Sashe 75
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ina a School" ta bashi amsa a hankali bayan ta d'ago sun sake had'a ido nashi idanun a d'an lumshe kamar dai yadda Haisam ke yi, ce mata yay yanzu nan a Class take da sauri ta girgiza mashi kai "a'a ina a Hostel ne an tashi daga Class" shiru ya d'an yi kafin ya tambayi mi take a Hostel ta bashi amsa da ai ita boarder ce, maida idon shi yay gefe yaci gaba da yin abunda yake yi wanda bata san ko minene ba, bayan d'an wani lokaci ba tare daya juyo ba yace mata ba ayin Day ne School en nasu,
"A'a ana yi, ai ko matar Ya Haisam Day take ni kuma Saboda ba garin nike ba yasa nike yin boarding" sai lokacin ya juyo suka had'a ido yace mata amman ba tace tana a wurin Elder sister en ta bane, shiru tay tana kallon shi sam tama manta da tace mashi haka don lokacin da sukai Maganar a rud'e take, tana kikkafta idanu tace mashi eh haka ne amman da Weekend ne take zuwa wurin ta, shiru ya d'an yi sai kuma yace to miyasa bazata zauna a wurin ta ba,
"Ai a boarding d'in an fi yin Karatu ne shiyasa" tana rufe baki taga yayi mata wani kallo mai kaman harara kawai sai ji tay yace sai dae dama in ita bata da k'ok'ari ne, waro ido tay ya d'age mata gira ya furta "Yeah" d'an murmushi tay tare da yamutsa fuska tace mashi wllh ita tana da k'ok'ari kuma sosae, tunda suka fara Maganar sai lokacin yanayin fuskar shi ya canza yay kaman zai murmushi tare da d'an ta6e bakin shi ganin haka yasa ta k'ara cewa "ai nan School d'in ma wllh mara k'ok'ari ma bai iya yin ta, da banda k'ok'ari ai da tuni ma sun kora ni tun kafin in fara karatun" yamutsa fuska yayi tare da d'an murmushi itama murmushin take tana kallon shi suna haka ya d'ago hannun shi ya d'an shafi beard d'in shi can ya furta dama ya ganta online ne shine yayi mata magana just to check on her, bata ji abunda yace ba sosae hakan yasa tace mashi bata ji mi yace ba dama tunda suka fara Vedio call d'in k'asa k'asa take jin voice d'in shi, shiru yay baida alamar zai k'ara fad'in abunda yace d'in, rantsuwa tay mashi tace bata ji ba yace mata Shikenan, marairaice mashi tay tana yamutsa fuska ta furta "Don Allah kayi hakuri wllh kaji na rantse banji mi kace ba" yanayin sautin Maganar tata da yar shagwaba tayi ta wanda ita bata san tayi hakan ba kawai sai gani tay yay d'an murmushi har gefen kumatun shi ya d'an lotsa, lumshe idon shi yay tare da yin yar hamma ya kai hannun shi ya rufe bakin bayan ya gama ya bud'e idon suka shiga cikin nata tay mashi zuru sai lokacin ya maimaita mata abunda yace d'in tay murmushi kafin tace ta gode, shiru bai ce komai ba sai ma d'age kai da yayi idanun shi a lumshe, bin shi da ido Fauzy tay sun d'an d'auki lokaci a haka can ya d'ago slowly ya fara bud'e idanun nashi suka shiga cikin nata, d'age mata gira yay ya furta "any problem?" da sauri ta girgiza mashi kai tace mashi sai anjima ya jinjina mata kai a hankali ya furta "Take care" kai ta d'aga mashi tana murmushi kafin ta kai hannu tay disconnecting kiran, bayan ta kashe kiran Murmushi ta shiga saki ba abunda take gani sai fuskar Sameer hakanan take jin komai nashi na burge ta bata ta6a zaton haka daga gare shi ba a yadda farko take