← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 205 OF 211

Sashe 205

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

wuraren ƙarfe biyar Fanan ta kira Haisam a waya ta tambayi yana ina ya bata amsa da yana a sama suna yin lesson dasu twins tace pls in ba damuwa ya zo part ɗinta tana son ganin shi ya furta Ok, ba'a ɗau lokaci ba ya turo ƙopar yana sanye da ƙananun kaya da suka amshi jikinshi, yana niyyar yin sallama ya dakata sakamakon wani ƙyalƙyali daya zubo mashi har saida ya ɗan runtse ido, bayan ya tsagaita da zubo mashi yasa hannu yana kakka6e wanda ya maƙale mashi a jiki da saman sumar shi, yana ɗagowa ya kalli gaban shi idanunshi suka sauka akan wata yar banner da aka yi rubutu mai walwali an rubuta _"Thank you for our new home, We really love you our Husband"_ ƙayataccen murmushi ya saki ganin rubutun kafin ya juya ya kalli cikin falon wanda aka ƙawata shi da baloons wato balo kala kala sannan an aje manyan hotunan bikinsu shida Fanan da kuma wanda akayi mashi da Fatuu a Dinner ɗin su da akai a Abuja sannan an aje wanda sukai su duka da yaran su harda babban cake mai hawa biyu anyi decoration da hotunan Haisam da zasu kai biyar sannan an yi rubutu in icing an rubuta "Home sweet home" sannan daga saman baki bakin cake ɗin anyi topping da fresh fruit da suka ƙara ƙawata shi, nufo shi Fatuu da Fanan sukayi sun sha gayun ƙananun kaya riga da wando da suka bayyanar da dirin su gashin kan su gaba ɗaya sun sake shi kai kace hausa bazata fito daga bakunansu ba, ko a iya matan da Allah ya ba Haisam za'a iya cewa ba ƙaramin dacewa yay ba don mata ne da suka amsa sunan mata uwa uba gasu da hali na gari, a gabanshi suka tsaya suna sakin murmushi tare da ƙara yi mashi godiyar yanata murmushi ya ware masu hannuwanshi a tare suka faɗa jikinshi suna ta yar dariya Jidderh da abokiyar aikinta ma dariyar suke ta shiga yi masu Vedio, bayan sun ɗago daga jikinshi kamo hannuwansu yayi suka nufo ciki, a saman doguwar kujera suka zauna dama a gabanta aka aje cake ɗin, bayan zaman su Jidderh tace yakamata a kira su twins suzo a yanka cake tare dasu Fanan ta miƙe ta nufi inda wayar landline take ta kira part ɗin Haisam, Esha ce ta ɗauka cikin zazzaƙar muryarta tace waye ne ke kiran Dad to bayanan da turanci tayi Maganar Fanan na murmushi tace to Momynsu ce, waro ido Eshar tayi sai kuma tayi dariya ta kira sunanta ta amsa tare da tambayarta ina su twins tace mata gasu nan tace to suzo part ɗinta yanzun nan akwae surprise da sauri Esha ta maimaita abunda tace tare da waro ido Fanan ɗin tace mata eh, kife kan telephone ɗin tayi cike da zumuɗi ta faɗi ma su twins abunda Momy tace ta nufi hanyar fita da gudu, Esha ce ta fara shigowa da gudu tana sanye da ɗan skirt na jeans da farar t-shart bayan ta shigo su twins suka biyo bayanta suma ƙananun kaya ne a jikinsu, koda Esha taga yadda akai ma Falon da tsananin mamaki taja ta tsaya a gabansu ido waje ta furta "Wow! what a surprised!!" hannu Fanan ta miƙo mata ta nufesu tana washe baki, a saman jikinta ta ɗaurata gaba ɗaya ta ruɗe sai faman tambayar su Dad ake ma Birthday take, saida Adam ya nuna mata rubutun jikin cake ɗin sannan ta fahimci mi ake, a tare gaba ɗaya suka kama ma Haisam ɗin hannu suka yanka cake Jidderh nata masu Video, bayan an yanka kowa ya ɗauka ya bashi a baki kafin shima ya basu har shafa mashi icing ɗin jiki sukai a fuska suna ta dariyar farinciki daga baya Fanan ta kama hannunshi da turanci tayi mashi kalami masu tsuma zuciya kan muhimmancin shi a wajenta da kuma yadda take son shi ƙarshe tayi mashi godiya da Addu'oi, bayan ta gama Fatuu ma tayi suma su Esha saida sukai mashi abun dai gwanin burgewa daga baya aka shiga yin hotuna, harda music Fanan ta kunna aikuwa Esha ba ƙaramin cashewa tayi ba sosae taba mutane dariya, sosae Haisam ya yaba da abunda sukai mashi shima saidai yay masu kalamai kan yadda suke a wurinshi saida aka kira sallar Magrib suka gama.

