← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 147 OF 211

Sashe 147

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Shirye shiryen biki nata kankama a dukkan 6angarorin angwaye da amaren, Bayan sati guda Fatuu ta taho da wata babbar Mata da zata zo Kano harda iyalinta Haisam ya haɗasu don su taimaka mata da su twins dama damuwar shi kenan yadda zata yi dasu shiyasa ma bata wani kwaso kaya ba iya ɗan babban trolley ne da yar jaka sauran sai zasu zo su taho mata dasu, bayan sun iso Kano Matar tace mata in ba jirgin da zai je Katsina yanzu sai su tafi gidanta kafin lokacin tafiyar yayi Fatuu na murmushi tace mata ai da Haisam ya siya mata ticket online akwae wanda zai tashi bada daɗewa ba yaran Matar suka shiga faɗin wayyo ba haka suka so ba sun so su bisu gidansu don basu gaji da ganin su twins ba ita dai Fatuu murmushi kawai take, itama Matar da wani matashin mutum da zai tafi Katsina ta haɗa su don ya taimaka mata shima a first class zai zauna inda Fatun zata zauna, lokacin Haisam ya kira don yaji in sun sauka Fatuu taba Matar waya sukai magana sosae yayi mata godiya tana ta fara'a irin tasu ta manyan Hajiyoyi tace ai ba komai duk yima kaine tana fatan wata rana in yazo ƙasar zai kawo mata su yace in sha Allah daga baya ta sanar dashi itama ta damƙa su a hannun wani da zasu zauna tare don ta bincika bata samu mace da zata zauna anan ba yace to ba komai ya ƙara mata Godiya kafin sukai sallama, Wuraren karfe sha biyu na rana suka sauka Katsina, cike da Farinciki su Gwaggo da kawu Amadu da Amarya Mino sai Tk daya kai su suka tarbe ta basu zo da Kamalu ba shi Kawu Amadu ya baro ma shago, kowa yay mamakin ganin yadda Fatuu ta canza har sun kasa rufe bakunansu gaba ɗaya hutu ya zauna mata sosae tayi 6ul6ul da ita ga skin ɗinta ta ƙara mulkewa ta ƙara haske in tayi dariya abun gwanin burgewa ga cikinta har ya ɗan fito, su Twins kam abun ba'a magana su wannan tun a jirgi aketa santin su, sai so suke su ɗauke su amman sun ƙi yarda dama Adam ne me ɗan yarda a ɗauke shi shima sai yaga Fatun na a kusa, da ƙyar ya yarda Mino ta ɗauke shi daga wurin mutumin da ya ruƙe shi a jirgi sai faman ta6e baki yake zai yi kuka Fatuu ta shiga rarrashinshi da turanci tana ce mashi itama Minon Mom ɗin shi ce, shi dai Abie na liƙe da ita da alama ma tsoronsu yake don har fuskar shi ta nuna ya waro ido tubarkalla sai bin su da kallo yake, Sosae su gwaggo sukai ma mutumin godiya yana murmushi ya nuna masu ba komai kafin sukai sallama ya tafi, bayan sun fito wurin da aka parker Motar su ukku suka shiga baya kawu Amadu ne yanzu zai tuƙa Motar don ya iya bayan tafiyar Fatuun Tk ya koya mashi da Motar tata tare da amincewarta, yana fara driving Fatuu ta shiga yaba mashi ganin har ya iya Tk dake gefen shi yace ai yanzu ba inda bai zuwa da mota, bayan sun bar Airport ɗin suna ta hira Fatuu ke tambayar Hajiya Tk na murmushi yace tana nan lafiya tana can tana jiran isowar su, lokacin da suka iso ƙopar gidansu tsayawa Fatuu tasa akai don ta gaisa da Yayanta Kamalu yana ganinta ya hau washe baki yace bari ya rufe shago yazo su ƙarasa gidan tare, a gaban Motar Tk ya matsa mashi suka tafi suna isa gate su officer suka taso suna masu sannu da zuwa daga baya aka buɗe masu gate suka shige, a gaban entrance ya parker Motar duk suka firfito lokacin Saude ta fito cikin washe baki ta nufo Fatuu itama tana ganinta ta fara mata murmushi tana zuwa ta ɗan rungumota tana mata sannu da zuwa aikuwa Abie na ganin haka ya fashe da kuka da sauri Aunty Saude ta saketa tana faɗin ashe ba'a ta6ata ta shiga ba shi haƙuri tana faɗin ai ta saketa to yay shiru ai kamar ma tana ƙara tunzura shi sai kukan yake ƙara yi ganin haka yasa Sauden cewa to ko dai tsoron baƙaƙen Mutane yake Gwaggo tace taga alama don tun ɗazu duk ya bi ya ƙanƙame Uwar tashi, ganin Abie ɗin na kuka yasa Adam shima fashewa da kukan dama ƙiris yake jira Mino ta matso dashi wurin Fatun don ta rarrashe