← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 73 OF 211

Sashe 73

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Da yake Weekend ne ana abubuwan nishad'i a gidan tuni Fatuu ta washe saidae taci alwashin ita da ta k'ara ba wani maganin bacci har a bada in dai ba patient ba a Asibiti shi ma sai in likita ne yace a bashi duk da tasan laifinta ne ita ta cika ma Hajiyar abun kuma ya had'u da shekaru, da daddare atare gaba d'aya wad'anda ke a gidan suka ci Abinci kamar dai da safe da kuma da rana, bayan sun gama cin Abincin daren sun koma part d'in su taje tayi wanka, bayan ta gama shiryawa da kayan bacci riga da wando tasa hula ta nufi Parlor wurin Hajiya da tuni ta wartsake tana zaune idanunta sanye da glass tana kallo, sannu tayi mata Hajiyar ta d'aga mata kai ta zauna itama, bata dad'e da zama ba Nameer ya shigo hannun shi ruk'e da ledojin Fura bayan sun gaisa ya d'aura akan c-table yace gashi nan Dad yace ya kawo daga haka yay masu saida safe, Fatuu ce tace mata ta d'aukko cup ta zuba mata Hajiyar ta d'an yamutsa fuska tace anya yau zata sha furar nan don gaskiya jiya itace ta bugar da ita wllh, duk sai Fatun bata ji dad'i ba ganin zata haramta mata abunda take so, wani tunani tay da sauri tace ma Hajiyar ita tana ganin ba daga furar bane k'ilan daga naman da suka ci ne ya had'u da furar shine suka bata reaction, Hajiyar tace anya sai kace dai kifi Fatun tace ai shima Naman yana iya sawa an koya masu a Makaranta Hajiyar tay mata wani kallo mai kaman harara tace to kuma shine ta bari suka ci, a dabarbarce tace ai bai cika sa wani abu ba kamar kifin ita tama dai fi tunanin k'ilan naman da aka sarrafa d'in ne keda matsala, ta6e baki Hajiya tay tace koma dai minene mai faruwa ai ta faru, da yake ranta na son furar tace mata ta zuba mata yar kad'an tasha in bata ji komai ba sai ta k'ara cike da jin dad'i Fatun tace to ta mik'e, bayan ta zuba mata ta bata itama ta zuba ta fara sha, suna cikin sha taji Hajiyar tace wai Haisam d'in ya had'a kayan tafiyar ko kuwa, d'an murmushi Fatuu tay ta sadda kai tace mata bata sani ba amman tasan k'ilan ya had'a zuwa yanzu tunda gobe zai tafi, d'an ta6e baki Hajiyar tayi sai kuma tace mata ta tashi taje ta gani in bai had'a ba ta had'a mashi in kuma ya had'a mata aiki ya tafi ya barta da wahala ita ta sani, kunya ce ta kama Fatun ta sadda kanta k'asa tana haka taji tace ta tashi taje, mik'ewa tay zata tafi Hajiyar tace to wa ta bar ma sauran furar ta d'auka taje da ita tana had'a kayan tana sha, d'auka tay sumi sumi ta wuce, a yadda take ta nufi hanyar fita daga parlon ta fuce, ta baya ta fita tana tafiya a ranta take raya gajen hak'uri gashi nan da kanta tace taje, wata zuciyar ta raya mata rabon kowa zai jigata ne tay yar dariya.

