Sashe 161
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"Amman kinsan ai tun da kika zama Yayata nike girmama ki ko" ɗan ta6e baki tay yana dariya yace yanzu ma zai ƙara girmamata tunda ta mashi aiki tay dariya kafin tace ai biya zai yi da sauri yace ta faɗi ko nawa ne zai bata in ma baida su zai samo tace bada kuɗi zai biya ba alƙawari zai yi na bazai ma Mino kishiya ba yana murmushi yace in don wannan ne dama baida wannan ra'ayin itace kaɗai matar shi har ya mutu ta ɗan harare shi tace ita zai ma daɗin baki,
"Ba daɗin baki bane am serious mizai sa in ƙara Aure inada Ameenatu, tamkar rainonta zanyi fa lokacin da zan manyanta lokacin zata ƙara cika mace to mi zai burge ni a wurin wata" murmushi Fatuu tay tace wasa ma take mashi ita ai tana da kishiyar ko yace to shi da gaske yake daga Babynshi ya gama tace Allah ya barsu tare ya basu zaman lafiya da zuriya ɗayyiba ya amsa da Amin kafin ya tambayi mi zai tayata da shi tace ba komai duk ta cimma aikin ma sauran ƙarashe yace Ok tare da yi mata godiya ya juya ya fita, farar shinkafa da miya tayi sai coleslaw tayi farfesun yan ciki saida ta wanke komai data 6ata ta zuba abincin a cikin warmers masu kyau ta kai kan Dinning table, bedroom ɗin Minon ta nufa bata yi tunanin Nameer na ciki ba saida ta shiga ta ganshi rungume da Minon suna bacci tay murmushi ta wuce inda ta aje purse ɗinta ta ɗauka kafin ta fito, parlor ta dawo ta fiddo wayarta nan taga missed call ɗin Gwaggo har biyu, sake kiranta tayi bayan ta ɗaga sun gaisa tace ta kira bata kusa ne Gwaggon tace eh tayi tunanin hakan dama zasu tafi ne taga bata ganta ba suyi sallama saida suka fito ɗanta Haisam ke faɗi mata tana gidan Mino tace eh tare da tambayar yanzu sun tafi kenan tace mata eh gasu a Mota, fatan Allah ya tsare tay tace sai tazo, kafin suyi sallama ta tambayi ya Minon tana yar dariya tace lafiya lou dama taƙi kwantar da hankalinta ne tana ta koke koke amman yanzu ta kwantar da hankalin Gwaggo na murmushi tace ina ruwan Mino a hankali zata saba sukai sallama tace tayi ma su Yaya da Safnah Allah ya tsare tace to, bayan sun gama wayar tunanin zaman mi zata zauna yi tay hakan yasa ta shiga kiran Haisam bayan ya ɗaga tace in bai komai yazo ya ɗauketa pls yace Ok, after some minutes ya kira yace mata yana a harabar gidan ta miƙe ta nufi hanyar fita, saida ta buɗe kopar gaban Motar taga ashe harda su twins yazo da yake Motar tinted ce gaba ɗaya an yi masu wanka suna sanye da kaya iri ɗaya suna ganinta Adam ya washe mata baki Abie kuma yay mata ɗan murmushi duk suka miko mata hannu suna son ta ɗaukesu suna faɗin Momy, saida ta zauna sannan ta ruƙe su gaba ɗaya ya tashi Motar suka tafi, bayan sun hau hanya take ce mashi ashe su Gwaggo sun tafi ya ɗaga mata kai tace ta kirata har sau biyu bata kusa da wayar, shiru suka ɗanyi can ya tambayeta lafiya gidan Nameer ɗin tay faffaɗan murmushi idonta akan shi tace mashi laifi yayi ne shine aka kaita rarrashi Haisam ɗin ya ɗan buɗa ido tare da ɗage gira sai kuma yay murmushi ba tare da yace komai ba, suna cikin tafiyar take tambayar shi yaushe zata je Katsina ya bata amsa da Us zasu tafi tace bazata je sallama ba yace in tana so sai taje amman yana son zasu je Adamawa su duba jikin arɗo yaji su Dad ɗinta suna faɗi ma Dad ɗinshi bai lafiya, sosae taji daɗi jin zasu je tace mashi eh bai jin daɗi yace Ok cikin next week sai suje.
Bayan sallar Azahar su Aunty yan Kano suka dawo an cika su da abubuwan arzuƙi Jidderh harda kukan baro Aunty Laila duk tayi sukuku koda ana Maganar Lailar bayan sun dawo sai ta sake saka wani sabon kukan Hajiya na faɗin itama ba Auren zata yi ta tafi ba, Bayan sallar La'asar su Hajiya Maryam suka wuce lagos su Hajiya Zainab ma lokacin suka tafi harda Fauzy.