A cikin satin akaita zuwa ganin sabon gidan da yi masu Allah yasa Alkhairi har Laila ma tazo daga Kano ita da mijinta da yaranta biyu don ta ƙara haihuwa, ranar Friday su Gwaggo suka zo da Kawu Amadu da Tk da kuma matansu sai yaransu don dukkansu sun ƙara haihuwa ita matar Tk mace ta ƙara haihuwa itama Haulat mace ce mai sunan Gwaggo wato Khadija, zuwan nasu yasa Fatuu ta ƙara zuwa Abujar kowa saida ya jinjina haɗuwar gidan akai masu Allah yasa Alkhairi da Addu'oi, a yadda suka shirya zasu bi Gwaggo ne apartment ɗin da take zama in tazo amman Fatuu ta hana tace anan zasu kwana harda gwaggon tunda ai don su suka zo, ƙarshe dai anan suka kwana don Haisam da Fanan duk sun saka baki kan su kwana anan, Washe gari Asabar bayan sunyi lafiyayyan breakfast suka shirya fita harda su Fanan da Fatuu sukai Mota ukku data Fatuu dasu Gwaggo suka zo da ita sai kuma ta Fanan sai wadda Haisam zai hau, Villa suka fara zuwa duk an nuna farincikin zuwansu karma Hajiya sosae tayi murnar ganin su akai masu tarba mai kyau, daga Villa gidan Mino suka wuce zo kaga murna har tana ce ma Gwaggo amman dai bazata koma ba har ta haihu ko Gwaggon na dariya tace a'a abunda da saura amman zata kwana biyu in ta haihun ta dawo, da ƙyar ta barsu suka tafi harda roƙonsu kan su dawo su kwana anan suka ce to ƙilan su dawo, daga nan gidan Aysha aka wuce itama taji daɗin ganinsu har ta kasa rufe baki gashi tayi masu lafiyayyan abinci don tasan da zuwan nasu, bayan gidan Aysha gidan Kamalu aka nufa nan ma dai sun nuna farincikin zuwan nasu hannu bibbiyu Farha ta kar6e su Babynsu har ta girma tubarkallah, gaba ɗaya ko ina roƙonsu ake kan su kwana ƙarshe saidai rabawa sukai Haulat da Husnah suka koma gidan Mino Tk da Amadu kuma gidan Kamalu zasu kwana Gwaggo kuma gidan Aysha sai dare su Fatuu suka koma gida,

Washe gari gaba ɗaya suka koma gidansu Fatuu a yadda suka shirya tare da ita zasu tafi Zaria su kwana washe gari Monday da safe sai su wuce Gwaggo dai anan zata tsaya sai ta kwana biyu,

Kwance tashi cikin Mino ya shiga wata na tara lokacin watan su Fatuu ɗaya da komawa sabon gida kuma Fatun na gida don sun samu hutu, tun ranar litinin ta fara yin naƙuda tsaitsaye zuwa washegari talata ciwo ya kankama amman koda aka kaita asibiti sai aka ce da saura su dawo gida taita yin exercise, kan kace mi duk ta fita hayyacinta dama abu ga sabon shiga tuni ido ya raina fata sai murƙususun azaba take har zuwa Fatuu tay ta dubata itama taga da saura ɗin haka tay ta ƙarfafa mata gwuiwa har tana ce mata kodai dama bata yin exercise da cikin ya tsufa cikin ciwo tace wllh tana yi, sai dare Fatuu ta koma gida Nameer ya dasa yin jinyar, wuraren ƙarfe sha biyu ba arziƙi ya kwasheta suka koma asibitin, wannan karon an kwantar da ita a vip wato ɗaki na musamman ita kaɗai ce aciki duk da haka an faɗi ma Nameer cewa da sauran lokaci, koda Fatuu ta kira taji ya jikinta Nameer ne ya sanar mata sun dawo asibiti an kwantar da ita amman ance still da saura tana jin haka tace gata nan zuwa, bayan zuwanta Asibitin Auntynsu Nameer ma tazo, shiru shiru ba haihuwa gashi ga dukkan alamu tana cikin azaba wasa wasa sai gashi har asuba bata haihu ba lokacin ta gama jigata ƙarfinta ya ƙare, gari na wayewa Aunty ta bada umarnin ayi mata Cs, sosae hankalin Nameer ya tashi jin zancen aikin amman ba yadda ya iya haka ya saka hannu, Wuraren ƙarfe tara na safe aka shiga da ita ɗakin tiyatar lokacin duk yan uwa sun zo harda Mom, Aysha ma tazo sai kuka take ana ce mata tayi mata Addu'a, ita kanta Fatuu hankalinta a tashe yake ƙarfin hali kawai take tana ta yi mata Addu'oi, bayan kamar minti ashirin da shiga da ita sai ga likitan ya fito yana ta murmushi ya sanar dasu tama haihu da kanta ba'a riga anyi aikin ba, zo kaga murna Aysha har da tsalle sai ga mai kuka ta koma yin dariya Fatuu da Nameer harda sujjadar godiya ga Allah sukai, lokacin da aka fito da Babyn wanda namiji ne baka jin komai daga bakunansu sai tubarkallah ma sha Allah Babyn kyakkyawan gaske gashi ƙato, daga baya itama Mino aka fito da ita saman gado baiwar Allah har an saka mata rigar aiki, bayan an canza mata ɗaki duk aka shiga ana mata ya jiki da barka, su Mino an ɗanɗana tun a asibitin ta rinƙa faɗin ta gama haihuwa aikuwa mi Fatuu zatayi in ba dariya ba tace wasa take ai yanzu ma ta fara sai gata harda kukanta sha6e sha6e tana ta rantsuwar ita Allah ta gama, da yamma aka sallameta ganin lafiyarta lau suka koma gidanta aka cigaba da zaman jego har ranar suna tazo yaro yaci sunan mahaifinsu Fatuu wato Muhammad aikuwa ba ƙaramin farinciki su Fatuu sukai ba, bayan suna da kwana ukku ta koma Yola acan zatayi wanka kamar yadda ta buƙata a wurin Nameer.
Chapter 205 · 0% Book details