Sashe 89
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayan sun iso parking space d'in shi ya shiga ya fiddo mata da Motar cikin harabar, bud'e kopar driver seat d'in yay ba tare daya fito ba yace mata ta bari suje kawai ta nok'e mashi kai tana d'an yamutsa fuska tace to in ba'a bari tana fita ita kad'ai ya za'ai ta saba, shiru ya d'anyi yana kallon ta har lokacin idanun shi a d'an lumshe suke, ba yadda ya iya tunda ta nuna tana so ya fito ita kuma ta shiga ta zauna sai faman sakin murmushi take bayan ta daidaita natsuwar ta ya rufe mata kopar, sauke glass tayi ta kashe mashi ido tare da furta kada ya damu ai yasan matar shi nada saurin gane abu yay murmushi kawai tace ya shigo ta aje shi a bakin gate sai ya koma ya girgiza kai yace zai koma, yana tsaye taja Motar ta tunkari gate Officer ya taso ya zuge mata shi da zata fita ya d'aga mata hannu tare da Fad'in Allah ya tsare ta sakar mashi horn, Jama'a kuzo kuga Fatuu yar fillo na tuk'a Jeep abun na Allah ne, bata yi tunanin tsayawa ba a gidan su shagon Kawu Amadu ma a rufe yake tasan bai wuce yana ciki yana bacci ta wuce.
Alhamdulillah, lafiya lou ta k'araso kopar gidan su Fauzyn, bayan ta parker ta fito kopar baya ta bud'e ta d'aukko basket d'in Abincin bayan ta rufe Motar tana niyyar nufar cikin gidan wayarta ta fara ringing tun bata ga mai kiran ba ta gane Haisam ne, d'auka tayi tana yar dariya tace ya kwantar da hankalin shi gata ta iso lafiya a hankali ya furta Alhamdulillah, tambayar shi tayi halan ma bai koma baccin ba yace mata ya kasa Saboda tunanin ta tane dariya tace to ai yanzu sai ya koma kafin ai la'asar ya furta Ok, tambayar ta yay yaushe zai zo ya dawo da ita tay d'an Jim kafin tace to asaman mi zai zo ko ya bari ta dawo da sauri yace a'a indai zata kai dare to bazata yi driving ba, k'arshe Tk tace to ya turo sai ya dawo da ita yace Ok, ba kowa a cikin parlon lokacin da ta shiga yaran Aunty Mareeya na tahfiz, sallama ta tsaya tana yi a cikin parlon jin shiru yasa tayi tunanin k'ilan bacci suke ta nufi d'akin Fauzy, tura kopar tayi ta shiga da sallama tana shiga ta hango Fauzy kwance a saman gado tana facing ceiling ta d'age k'afafun ta, saida ta isa bakin gadon sannan ta ankare da ita da sauri ta kai hannu ta cire earpiece d'in dake a kunnanta ta tashi zaune jikinta sanye da jeans da shirt, waro ido tay alamar mamaki Fatun ta zauna a bakin gadon bayan ta aje basket din,
"Yaushe kika zo har ban ji shigowar ki ba?" Fauzy ta tambaya da alamun Mamaki, yar harararta Fatuu tay tace "Yaushe dama zaki ji na zo kin dad'e kunnuwa" dariya tay tayi mata sannu da zuwa Fatun ta amsa,
"Ya yi kyau Amaryar Ya Haisam Mom twins in sha Allah, wannan wanka haka kinga yadda kika had'u sai kikai kaman wata shuwa Arab wllh" yar dariya Fatuun tayi "godiya nike Amaryar Sameer in sha Allah" yanayin fuskar Fauzy ne ya canza tana d'an murmushi had'i da d'an ta6e baki Fatun tace ita da zata ce Allah ya yarda tay murmushi kawai,
"ina Ya Haisam d'in shi ya kawo ki?" Girgiza mata kai tay tace ita kad'ai tazo tace Napep ta hawo kenan, k'ara girgiza kai tay tace a Motar ta, da alamun mamaki Fauzy tace "inyee, kice hannun ki ya fad'a sosae" kai ta d'aga mata tana murmushi, shiru suka d'an yi duk suna d'an murmushi Fauzy na son tambayar ta yadda sukai da Haisam ta kasa can dai tay k'arfin halin ce mata ta tambayi Ya Haisam d'in tace mata eh,