mashi kallon mai girman kai, maida bayanta tay jikin bango ta d'age kai tana cigaba da sakin murmushi tana haka taji wayarta tayi k'ara alamar shigowar sak'o, sauke kanta tayi ta fara k'ok'arin duba sak'on, lokacin data ga sak'on wanda credit alert ne na kud'i dubu d'ari biyar aka turo mata gaba d'aya zaro idanu waje tay ta kai d'ayan hannunta ta dafe k'irji baki bud'e take kallon screen d'in wayar, mamaki ne ya cikata don ta gane Sameer ne ya turo su, "to ya akai ya san account number d'in ta??" Itace tambayar da ta shiga jefa ma kanta, zuciyar ta ce ta fara raya mata k'ilan lokacin da ya d'auki wayar a gidan daya kaita wanda dama a lokacin take tunanin ya d'auki number d'in wayarta can kuma ta k'ara yin tunanin ko kuma ranar da ya bata waya da suka taho a hanya ya amshi wayar tabbas a d'aya daga cikin hakan ne ya d'auka, tama rasa murna zatai ko mi don sosae mamaki ya kamata na yadda ya turo mata wannan iyayen kud'in, ta d'an d'auki lokaci tana ta mamakin kafin tay tunanin kiran shi don tay mashi godiya, sau biyu ta kira bai d'aga ba kiran na biyun ma kafin ya katse taji yayi rejecting, Aunty Mareeya ce ta fad'o mata a rai da sauri hannunta har yana rawa ta shiga kiran ta, tana yin ringing biyu ta d'auka, gaisawa sukai tay mata ya School da yake yau Fauzyn ta dawo daga Weekend,
"Aunty Albishirin ki!" tana rufe baki da sauri tace "Goro d'an Governor ya kira ne? don Allah Fauziyya kice man shi ne ya kira" dariya Fauzy ta kyalkyace da ita Aunty ta buga wani tsoki a k'agare ta furta "dalla ni ki fad'i man in shine d'in ya kira" tsagaitawa da yin Dariyar tay tace mata eh ya kira, wata uwar hamdala ta saki ta fara fad'in Alhamdulillah Allah ya amsa Addu'ar da take tayi,
"Ya kukai da shi da ya kira?" Cikin washe baki Aunty ta tambaya,
"Kawai fa na hau online sai gani nayi an yi man magana da bak'uwar lamba na shiga cikin chat naga an tambayi ya nike to dana ga bansan ko waye ba sai na duba hoton dp naga shine ina cikin dubawar ma sai ga Vedio call ya shigo..
......." Nan ta kwashe komai ta fad'i mata, a d'okance Aunty tace "Kai Ma sha Allah abu yayi dad'i wllh, ai kece da shegiyar kafiya wllh ba yadda banyi dake ba akan ki kira ki gaida shi amman kika k'i da yanzu an wuce wurin k'ilan anata Maganar saka rana ma, su mutane irin wannan ai ba'a masu sanya tunda dai an samu dama irin haka ma mantawa suke da mutum wllh shima nasan Allah ne ya amsa Addu'a ta ya karkato hankalin shi gare ki, to yanzu Shikenan iya gaisuwar kukai ko da wani abu?" Fauzy dake ta yar dariya tace "a'a....." bata k'arasa ba Aunty ta katseta "yace zai zo kenan?" Dariya Fauzy ta k'ara sakawa tace "ni fa Aunty bamu yi hakan da shi ba, kud'i ne ya turo man yanzu bayan mun gama wayar 500k bamma san ya akai ya samu account number dina ba amman nafi tunanin k'ilan dai d'auka yay a wayata" jin har ta gama Maganar Auntyn bata ce komai ba yasa ta kira Sunanta tace mata tana jin ta, wata uwar ajiyar zuciya Aunty Mareeya ta sauke a razane ta furta "Yar gidan Hajiya dubu d'ari biyar fa kika ce, rabin miliyan fa kenan!"cike da tabbatarwa Fauzy tace mata eh wllh gama alert d'in nan, shewa Aunty Mareeya ta saka tana fad'in "Wayyo Allah dad'i kashe ni ni Mariyatu, Yar gidan Hajiya na fad'i maki komar ki ta kamo mana gingimemen kifi wllh Manya masu babbar kyauta, wannan irin kyauta haka farko Wayar fin miliyan yanzu kuma kud'i rabin miliyan a hakan ma wai ba soyayya ake ba to inaga in an fara Soyewa kina sakar mashi kalamai ai sai baki ATM kawai wllh" dariya sosae Fauzy ke yi itama Aunty dariyar take ta farinciki,
