← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 151 OF 211

Sashe 151

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

fuska a tur6une Hajiyar tace "dawa yace ayi mata wata gara?" shiru gwaggon tayi Hajiyar tace to ba wata garar da za'a ɗauka zata yi Magana yanzu da Senator kan sauran kayan amman kada a sake a kai wasu kayan abinci da sunan gara in kuma ba'a ji Maganarta ba to rai kuwa zai 6aci, Gwaggo na murmushi tace in sha Allahu baza'a kai ba ta bata haƙuri Hajiyar tace ta saurareta yanzu zata yi Magana game da kayan zata kirata cike da girmamawa tace to, bada jimawa ba sai gashi ta sake kiranta ta sanar mata goben in Allah ya kaimu kafin a ɗaura auren za'a turo Mota da zata kwashe sauran kayan in ma akwae wanda zasu bi Motar lafiya lau su wanda zasu tafi ta jirgin sai su fidda su zuwa da safe zata ƙara kira su yi magana, Sosae Gwaggo tayi mata godiya da Addu'oi kafin suyi sallama saida ta jaddada mata kan kada a sake a saka kayan garar nan suyi amfani da abun su Gwaggo na murmushi tace in sha Allah baza'a saka dasu ba suka yi sallama, bayan sun gama wayar dama Gwaggon ware kanta tayi da suna wayar ta shiga tunanin to suwa za'a bada su tafi ta jirgin bata son wani yaga an yi mashi ba daidai ba, tunanin kiran Fatuu suyi shawara tayi dama tana gidan, bayan tazo ne tayi mata bayanin da Hajiya tay game da ɗaukar Minon Fatun tace "ni hakan ma wllh yayi man daɗi dama ji yadda suka kwaso uban mutane kuma nan nufin su duk gaba ɗaya za'a dasu kai Amaryar, kawai mutum biyar ɗin asa Aunty mareeya, Aunty Feenah sai ke sai kuma babbar ƙawar Mino sai cikon ta biyar ɗin asa...." shiru tay tana tunanin wadda za'a sa ta tambayi Gwaggo ko hada Yadikko za'a tace mata a'a ita da take Uwar Amarya tace to wa take ganin za'a sa na biyar ɗin gwaggon tace "sai ke ko, ai baki sa kan ki ba" Fatun tace shikenan hakan yayi da yanayin yar damuwa Gwaggo tace amman hakan baza'ai ma abun wata fahimta ba ace ba dangin Baffan su da kuma Mahaifiyarta Fatuu tace to su kawai sai a saka su a Motar da aka ce suyi gaba Gwaggon tayi ɗan shiru kafin tace ita bata son abunda zai ja rashin fahimta aga tayi ba daidai ba bari dai a kira Yadikko a faɗi mata aji mi zata ce, bayan an kira ta faɗi mata hannu ta kai ta rufe baki kafin ta cire tace mi zai ja a ɗaura yan Adamawa a jirgi ai abun kallo da magana zasu ja gara ayi yadda Fatuu tace ala bashshi su Yaya da Mero da innarta wato Kakar Mino sai Yayarta hansai su sai a ɗaura su a Motar Gwaggo tace tana ganin hakan lafiya lou tace eh in ma wani yayi tsegumi kan hakan sai ace basu da abubuwan da ake buƙata na yin tafiyar dasu a jirgi, hakan da tace yayi ma Gwaggo akan wannan matsayar suka tsaya, sai wurin ƙarfe sha ɗaya da rabi Fatuu ta koma gida direct part ɗinta ta wuce ba kowa a parlon ta wuce Bedroom, lokacin data tura ƙopar ta shiga a saman gado ta hango haisam yayi shigar bacci haka su twins ma ya saka masu kayan baccinsu da alama ma har wanka yayi masu Abie na a saman ƙirjin shi yana bacci Grandpa kuma na a ta gefen shi ya rungumo shi jikinshi da hannun shi guda gaba ɗayan su bacci suke yadda sukai kwanciyar abun gwanin burgewa, ta ɗan ɗauki lokaci tana ta kallonsu tana sakin murmushi kafin ta nufi hanyar laudary, after some minutes ta fito ɗaure da towel da ƙaramin towel tana goge jikinta kanta yasha kitso da Mero tayi mata ɗazun, press ta nufa ta fiddo kayan baccin da zata saka Nursing pajamas, bayan ta gama sawa gaban mirror ta nufa tana kallon kitson da aka mata yar yar sosae taga yayi mata kyau ko don bata saba yi bane, mai da take shafawa da daddare ta shafa harda na tafin hannu da yatsu sannan ta goga roll-on bayan ta gama ta feffeshe jikinta da turarurruka masu sanyin ƙamshi, wurin gadon ta nufa saida ta gyara ma twins nasu gadon kafin ta kai hannu a hankali don kada ta tada Haisam ta ɗauko Abie ta kai shi saman gadon shi, tana ƙoƙarin daukar Grandpa Haisam ɗin ya buɗe ido slowly suka sauka kanta ta sakar mashi murmushi tare da kashe mashi ido shima yay mata murmushin, shima Adam gadon shi ta kai shi ta juyo tana ce ma Haisam sun ci Abinci ne taga har ta kwantar dasu ba wanda ya farka ya lumshe mata ido kafin a hankali yace ya basu kafin suyi bacci yana gama Maganar ta faɗa jikin shi tana faɗin thank you Daddy wai a madadin su twins ɗin ya ƙara faɗaɗa murmushin shi, bin juna sukai da kallo kowa fuskarshi da annuri can yace yadda ta kwantan baza tayi hurting kan ta ba tace ai bata danne cikin sosae ba ya lumshe ido, tambayarta yay ya hidima tace anata yi gaba ɗaya a gajiye take don ma Gwaggo na hanata aiki sosae ya jinjina kai kafin ya kai hannu ya fara shafa kitsonta ya furta yayi kyau ta furta thanks tare da lumshe mashi ido irin yadda yake, yana ɗaya daga cikin abunda take so tattare dashi kenan duk in kayi abunda ke buƙatar yabawa sai ya ya6a sa6anin da yawan wasu mazajen basu iya yaba ma matan su in suka yi kwalliya ko wani ado wasu har sai matan sun tanka sun ce wai baka ga nayi abu kaza ba sannan in an ci sa'a yace yayi kyau wani kuwa saidai yace shi bai ma lura ba irin hakan kaman cin fuska ne ace kana tare da mace a wuri guda amman tayi abu kace wai baka lura ba shiyasa da yawan matan basu yin adon akai akai tunda wanda suke yi domin su basu yabawa sai waɗanda ya zamar ma jiki ne sun saba suke cigaba da yi koda mazan basu yabawa, Maza yakamata su gyara yaba kwalliyar mace nasa taji daɗi ta ƙara ƙaimi wurin yi akai akai sannan yana ƙara soyayya don ita mace abu kaɗan kesa a siye zuciyarta, sauketa yay daga jikin shi yace mata yana zuwa ta ɗaga mashi kai, toilet ya nufa yana shiga wayar Fatuu ta fara ringing har saida gabanta ya ɗan faɗi ta raya wake kiranta a wannan lokacin sha biyu har ta wuce, saukkowa tayi ta nufi gaban dressing mirror inda wayar take har lokacin ringing take ta kai hannu ta ɗaukko tana duba mai kiran ta saki murmushi ganin Fauziyya ce,