"to ya kukai da shi ne?" Wani kallo mai kamar harara tayi mata tace "ba ke zan fad'i mawa ba wadda ta bani sak'on zan fad'i ma yadda mukai dashi" gyad'a kai tayi tace Allah ya bata hak'uri Fatun ta saki dariya, tambayar ta tayi Aunty Mareeya tace mata tana d'aki ita da mijinta k'ilan ko bacci suke tun bayan dai da suka ci Abinci kowa ya shige d'aki itama tayi baccin ta farka ne,
"ko in kira maki ita a waya ne?" Da sauri Fatuu tace a'a tunda ba yanzu zata tafi ba ta k'yale ta in ta fito sunyi Maganar tace to, kallon basket d'in data shigo dashi tay tace "k'awata mi muka samu haka?" tana murmushi tace mata alkubus d'in fulawa ne tayi, matsowa bakin gadon tayi ta kai hannu ta d'aukko basket d'in, a saman gadon ta d'aura shi kafin ta kai hannu ta bud'e babbar Warmer d'in, sosae Alkubus d'in yayi kyau ya bada shape d'in robobin da tayi amfani dasu wurin yi, bud'e d'ayar warmer d'in tay nan miya ce da ta ji had'i tayi kitif tasha ganda mai had'e da tsoka sai uban k'amshi ke tashi, jinjina kai Fauzy tayi tana murmushi tace "Abinci mai sunan Abinci dai na a Warmers d'in yan gayu" yar dariya Fatuu tay tace "su ku kenan",
Fauzy tace ina ai su ba yan gayu bane, rufe Warmers d'in tay ta maido basket d'in k'asa bayan ta aje ta d'ago Fatuu tace bazata ci ba tace zata ci bari cikinta ya d'an k'ara fad'awa yadda zata yi mashi cin mutunci ta d'aga mata kai, hira suka shiga yi farko kan Sameer ne Fauzy na bayyana mata abunda take tunani game da ba sonta yake ba kawai hakanan zai aure ta in ma an amince mashi kenan ita kuma Fatun tana nuna mata bata tunanin hakan daga baya suka dawo hirar karatun su, suna haka aka fara kiran sallar la'asar bayan d'an wani lokaci Fatuu ta mik'e don tayi salla, cire nad'in lifaya d'in tayi ya rage doguwar rigar ce a jikinta Fauzy dake kallon ta tace "Ma sha Allah abu dai sai k'ara girma yake, kinsan har na k'osa inga Babyn ku don nasan dole zai yi ko zata yi ruwan kyau wllh" dariya kawai Fatuu tayi Fauzyn ta k'ara cewa Allah dai ya raba lafiya tace Amin ya Rabbi, toilet ta nufa idon Fauzy a kanta tana magana kan yadda hips d'in ta suma suka k'ara bud'ewa, bayan tayo Alwalar ta fito ganin Fauzyn bata da niyyar tashi yasa tace mata ita bazata yi sallar bane ta d'aga mata tace "tawa ta kai tuni" yar dariya Fatuu dake tsaye tayi tace yaushe rabonta da tace bata salla tun bayan da ta samu ciki Fauzy tace dama ita da period yanzu ai sai bayan ta haihu in kuma tana daga cikin Matan da basu yi ne in suna shayarwa to har sai ta yaye bayan na haihuwa ya d'auke ta d'aga mata kai, Hijab tasa Fauzyn ta bata bayan ta shimfid'a mata abun salla ta kabbara, nufar k'opa Fauzy tayi ta fita bada jimawa ba sai gata ta dawo ruk'e da plate ta duk'a a gaban basket d'in ta fara zuba alkubus d'in, komawa tay saman gado ta fara ci,
"Wllh k'awata ba zancen santi ba kin bala'en iya girki, yanzu dai ji yadda wannan alkubus d'in yayi dad'i sai kace na alkama ne wllh, wai don Allah ya akai kika iya sarrafa Abinci ne Allah sau da yawa ina mamakin hakan acikin rai na" ta k'arasa tare da tura tsokar nama idonta akan Fatuu data sallame salla tana kallonta da murmushi,
