← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 108 OF 211

Sashe 108

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read

"Wane suna kike so a sa masu?' calmly ya tambayeta tana murmushi tace mashi ai shine Baba ko shi yakamata ya zabar masu ya d'an girgiza kai yace ita tafi cancanta ta za6a masu sunan da take so tay d'an jimm kafin tace to shi ya zaba ma d'aya itama haka jin yayi shiru ta kai idanunta da suka shishshige ta kalle shi ta furta "hakan yayi maka?" lumshe mata ido yay tace to wane suna zai za6ar mashi yay d'an shiru kafin yace sunan Dad d'in shi ta jinjina kai tace yayi, tambayar ta yay ita wane suna ta za6ar ma shi tana ta murmushi tace sunan Kakan su Mijin Hajiya yanayin kallon da yake mata ne ya sauya da d'an alamun mamaki yace ita bata so asa mashi sunan Dad d'inta ne tace "ina so, amman dai nafi son asa wanda nace Saboda Hajiya nasan zata ji dad'i sosae" shiru yay yanata kallon ta can taji yace hakan bazai zama son kai ba kuwa har saida tayi yar dariya tace to miye abun son kai ai duk d'aya ne ko kuma sunan Baffan nata ko in ta k'ara haihuwar ba sai asa ba, da mamaki ya furta "zaki k'ara kenan?" shiru tay ta kasa bashi amsa a ranta tana tuna wuyar da tasha wadda yanzu har ta zama labari don bata wani jin ciwo a jikinta saidai rashin k'arfi tana jin ta wani irin fayau daba cikin, ce mashi tayi ai dole ta k'ara tunda yanzu ta fara, "amman dai wahalan yayi yawa gaskiya I think ba sai kin k'ara ba"

"Baka son Ya'ya ne?" Amsa ya bata da yana so amman tunda abun akwae wuya sai a hak'ura kawai tana yar dariya tace to ai duk haka ake haihuwan a haka ma ita nata da Sauk'i ya d'an ta6e baki yace haka wai Aunty tace, ce mashi tay yayi masu hudubar ya ce to bayan ya gama ya d'ago tace ko na hannun shi asaka mashi sunan Grandpa din tunda shine babba sai wannan asaka mashi sunan Dad ya d'aga mata kai slowly ya furta hakan yayi, mik'a mata Adam d'in yayi ya d'aukko na jikinta wato Aliyu shima ya fara yi mashi yana gamawa Aunty tazo ta tambayi an saka masu sunan yace mata eh ta tambayi wanda aka saka ya fad'i mata, jinjina kai tayi tace "Ma sha Allah, Allah ubangiji ya raya mana su ya Albarkaci rayuwarsu" Haisam ne ya amsa ita kuma Fatun a cikin rai ta amsa Auntyn ta k'ara cewa "Yakamata a kira gida a sanar masu nasan yanzu tunda Asuba tayi zasu gane bamu nan gashi duk mun taho ba wayoyi" Haisam ne yace mata bari in yayi salla sai yaje gidan ya fad'i tace to, bayan tafiyar Haisam su Nurse Haleema wurin gadon suka zo suka tsatsaya sai faman santin yaran suke gaba d'aya suma sai faman washe baki suke Nurse Chioma tace ita tunda ake haihuwar Twins a Asibitin ba'a ta6a haihuwan wanda suka matuk'ar bata sha'awa ba kaman wannan wllh ji take kaman a bata su kyauta Aunty dake dariya tace ai ga Mom d'in su nan ta tambayeta ta bata da sauri Chiomar tace ita tama fara bayan agabanta akai nak'udar su, Nurse Haleema ma Addu'ar Allah ya bata irin su tayi da sauri Chioma tace aikuwa ba bak'ar fata ba wllh bazata haife su ba ita bak'a bak'a mai d'an hanci Mijinta bak'i hancin shi mai d'an fad'i taya zasu Haifa irin su gaba d'aya aka saka dariya Haleemar ta kai hannu ta 6aketa a shoulder, mik'ewa Aunty tayi tace masu su kai babies d'in d'ayan gadon bari ta taimaka ma Mom dinsu ta tsaftace jikinta duk suka ce to, bayan ta taimaka ma Fatuu ta mik'e rigar jikinta duk ta 6aci da yake mai haske ce Aunty na ruk'e da ita suka nufi toilet wani iri take jin tafiyar ta don ma Allah ya taimake ta ko K'ari ba'a mata ba don Aunty harda Olive oil tayi mata amfani wurin fitowar na farkon.

Fitowa Dad yay don tafiya Masallaci saida yaje ya taso su Affan da Mubeen kamar ko yaushe suka tafi, lokacin da suka je parking space yayi tunanin ganin Haisam acan amman sai bai gan shi ba hakan yasa shi cewa su d'an jira shi, bayan d'an wani lokaci yayi tunanin kiran shi saidai har wayar ta yanke bai d'aga ba hakan yasa shi k'ara yin tunanin ko ya riga ya tafi duk da yasan ko yaushe a tare suke tafiya, koda suka je Masallacin basu gan shi a can ba har aka gama sallar suka juyo Dad nata d'an tunanin to ko lafiya Haisam d'in bai je salla ba, lokacin daya shiga Bedroom d'in shi Mom na zaune akan prayer mat bata dad'e data gama sallar ba tana tasbih, zama yay daga gefenta a bakin gado ta juyo ta kalle shi da d'an murmushi ta gaishe shi ya amsa, ganin yayi shiru yana kallon k'asa kaman mai tunanin wani abu yasa ta tambayi Lafiya ya d'ago yace mata Son ne bai je Salla ba kuma yanata kiran layin shi yana shiga bai d'auka ba tace to ko ya makara ne shine yayi sallar a gida, girgiza mata kai yay yace ai tun da zasu je ya kira shi bai d'aga ba sai yayi tunanin ko ya tafi ne to acan ma basu iske shi ba har aka gama sallar kum bai zo ba yanzu bayan sun dawo saida ya k'ara kiran shi tana ta ringing still bai picking ba,
Chapter 108 · 0% Book details