"Ina ganin yakamata a kira su Hajiya a sanar masu game da shi" da sauri Fauzy tace "a'a Aunty ni ina ganin bai kamata a sanar dasu ba...." Katseta tay cikin d'aga murya tace to Saboda me, Fauzyn tace "Saboda ban son suma su saka rai kamar yadda kika saka tunda kinga ba wani abu ke tsakanin mu dashi ba kece kawai kike ganin sona yake"
ajiyar zuciya Aunty ta sauke "hakane, amman yanzu dole wani abun ya shiga tsakanin ku na fahimci in aka daka ta tashi ba ranar da zai fito ya bayyanar da abunda ke ran shi don haka ki zo gida inada Meeting da ke" Fauzy dake dariya tace duka ba yau ta dawo Makarantar ba tace eh tazo dai tana son ganinta,
"amman yanzu fa yamma tayi Aunty ko a bari sai gobe in an tashi Class direct sai in taho nan"
"Ok hakan yayi, yauwa in kika fito ki tsaya wurin mai gashin kazar nan na wurin Asibiti ki siyo mana dankwala dankwala guda ko ukku koma biyar sannan nasan baki rasa sanin inda ake saida su shawarma ki tsaya ki siyo mana har da pizza dasu ice cream ba sai kin siyo lemu ba tunda akwae anan ni kuma nan zan yi had'addan Abinci don wannan abun farincikin dole muyi Walima" dariya sosae Fauzy ke yi tace to sai ta turo kud'in da zata siyo abubuwan data lissafan aikuwa a hasale tace su kud'in da aka turo matan don ta kalle su ne ya turo mata, cike da ankararwa Fauzyn tace "amma Aunty an ta6a mashi kud'i kuwa....",
"A'a ana yi, ai ko matar Ya Haisam Day take ni kuma Saboda ba garin nike ba yasa nike yin boarding" sai lokacin ya juyo suka had'a ido yace mata amman ba tace tana a wurin Elder sister en ta bane, shiru tay tana kallon shi sam tama manta da tace mashi haka don lokacin da sukai Maganar a rud'e take, tana kikkafta idanu tace mashi eh haka ne amman da Weekend ne take zuwa wurin ta, shiru ya d'an yi sai kuma yace to miyasa bazata zauna a wurin ta ba,
"Ai a boarding d'in an fi yin Karatu ne shiyasa" tana rufe baki taga yayi mata wani kallo mai kaman harara kawai sai ji tay yace sai dae dama in ita bata da k'ok'ari ne, waro ido tay ya d'age mata gira ya furta "Yeah" d'an murmushi tay tare da yamutsa fuska tace mashi wllh ita tana da k'ok'ari kuma sosae, tunda suka fara Maganar sai lokacin yanayin fuskar shi ya canza yay kaman zai murmushi tare da d'an ta6e bakin shi ganin haka yasa ta k'ara cewa "ai nan School d'in ma wllh mara k'ok'ari ma bai iya yin ta, da banda k'ok'ari ai da tuni ma sun kora ni tun kafin in fara karatun" yamutsa fuska yayi tare da d'an murmushi itama murmushin take tana kallon shi suna haka ya d'ago hannun shi ya d'an shafi beard d'in shi can ya furta dama ya ganta online ne shine yayi mata magana just to check on her, bata ji abunda yace ba sosae hakan yasa tace mashi bata ji mi yace ba dama tunda suka fara Vedio call d'in k'asa k'asa take jin voice d'in shi, shiru yay baida alamar zai k'ara