Washe gari tunda Fatuu ta tashi cikin damuwa take, a part d'in Haisam tay wanka don nan ta kwana bayan ta koma part d'in Hajiya ta canza kaya, bayan sun gama yin Breakfast part d'in Haisam d'in ta koma, gaba d'aya yini yay aikin rarrashinta don sai kuka take mashi, lokacin daya dawo sallar la'asar tana zaune a bakin gadon shi itama bata dad'e da gama yin sallar ba, zama yay a bakin gadon suna kallon juna slowly ya furta mata zasu wuce don 4:30 jirginsu zai tashi zuwa Lagos yanzu yakamata su tafi don hud'u ta kusa, kai kawae ta d'aga mashi yace bazata raka shi Airport ba, a marairaice tace mashi bata son taje tay ta kuka tunda yak'i daina zuwa, kai ya d'aga mata ya kai hannu ya rungumo ta ya furta zai yi missing d'in ta sosae cikin muryar kuka tace itama, d'ago da ita yay suna kallon juna yay mata d'an murmushi ya kai bakin shi yay pecking duka kumatunta ya furta "I love you My Baby" itama tace mashi haka ce mata yay ta tashi suje ya rakata cikin gida tace mashi a'a zata zauna anan sai anjima zata koma, shiru ya d'an yi kafin yace tay mashi alkawarin ta daina kukan cikin karyayyar murya tace ai shi yake zuwa amman zata bari ya d'aga mata kai, mik'ewa yay ya nufi inda trolley d'in shi yake ajiye dama saida ya gama shiryawa sannan ya tafi Masallaci, juyowa yay ya kalleta ya furta ta kula da kanta sosae ta d'aga mashi kai tana kikkafta ido, har ya kai k'opa yaji ta kira sunan shi ya dakata ya juyo, mik'ewa tay ta nufo shi a gaban shi ta tsaya idanun ta cike da k'walla tace bari ta raka shi, murmushi yay yace indai bata so ta barshi tace a'a zata je, dama ranar k'ananun kaya ce hakan yasa ta d'aura after dress da zata zo wurin shi gyalen rigar na saman kanta, ce mashi tay ya kawo akwatin ta ruk'e ya girgiza mata kai ya kawo d'ayan hannun shi ya kama nata suka tafi,

Gaba d'aya yan gidan sun fito bakin Entry Hall don yi masu rakiya lokacin da suka k'araso, harda Dad da Hajiya dasu Jidderh da Aunty ba wanda aka bari, a Jeep din da za'a d'auki Dad Aunty da Mom suka shiga sai Nameer ya shiga gaba, sai wata Jeep din Haisam ya shiga gaba Hajiya da Fatuu da Jidderh suka shiga baya sai k'aramar Mota Yasmeen da Affan dasu twins suka shiga a k'arshe kuma Hilux d'in escort ce a jere Motocin suka tafi. Bayan anje Airport d'in duk yadda Fatuu taso kar tayi kuka da zasu rabu abun yaci tura saida tayi akaita rarrashinta harda Dad a cikin masu rarrashin nata shi kan shi Haisam d'in wani iri yake jin shi, tana ji tana gani Hubby d'inta ya tafi.

Bayan sun baro Airport d'in ba gida suka koma ba bazama sukai Outing, sosae suka zaga gari harda wani babban park suka je sukai ta hawa liluna iri iri ita dai Fatuu an hana ta hawa sai aikin kallo take tana nishad'i don harda Dad dasu Mom aka hau wasu lilon Hajiya dae itama aikin kallon tayi daga baya kuma suka yi hotuna, bayan sun baro park d'in wani babban shopping mall suka je nan aka ce kowa ya za6i abunda yake so, Su Mom duk kayan shafa da turarurruka suka d'auka haka Jidderh ma da Yasmeen suma cosmetics d'in suka d'auka suka had'a da Undies, Su Twins da Fatuu wurin kayan zak'i suka nufa saida suka cika basket dinsu da su Sweets, biscuits, chocolate da sauran su Fatuu sai ce masu take su barshi haka amman suka k'i wai ai harda Baby d'in su shima za'a d'aukar mawa Fatuu sai dariya take, Hajiya ita k'in d'aukar komai tay tace bata buk'atar komai Senator ne ya za6ar mata turarurruka Mom kuma ta d'aukar mata dogayen riguna da tasan tana sa irinsu harda Fatuu ta za6ar ma wasu dogayen riguna tace zata ji dad'in su nan gaba, Affan ma underwear ya d'auka sai turare da kayan zak'i, kowa dai ya d'auki abunda yake so, suna cikin shopping d'in Haisam ya kira Fatuu ya sanar mata sun isa Lagos ta hau yi mashi shagwabar tana missing nashi, anan Mall d'in suka yi sallar Magrib bayan sun gama suka shiga Eatery d'in wurin, kowa abunda yake so shi aka kawo mashi ya ci, daga nan bayan sun gama gida suka koma lokacin da suka dawo an fara kiran sallar isha kowa ya nufi part d'in shi cike da annashuwa, basu zauna cin Abincin dare ba don duk a k'oshe suke saidai wad'anda suka fara jin yunwa ne suka d'an ci harda Fatuu acici ta k'ara.
Chapter 73 · 0% Book details