i Allah ya bata lafiya ya inganta, amsawa sukai da Amin Aunty Mareeya tace ana ta shan Dinner d'in biki ashe Amarya da juna biyun ta mak'ale,
labarin yadda likita ya kasa fad'a Fauzy ta shiga basu sukai ta dariya suna fad'in ai dole ya kasa fad'a don wannan ba K'aramin Al'amari bane.