"wurin gwaggo da Aunty Saude na koya na kuma k'ara da tawa fasahar, in kina so ki zo in koya maki ki rink'a yi ma Angon ki Sameer yadda zaki kama mana shi da kyau" tana dariya tace wannan wane irin Abinci ne bai ci ai tasan dole yana cin masu dad'i Fatuu tace to ai itama Hubby d'inta na cin masu dad'in amman a haka yake santin nata duk in tayi hakan ai ba hujja bace da zata ce bazata k'ara koyan yadda zata rink'a yin Abinci mai dad'i ba, sosae Maganar taba Fauzy dariya tace sai kace ta ga anyi auren nasu Fatun tace ai in sha Allahu ma za'a yi Sameer bai da wata mata sai ita da yardar Allah, shiru tay don bata san mi zata ce mata ba gashi tak'i ta fad'i mata yadda sukai da Haisam,
Alhamdulillah, lafiya lou ta k'araso kopar gidan su Fauzyn, bayan ta parker ta fito kopar baya ta bud'e ta d'aukko basket d'in Abincin bayan ta rufe Motar tana niyyar nufar cikin gidan wayarta ta fara ringing tun bata ga mai kiran ba ta gane Haisam ne, d'auka tayi tana yar dariya tace ya kwantar da hankalin shi gata ta iso lafiya a hankali ya furta Alhamdulillah, tambayar shi tayi halan ma bai koma baccin ba yace mata ya kasa Saboda tunanin ta tane dariya tace to ai yanzu sai ya koma kafin ai la'asar ya furta Ok, tambayar ta yay yaushe zai zo ya dawo da ita tay d'an Jim kafin tace to asaman mi zai zo ko ya bari ta dawo da sauri yace a'a indai zata kai dare to bazata yi driving ba, k'arshe Tk tace to ya turo sai ya dawo da ita yace Ok, ba kowa a cikin parlon lokacin da ta shiga yaran Aunty Mareeya na tahfiz, sallama ta tsaya tana yi a cikin parlon jin shiru yasa tayi tunanin k'ilan bacci suke ta nufi d'akin Fauzy, tura kopar tayi ta shiga da sallama tana shiga ta hango Fauzy kwance a saman gado tana facing ceiling ta d'age k'afafun ta, saida ta isa bakin gadon sannan ta ankare da ita da sauri ta kai hannu ta cire earpiece d'in dake a kunnanta ta tashi zaune jikinta sanye da jeans da shirt, waro ido tay alamar mamaki Fatun ta zauna a bakin gadon bayan ta aje basket din,
"Yaushe kika zo har ban ji shigowar ki ba?" Fauzy ta tambaya da alamun Mamaki, yar harararta Fatuu tay tace "Yaushe dama zaki ji na zo kin dad'e kunnuwa" dariya tay tayi mata sannu da zuwa Fatun ta amsa,
"Ya yi kyau Amaryar Ya Haisam Mom twins in sha Allah, wannan wanka haka kinga yadda kika had'u sai kikai kaman wata shuwa Arab wllh" yar dariya Fatuun tayi "godiya nike Amaryar Sameer in sha Allah" yanayin fuskar Fauzy ne ya canza tana d'an murmushi had'i da d'an ta6e baki Fatun tace ita da zata ce Allah ya yarda tay murmushi kawai,
"ina Ya Haisam d'in shi ya kawo ki?" Girgiza mata kai tay tace ita kad'ai tazo tace Napep ta hawo kenan, k'ara girgiza kai tay tace a Motar ta, da alamun mamaki Fauzy tace "inyee, kice hannun ki ya fad'a sosae" kai ta d'aga mata tana murmushi, shiru suka d'an yi duk suna d'an murmushi Fauzy na son tambayar ta yadda sukai da Haisam ta kasa can dai tay k'arfin halin ce mata ta tambayi Ya Haisam d'in tace mata eh,
"to ya kukai da shi ne?" Wani kallo mai kamar harara tayi mata tace "ba ke zan fad'i mawa ba wadda ta bani sak'on zan fad'i ma yadda mukai dashi" gyad'a kai tayi tace Allah ya bata hak'uri Fatun ta saki dariya, tambayar ta tayi Aunty Mareeya tace mata tana d'aki ita da mijinta k'ilan ko bacci suke tun bayan dai da suka ci Abinci kowa ya shige d'aki itama tayi baccin ta farka ne,