Alhamdulillah Yan Katsina sun isa lafiya sai fatan Allah ya huta gajiya, a ranar bayan sallar isha duk suna zaune a cikin parlon Gwaggo suna yin hirar bikin baka jin komai sai fullanci dake tashi su innarsu Altine sai zuzuta gidan Mino suke suna faɗin ai Aljannar duniya aka kaita, suna cikin yin firar Amadu da Kamalu suka shigo jin firar da suke ne yasashi kunna Vedio ɗin gidan Minon da yayi lokacin da suke zagayawa ya miƙa ma Yadikko ta fara gani, sakin baki tay da tsananin mamaki take kallon Vedio ɗin tana faɗin yanzu anan Minon take aka bata amsa da eh su Altine da basu je ba duk sun zagayeta sun saki baki galala suma suna kallo, ƙarshe dai kukan farinciki Yadikko ta saka ta hau gode ma Allah da kuma Gwaggo tana faɗin koda tayi aikatau a Abuja bata ta6a tunanin wani nata zai zauna a can ba balle kuma ƴarta, inna Mero matar arɗo ce tace hada halin kirkinta yaja mata yadda ta ruƙe ƴaƴan kishiyarta da Amana bata zalunce su ba ta ɗaukesu tamkar nata gashi nan hakan yayi mata rana tunda data zalunce su ba yadda za'ai Gwaggo ta ruƙa mata ɗiya har itama tayi aure gidan daula su Kakar Minon suka shiga faɗin hakane wllh Yaya kuwa duk tabi tasha jinin jikinta sai murmushin yaƙe take, suna haka wayar Kamalu ta fara ringing ya kai idon shi kan screen ɗin yaga baƙuwar lamba saida ya fito waje saboda hayaniya sannan ya ɗaga tare da yin sallama daga ɗayan bangaren zazzaƙar muryar mace ta amsa mashi tare da tambayar ya yake ya bata amsa da lafiya lou kafin ya tambayi wacece, farko shiru tayi kamar bazata tanka ba saida ya ƙara tambaya sannan tace kenan data amshi number ɗin shi tace zata kira yay saving bai yi ba kenan, jin haka yasa ya ganeta da sauri yace tayi haƙuri ya manta ne da yake lokacin jiran shi ake tace Ok kafin ta tambayi ya suka koma yace Alhamdulillah itama ya tambayeta sun koma ne ko suna Abuja tace mashi No sun koma, ɗakinsu ya nufa suka cigaba da yin wayar saidai itace ke fara yin magana sannan yayi harda tambayarshi game da karatunshi ya bata amsa da bayan ya gama Secondary acan garin su bai cigaba ba dalilin da yasa yanzu ya dawo nan kenan don ya cigaba har ma ya siya Jamb zai yi tace Ok tare da yi mashi fatan Akhairi yayi mata godiya daga baya tace mashi tana son zasu zama Friends in ba damuwa har saida ya jinjina Maganar a ran shi don baiyi zaton jin hakan daga wurinta ba jin yayi shiru tace ko bazai yi abota da ita ba, da sauri yace a'a zasu yi suka cigaba da yin wayar kafin daga baya sukai sallama ya tashi ya koma shago.
"Ba daɗin baki bane am serious mizai sa in ƙara Aure inada Ameenatu, tamkar rainonta zanyi fa lokacin da zan manyanta lokacin zata ƙara cika mace to mi zai burge ni a wurin wata" murmushi Fatuu tay tace wasa ma take mashi ita ai tana da kishiyar ko yace to shi da gaske yake daga Babynshi ya gama tace Allah ya barsu tare ya basu zaman lafiya da zuriya ɗayyiba ya amsa da Amin kafin ya tambayi mi zai tayata da shi tace ba komai duk ta cimma aikin ma sauran ƙarashe yace Ok tare da yi mata godiya ya juya ya fita, farar shinkafa da miya tayi sai coleslaw tayi farfesun yan ciki saida ta wanke komai data 6ata ta zuba abincin a cikin warmers masu kyau ta kai kan Dinning table, bedroom ɗin Minon ta nufa bata yi tunanin Nameer na ciki ba saida ta shiga ta ganshi rungume da Minon suna bacci tay murmushi ta wuce inda ta aje purse ɗinta ta ɗauka kafin ta fito, parlor ta dawo ta fiddo wayarta nan taga missed call ɗin Gwaggo har biyu, sake kiranta tayi bayan ta ɗaga sun gaisa tace ta kira bata kusa ne Gwaggon tace eh tayi tunanin hakan dama zasu tafi ne taga bata ganta ba suyi sallama saida suka fito ɗanta Haisam ke faɗi mata tana gidan Mino tace eh tare da tambayar yanzu sun tafi kenan tace mata eh gasu a Mota, fatan Allah ya tsare tay tace sai tazo, kafin suyi sallama ta tambayi ya Minon tana yar dariya tace lafiya lou dama taƙi kwantar da hankalinta ne tana ta koke koke amman yanzu ta kwantar da hankalin Gwaggo na murmushi tace ina ruwan Mino a hankali zata saba sukai sallama tace tayi ma su Yaya da Safnah Allah ya tsare tace to, bayan sun gama wayar tunanin zaman mi zata zauna yi tay hakan yasa ta shiga kiran Haisam bayan ya ɗaga tace in bai komai yazo ya ɗauketa pls yace Ok, after some minutes ya kira yace mata yana a harabar gidan ta miƙe ta nufi hanyar fita, saida ta buɗe kopar gaban Motar taga ashe harda su twins yazo da yake Motar tinted ce gaba ɗaya an yi masu wanka suna sanye da kaya iri ɗaya suna ganinta Adam ya washe mata baki Abie kuma yay mata ɗan murmushi duk suka miko mata hannu suna son ta ɗaukesu suna faɗin Momy, saida ta zauna sannan ta ruƙe su gaba ɗaya ya tashi Motar suka tafi, bayan sun hau hanya take ce mashi ashe su Gwaggo sun tafi ya ɗaga mata kai tace ta kirata har sau biyu bata kusa da wayar, shiru suka ɗanyi can ya tambayeta lafiya gidan Nameer ɗin tay faffaɗan murmushi idonta akan shi tace mashi laifi yayi ne shine aka kaita rarrashi Haisam ɗin ya ɗan buɗa ido tare da ɗage gira sai kuma yay murmushi ba tare da yace komai ba, suna cikin tafiyar take tambayar shi yaushe zata je Katsina ya bata amsa da Us zasu tafi tace bazata je sallama ba yace in tana so sai taje amman yana son zasu je Adamawa su duba jikin arɗo yaji su Dad ɗinta suna faɗi ma Dad ɗinshi bai lafiya, sosae taji daɗi jin zasu je tace mashi eh bai jin daɗi yace Ok cikin next week sai suje.