"Ƙawata Amarya ko kun iso ne?" ta fada bayan ta ɗaga daga can ɗayan bangaren Fauzy ta bata amsa da eh yanzun nan suka sauka Abuja, cikin nuna farinciki Fatuu tayi mata anzo lafiya ta amsa ta sake tambayar Nasarawa zasu wuce tace mata a'a gidan su na Abuja zasu tsaya don gobe yana son zuwa ɗaurin aure dasu Daddyn Haisam Fatun tace suma goben zasu haɗu kenan in suka kawo amarya harda cewa ta ƙagara taga yadda ta koma Yaya Sameer ya iya kiwo Fauzyn tay yar dariya mai sauti daga baya sukai sallama, aje wayar tayi ta juya zata koma gado lokacin Haisam ya buɗe ƙopar laundry ya fito ta juya ta nufe shi suna haɗuwa ya rungumeta tana kallon fuskar shi da murmushi ta faɗi mashi Fauzy ce ta kirata ta sanar mata sun sauka Abuja yanzu ya jinjina kai kafin yace sun yi waya da Sameer kafin su taho, ɗaukarta yay ya nufi gado da ita tana ta dariya tana faɗin wai sai yaushe zai fara jin nauyin ta yay murmushi kawai, bayan ya kwantar da ita mikewa yay ya kunna lamp ta side ɗin da yake kafin ya nufi wurin Switch ya kashe hasken ɗakin ya dawo gadon ya fara mata tausa cikin salon ƙauna tana ta lumshe ido tare da yaba abunda yake matan sun ɗan ɗauki lokaci yana mata massage ɗin kafin ya fara canza salo tana ganin haka itama ta fara bashi nata salon daga haka suka lula wata duniya da ma'aurata ke zuwa.

FRIDAY
Chapter 151 · 0% Book details