fad'in abunda yace d'in, rantsuwa tay mashi tace bata ji ba yace mata Shikenan, marairaice mashi tay tana yamutsa fuska ta furta "Don Allah kayi hakuri wllh kaji na rantse banji mi kace ba" yanayin sautin Maganar tata da yar shagwaba tayi ta wanda ita bata san tayi hakan ba kawai sai gani tay yay d'an murmushi har gefen kumatun shi ya d'an lotsa, lumshe idon shi yay tare da yin yar hamma ya kai hannun shi ya rufe bakin bayan ya gama ya bud'e idon suka shiga cikin nata tay mashi zuru sai lokacin ya maimaita mata abunda yace d'in tay murmushi kafin tace ta gode, shiru bai ce komai ba sai ma d'age kai da yayi idanun shi a lumshe, bin shi da ido Fauzy tay sun d'an d'auki lokaci a haka can ya d'ago slowly ya fara bud'e idanun nashi suka shiga cikin nata, d'age mata gira yay ya furta "any problem?" da sauri ta girgiza mashi kai tace mashi sai anjima ya jinjina mata kai a hankali ya furta "Take care" kai ta d'aga mashi tana murmushi kafin ta kai hannu tay disconnecting kiran, bayan ta kashe kiran Murmushi ta shiga saki ba abunda take gani sai fuskar Sameer hakanan take jin komai nashi na burge ta bata ta6a zaton haka daga gare shi ba a yadda farko take mashi kallon mai girman kai, maida bayanta tay jikin bango ta d'age kai tana cigaba da sakin murmushi tana haka taji wayarta tayi k'ara alamar shigowar sak'o, sauke kanta tayi ta fara k'ok'arin duba sak'on, lokacin data ga sak'on wanda credit alert ne na kud'i dubu d'ari biyar aka turo mata gaba d'aya zaro idanu waje tay ta kai d'ayan hannunta ta dafe k'irji baki bud'e take kallon screen d'in wayar, mamaki ne ya cikata don ta gane Sameer ne ya turo su, "to ya akai ya san account number d'in ta??" Itace tambayar da ta shiga jefa ma kanta, zuciyar ta ce ta fara raya mata k'ilan lokacin da ya d'auki wayar a gidan daya kaita wanda dama a lokacin take tunanin ya d'auki number d'in wayarta can kuma ta k'ara yin tunanin ko kuma ranar da ya bata waya da suka taho a hanya ya amshi wayar tabbas a d'aya daga cikin hakan ne ya d'auka, tama rasa murna zatai ko mi don sosae mamaki ya kamata na yadda ya turo mata wannan iyayen kud'in, ta d'an d'auki lokaci tana ta mamakin kafin tay tunanin kiran shi don tay mashi godiya, sau biyu ta kira bai d'aga ba kiran na biyun ma kafin ya katse taji yayi rejecting, Aunty Mareeya ce ta fad'o mata a rai da sauri hannunta har yana rawa ta shiga kiran ta, tana yin ringing biyu ta d'auka, gaisawa sukai tay mata ya School da yake yau Fauzyn ta dawo daga Weekend,
"Aunty Albishirin ki!" tana rufe baki da sauri tace "Goro d'an Governor ya kira ne? don Allah Fauziyya kice man shi ne ya kira" dariya Fauzy ta kyalkyace da ita Aunty ta buga wani tsoki a k'agare ta furta "dalla ni ki fad'i man in shine d'in ya kira" tsagaitawa da yin Dariyar tay tace mata eh ya kira, wata uwar hamdala ta saki ta fara fad'in Alhamdulillah Allah ya amsa Addu'ar da take tayi,
"Ya kukai da shi da ya kira?" Cikin washe baki Aunty ta tambaya,
"Kawai fa na hau online sai gani nayi an yi man magana da bak'uwar lamba na shiga cikin chat naga an tambayi ya nike to dana ga bansan ko waye ba sai na duba hoton dp naga shine ina cikin dubawar ma sai ga Vedio call ya shigo..