Bayan sallar Azahar su Aunty yan Kano suka dawo an cika su da abubuwan arzuƙi Jidderh harda kukan baro Aunty Laila duk tayi sukuku koda ana Maganar Lailar bayan sun dawo sai ta sake saka wani sabon kukan Hajiya na faɗin itama ba Auren zata yi ta tafi ba, Bayan sallar La'asar su Hajiya Maryam suka wuce lagos su Hajiya Zainab ma lokacin suka tafi harda Fauzy.
Alhamdulillah Yan Katsina sun isa lafiya sai fatan Allah ya huta gajiya, a ranar bayan sallar isha duk suna zaune a cikin parlon Gwaggo suna yin hirar bikin baka jin komai sai fullanci dake tashi su innarsu Altine sai zuzuta gidan Mino suke suna faɗin ai Aljannar duniya aka kaita, suna cikin yin firar Amadu da Kamalu suka shigo jin firar da suke ne yasashi kunna Vedio ɗin gidan Minon da yayi lokacin da suke zagayawa ya miƙa ma Yadikko ta fara gani, sakin baki tay da tsananin mamaki take kallon Vedio ɗin tana faɗin yanzu anan Minon take aka bata amsa da eh su Altine da basu je ba duk sun zagayeta sun saki baki galala suma suna kallo, ƙarshe dai kukan farinciki Yadikko ta saka ta hau gode ma Allah da kuma Gwaggo tana faɗin koda tayi aikatau a Abuja bata ta6a tunanin wani nata zai zauna a can ba balle kuma ƴarta, inna Mero matar arɗo ce tace hada halin kirkinta yaja mata yadda ta ruƙe ƴaƴan kishiyarta da Amana bata zalunce su ba ta ɗaukesu tamkar nata gashi nan hakan yayi mata rana tunda data zalunce su ba yadda za'ai Gwaggo ta ruƙa mata ɗiya har itama tayi aure gidan daula su Kakar Minon suka shiga faɗin hakane wllh Yaya kuwa duk tabi tasha jinin jikinta sai murmushin yaƙe take, suna haka wayar Kamalu ta fara ringing ya kai idon shi kan screen ɗin yaga baƙuwar lamba saida ya fito waje saboda hayaniya sannan ya ɗaga tare da yin sallama daga ɗayan bangaren zazzaƙar muryar mace ta amsa mashi tare da tambayar ya yake ya bata amsa da lafiya lou kafin ya tambayi wacece, farko shiru tayi kamar bazata tanka ba saida ya ƙara tambaya sannan tace kenan data amshi number ɗin shi tace zata kira yay saving bai yi ba kenan, jin haka yasa ya ganeta da sauri yace tayi haƙuri ya manta ne da yake lokacin jiran shi ake tace Ok kafin ta tambayi ya suka koma yace Alhamdulillah itama ya tambayeta sun koma ne ko suna Abuja tace mashi No sun koma, ɗakinsu ya nufa suka cigaba da yin wayar saidai itace ke fara yin magana sannan yayi harda tambayarshi game da karatunshi ya bata amsa da bayan ya gama Secondary acan garin su bai cigaba ba dalilin da yasa yanzu ya dawo nan kenan don ya cigaba har ma ya siya Jamb zai yi tace Ok tare da yi mashi fatan Akhairi yayi mata godiya daga baya tace mashi tana son zasu zama Friends in ba damuwa har saida ya jinjina Maganar a ran shi don baiyi zaton jin hakan daga wurinta ba jin yayi shiru tace ko bazai yi abota da ita ba, da sauri yace a'a zasu yi suka cigaba da yin wayar kafin daga baya sukai sallama ya tashi ya koma shago.