shi, Hajiya ce ta fito tana dogara sandarta ta alfarma idanunta sanye cikin glasses ta nufo su tana faɗin ita dai tayi gajen haƙuri ta fito, ganin su twins na kuka yasa ta tambayi mi ya faru duk suke kuka Saude ta faɗi mata ta jinjina kai tana dariya tace aikuwa aiki ya same su in dai tsoron baƙaƙen mutane suke tunda ƙasar su suka zo duk akai dariya, gaishe da ita Fatuu tay ta amsa tana ta fara'a tay mata sannu da zuwa kafin tace to a shigo ciki a zauna yadda za'a gaisa sosae suka ce so ta kalli su twins da suka bita da ido tace masu barkansu da zuwa ƙasar baƙaƙen fata, tambayar ina mai gidan nata yake tay Fatuu ta nuna mata shi a hannun Mino tace wato ita kenan don tana fara ya yarda da ita duk sukai dariya, cikin gidan duk suka nufa a parlor aka zazzauna ana ƙara gaisawa da ƙara yi masu sannu da zuwa Hajiya ta tambayi Fatuu jikinta tana ta murmushi tace Alhamdulillah tay fatan Allah ƙara ingantawa ya sauketa lafiya ta amsa tare da su Saude, sake tambayar ya ta baro su Haisam Hajiyar tay tace lafiya lou duk suna gaishe su suna nan zuwa, Saude nata kallon Fatuu don komai tayi burgeta take can ta kasa haƙuri tace mata har ta canza sosae Hajiya tace ai dole yanayin ƙasa ba ɗaya ba, Maganar Abinci Hajiya tayi ma Fatuu tace gashi can an shirya akan table in kuma a kawo nan to tace eh a kawo nan cikin parlor Saude ta amsa da to ta miƙe, sallama gwaggo tayi masu Hajiya tace ta tsaya sai sun ci Abinci sannan, lafiyayyun Abinci da abun sha aka jere akan carpet duk Saude tay serving nasu abun yay kamar yar Walima har gwaggo na faɗin to kada kuma su cinye ma baƙi abinci Hajiya tace ai dama harda yan tarbar baƙin aka yi, a nutse suka fara cin abincin harda Hajiya a kan c-table aka ɗaura mata bayan ta fara ci tace ma Mino ta kawo mata Adam, kuka ya saka bayan ta kawo mata shi yana miƙa hannu alamar Mino ta ɗauke shi Hajiya ta shiga rarrashin shi tana faɗin "Haba mai gida yada tsoron Mata inata farincikin tarbarka sai kuma kaƙi yarda dani" su Gwaggo nata murmushi Hajiya ta kalli Fatuu tace "to wai ma yana fahimtata ko sai anyi turanci" amsa ta bata da eh suna gane hausa amma sun fi fahimta in akayi turanci, komawa Hajiya tayi tana rarrashin shi da turanci har ya fara yin shiru manyan idanun shi a kanta yana ta6e baki ita kuma tana ta faɗin yayi shiru shagwa6a66an maigida, lokacin da suka gama cin Abincin an kira Azahar Kawu Amadu da Tk suka tafi Masallaci gwaggo ma tayi ma Hajiya sallama su Fatuu da Mino suma suka fito don tafiya part ɗin su wanda tuni Saude ta gyara mata shi, bayan sallar la'asar lokacin Fatuu tayi wanka ta canza kaya haka su twins ma an yi masu wanka an canza masu kaya iri ɗaya suka tafi gidan Gwaggo, a can gidan ma anyi masu abincin tarbar su Fatuu tace sai anjima sai suci tunda yanzu basu jin yunwa suka shiga tattaunawa game da shirye shiryen bikin Minon nan Gwaggo ke sanar mata Abbas ya bata gudunmawar dubu ɗari biyu Fatuu taji daɗi tay godiya da Allah ya saka da Alkhairi, anan Haulat tazo ta iske Fatuu tsaf tsaf da ita tana sanye cikin doguwar rigar material mai kyau tayi rolling veil in ka ganta baka ta6a cewa ta ta6a aure tana ruƙe da hannun ɗiyarta lokacin data zo itama tsaf da ita an sa mata kaya masu kyau haka kanta ba laifi tana da gashi ma sha Allah, gaba ɗaya sunyi farincikin ganin juna Fatuu tace ai da tana niyyar zuwa gidansu bayan Magrib shiyasa bata kirata ba ta tambayi ya akai tasan ta dawo tace mata kawu Amadu ne ya kirata ya sanar mata, nan suka shiga yin hira itama saida ta tanka kan yadda Fatun ta canza tana dariya tace ai itama ta canza taji daɗin ganinta haka don da alama ta kwantar da hankalinta Haulat ɗin tace mata eh, duk yadda Haulat taso ta ɗauki su twins sun ƙi yarda kuma sun ƙi bari Fatuu itama ta ɗauki ɗiyar Haulat ɗin da tayi yunƙurin ɗaukarta sai su fashe da kuka abun ma sai ya zama abun dariya, tana nan har aka yi sallar Magrib bayan an gama ta tafi.
Chapter 147 · 0% Book details