"ko in kira maki ita a waya ne?" Da sauri Fatuu tace a'a tunda ba yanzu zata tafi ba ta k'yale ta in ta fito sunyi Maganar tace to, kallon basket d'in data shigo dashi tay tace "k'awata mi muka samu haka?" tana murmushi tace mata alkubus d'in fulawa ne tayi, matsowa bakin gadon tayi ta kai hannu ta d'aukko basket d'in, a saman gadon ta d'aura shi kafin ta kai hannu ta bud'e babbar Warmer d'in, sosae Alkubus d'in yayi kyau ya bada shape d'in robobin da tayi amfani dasu wurin yi, bud'e d'ayar warmer d'in tay nan miya ce da ta ji had'i tayi kitif tasha ganda mai had'e da tsoka sai uban k'amshi ke tashi, jinjina kai Fauzy tayi tana murmushi tace "Abinci mai sunan Abinci dai na a Warmers d'in yan gayu" yar dariya Fatuu tay tace "su ku kenan",
Fauzy tace ina ai su ba yan gayu bane, rufe Warmers d'in tay ta maido basket d'in k'asa bayan ta aje ta d'ago Fatuu tace bazata ci ba tace zata ci bari cikinta ya d'an k'ara fad'awa yadda zata yi mashi cin mutunci ta d'aga mata kai, hira suka shiga yi farko kan Sameer ne Fauzy na bayyana mata abunda take tunani game da ba sonta yake ba kawai hakanan zai aure ta in ma an amince mashi kenan ita kuma Fatun tana nuna mata bata tunanin hakan daga baya suka dawo hirar karatun su, suna haka aka fara kiran sallar la'asar bayan d'an wani lokaci Fatuu ta mik'e don tayi salla, cire nad'in lifaya d'in tayi ya rage doguwar rigar ce a jikinta Fauzy dake kallon ta tace "Ma sha Allah abu dai sai k'ara girma yake, kinsan har na k'osa inga Babyn ku don nasan dole zai yi ko zata yi ruwan kyau wllh" dariya kawai Fatuu tayi Fauzyn ta k'ara cewa Allah dai ya raba lafiya tace Amin ya Rabbi, toilet ta nufa idon Fauzy a kanta tana magana kan yadda hips d'in ta suma suka k'ara bud'ewa, bayan tayo Alwalar ta fito ganin Fauzyn bata da niyyar tashi yasa tace mata ita bazata yi sallar bane ta d'aga mata tace "tawa ta kai tuni" yar dariya Fatuu dake tsaye tayi tace yaushe rabonta da tace bata salla tun bayan da ta samu ciki Fauzy tace dama ita da period yanzu ai sai bayan ta haihu in kuma tana daga cikin Matan da basu yi ne in suna shayarwa to har sai ta yaye bayan na haihuwa ya d'auke ta d'aga mata kai, Hijab tasa Fauzyn ta bata bayan ta shimfid'a mata abun salla ta kabbara, nufar k'opa Fauzy tayi ta fita bada jimawa ba sai gata ta dawo ruk'e da plate ta duk'a a gaban basket d'in ta fara zuba alkubus d'in, komawa tay saman gado ta fara ci,
"Wllh k'awata ba zancen santi ba kin bala'en iya girki, yanzu dai ji yadda wannan alkubus d'in yayi dad'i sai kace na alkama ne wllh, wai don Allah ya akai kika iya sarrafa Abinci ne Allah sau da yawa ina mamakin hakan acikin rai na" ta k'arasa tare da tura tsokar nama idonta akan Fatuu data sallame salla tana kallonta da murmushi,
"wurin gwaggo da Aunty Saude na koya na kuma k'ara da tawa fasahar, in kina so ki zo in koya maki ki rink'a yi ma Angon ki Sameer yadda zaki kama mana shi da kyau" tana dariya tace wannan wane irin Abinci ne bai ci ai tasan dole yana cin masu dad'i Fatuu tace to ai itama Hubby d'inta na cin masu dad'in amman a haka yake santin nata duk in tayi hakan ai ba hujja bace da zata ce bazata k'ara koyan yadda zata rink'a yin Abinci mai dad'i ba, sosae Maganar taba Fauzy dariya tace sai kace ta ga anyi auren nasu Fatun tace ai in sha Allahu ma za'a yi Sameer bai da wata mata sai ita da yardar Allah, shiru tay don bata san mi zata ce mata ba gashi tak'i ta fad'i mata yadda sukai da Haisam,