......." Nan ta kwashe komai ta fad'i mata, a d'okance Aunty tace "Kai Ma sha Allah abu yayi dad'i wllh, ai kece da shegiyar kafiya wllh ba yadda banyi dake ba akan ki kira ki gaida shi amman kika k'i da yanzu an wuce wurin k'ilan anata Maganar saka rana ma, su mutane irin wannan ai ba'a masu sanya tunda dai an samu dama irin haka ma mantawa suke da mutum wllh shima nasan Allah ne ya amsa Addu'a ta ya karkato hankalin shi gare ki, to yanzu Shikenan iya gaisuwar kukai ko da wani abu?" Fauzy dake ta yar dariya tace "a'a....." bata k'arasa ba Aunty ta katseta "yace zai zo kenan?" Dariya Fauzy ta k'ara sakawa tace "ni fa Aunty bamu yi hakan da shi ba, kud'i ne ya turo man yanzu bayan mun gama wayar 500k bamma san ya akai ya samu account number dina ba amman nafi tunanin k'ilan dai d'auka yay a wayata" jin har ta gama Maganar Auntyn bata ce komai ba yasa ta kira Sunanta tace mata tana jin ta, wata uwar ajiyar zuciya Aunty Mareeya ta sauke a razane ta furta "Yar gidan Hajiya dubu d'ari biyar fa kika ce, rabin miliyan fa kenan!"cike da tabbatarwa Fauzy tace mata eh wllh gama alert d'in nan, shewa Aunty Mareeya ta saka tana fad'in "Wayyo Allah dad'i kashe ni ni Mariyatu, Yar gidan Hajiya na fad'i maki komar ki ta kamo mana gingimemen kifi wllh Manya masu babbar kyauta, wannan irin kyauta haka farko Wayar fin miliyan yanzu kuma kud'i rabin miliyan a hakan ma wai ba soyayya ake ba to inaga in an fara Soyewa kina sakar mashi kalamai ai sai baki ATM kawai wllh" dariya sosae Fauzy ke yi itama Aunty dariyar take ta farinciki,
"Ina ganin yakamata a kira su Hajiya a sanar masu game da shi" da sauri Fauzy tace "a'a Aunty ni ina ganin bai kamata a sanar dasu ba...." Katseta tay cikin d'aga murya tace to Saboda me, Fauzyn tace "Saboda ban son suma su saka rai kamar yadda kika saka tunda kinga ba wani abu ke tsakanin mu dashi ba kece kawai kike ganin sona yake"
ajiyar zuciya Aunty ta sauke "hakane, amman yanzu dole wani abun ya shiga tsakanin ku na fahimci in aka daka ta tashi ba ranar da zai fito ya bayyanar da abunda ke ran shi don haka ki zo gida inada Meeting da ke" Fauzy dake dariya tace duka ba yau ta dawo Makarantar ba tace eh tazo dai tana son ganinta,
"amman yanzu fa yamma tayi Aunty ko a bari sai gobe in an tashi Class direct sai in taho nan"
"Ok hakan yayi, yauwa in kika fito ki tsaya wurin mai gashin kazar nan na wurin Asibiti ki siyo mana dankwala dankwala guda ko ukku koma biyar sannan nasan baki rasa sanin inda ake saida su shawarma ki tsaya ki siyo mana har da pizza dasu ice cream ba sai kin siyo lemu ba tunda akwae anan ni kuma nan zan yi had'addan Abinci don wannan abun farincikin dole muyi Walima" dariya sosae Fauzy ke yi tace to sai ta turo kud'in da zata siyo abubuwan data lissafan aikuwa a hasale tace su kud'in da aka turo matan don ta kalle su ne ya turo mata, cike da ankararwa Fauzyn tace "amma Aunty an ta6a mashi kud'i kuwa....",