Sashe 156
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
dariya Kamalu yay ya tambayi baturiya ce Tk yace Babanta ne bature yace ashe shiyasa yaga idanunta wani iri daga haka suka tafi, Bayan Fatuu ta koma ciki part ɗin data zauna lokacin data haifi twins ta nufa dama acan ta sauka Mino ma da Aysha da Safnah duk suna tare, a parlor ta iske Fauzy zaune dasu Safnah harda Mino ta miƙa mata hannu tace ta taso su shiga ciki, bayan sun shiga cikin Bedroom ɗin a saman gado suka zauna Fatuu na murmushi tace "Amaryar Ya Sameer bamu samu mun zauna ba inata son in tambaye ki ya amarci" ɗan ta6e baki tay tana murmushi tace ai yanzu amarci ya wuce Fatun tace duka wata ukkunne zata ce amarci ya wuce tace Uhmm kawai, hira suka cigaba da yi harda ta makaranta suna cikin yi Fauzy ta kai hannu ta ɗaukko jakarta dake a saman bedside data aje tun ɗazu ta buɗe, wata yar farar roba mai kyau ta fiddo tare da farin hanky ta maida jakar bayan ta daidaita zamanta ta latsa saman robar ya buɗe Fatuu nata kallonta a zaton ta wani abun ci zata fiddo kawai sai gani tay ta kai bakinta saitin inda ya buɗe ta zubda miyau kafin ta saki marfin ya rufe tasa hanky ɗin tana goge gefen bakinta, sakin baki Fatuu tay tana kallonta da alamun mamaki, kallonta Fauzy tay suna haɗa ido tayi murmushi tace mata ya akai ne, hannu Fatuu ta kai ta kama ha6a tace "Ke wai tsaya mi hakan da kikai ke nufi, ni nayi zaton ko Sweet ce zaki fiddo sai inga kin zubda miyau!" Dariya Fauzy tayi tace tun ɗazun yake damunta tana ta daurewa ta haɗiye saboda mutane, waro ido Fatuu tay ta buɗe baki da tsananin mamaki tace "Wai kaddai ciki gare ki Fauzy?" tana murmushi ta ɗaga mata kai alamar eh, hannu Fatuu tasa ta rufe baki sai kuma ta cire cikin washe baki tace "Ashe shiyasa naga kin ƙara haske sosae saidai kuma baki yi ƙiba ba sai ma ɗan ramewa da kikai ni na ɗauka duk amarcin ne yasa haka wllh" girgiza mata kai tay tace wahala ce don laulayi take sosae tayi mamakin ma yadda da tazo bikin ya rage sosae har abinci take ci acan ai ko abincin bata iya ci ga yawan amai har magani aka bata wanda zai sa ta daina aman in tana sha kullum to in ta sha sai ya rinƙa damunta in bata yi aman ba sai kawai wani lokacin ta ƙi sha, tambayarta Fatuu tayi watan cikin tace mata ɗaya da rabi,
"Kenan ma kice da kuka je Honeymoon kika same shi" kai ta ɗaga mata tace saida yay sati ukku sannan suka san dashi ko Aunty Mareeya bata sani ba sai yanzu tana ganinta ta gane Fatun tace "Ni kinga wllh ban gane ba saboda banyi tunanin Ya Sameer ɗin zai bari ki samu ciki da wuri ba daga yanayin shi",
"Aikuwa yay farinciki dana samu ni kaina saida nayi mamaki don ko Maganar haihuwa bai yi man nayi zaton bazai so cikin ba sai gashi baki ga yadda yake nan nan da ni ba, dafa wai ma bazai zo bikin nan dani ba Aikuwa nayi ta mashi kuka yace shi tsoron shi kada wani abu ya samu cikin nace mashi ai kema da cikin kika taho bikin ko shine yace to zai taho dani da yake kuma gaskiya bai son yaga damuwata yanzu kinga ya rude",
yar shewar dariya Fatuu tay tace "kice dai kin damƙe ya Sameer a hannu aikin Aunty Mareeya yayi kyau",
tana yar dariya tace "Aikin Aunty Mareeya ko aikin jawo ma mutum wahala ke wllh saida ta kai ina tsoron shi dana ji sallamarshi sai gabana ya faɗi har Aunty Mareeya na ta6a kira nayi mata complain taita ƙarfafa man gwuiwa daga baya dole na saba tunda naga yana son hakan sosae" Fatuu na dariya tace "kice dai Ya Sameer ya Magantu yadda Aunty Mareeya ke so" Dariya Fauzy ta saka tace wllh ita farko ma yay ta bata mamaki sai kace ba shi ba Fatuu dake ta dariya tace haka suke fa miskilan nan dama Aunty Mareeya ta faɗa ta haka ake jin bakin su,
"Amman dai ba wata matsala da kike fuskanta a wurinshi ko" Fatuu ta tambaya bayan sun gama yin dariyar, girgiza mata kai Fauzy tay tace "Wllh baida wata matsala gaba ɗaya yadda nayi tunanin shi ba haka ba, sosae yake sake man yana bani kulawa dana nuna inason abu sai yayi man in kuma na nuna banso shikenan, kamar farko kinga mata na kiranshi har ya amsa wayar a gabana tunda na nuna 6acin raina shikenan ya daina lokacin harda bani haƙuri don fushi nayi dashi duk ya ruɗe tun daga lokacin bai hana ni ɗaukar wayar shi da kaina nabi na goge duk lambar wata mace da saƙonni kuma bai ce man komai ba, ko tari nayi sai ya tambaye ni lafiya haka in ina wani abun yana taya ni duk da ba wani aiki ma nike ba da nace ya sallami mai mashi girki in rinƙa yi to yanzu saboda cikin nan ma yace ba za'a sallame shi ba harda mace ma ya ƙaro man da take man aikin gida",
tunda ta fara magana Fatuu keta faman sakin murmushin farinciki har ta gama tace amman taji daɗin labarin nan sosae wllh wani hanin ga Allah baiwa ne da bawa yayi haƙuri sai yaga ya kai matakin da bai ta6a zato ba,
"Kenan ma kice da kuka je Honeymoon kika same shi" kai ta ɗaga mata tace saida yay sati ukku sannan suka san dashi ko Aunty Mareeya bata sani ba sai yanzu tana ganinta ta gane Fatun tace "Ni kinga wllh ban gane ba saboda banyi tunanin Ya Sameer ɗin zai bari ki samu ciki da wuri ba daga yanayin shi",
"Aikuwa yay farinciki dana samu ni kaina saida nayi mamaki don ko Maganar haihuwa bai yi man nayi zaton bazai so cikin ba sai gashi baki ga yadda yake nan nan da ni ba, dafa wai ma bazai zo bikin nan dani ba Aikuwa nayi ta mashi kuka yace shi tsoron shi kada wani abu ya samu cikin nace mashi ai kema da cikin kika taho bikin ko shine yace to zai taho dani da yake kuma gaskiya bai son yaga damuwata yanzu kinga ya rude",
yar shewar dariya Fatuu tay tace "kice dai kin damƙe ya Sameer a hannu aikin Aunty Mareeya yayi kyau",
tana yar dariya tace "Aikin Aunty Mareeya ko aikin jawo ma mutum wahala ke wllh saida ta kai ina tsoron shi dana ji sallamarshi sai gabana ya faɗi har Aunty Mareeya na ta6a kira nayi mata complain taita ƙarfafa man gwuiwa daga baya dole na saba tunda naga yana son hakan sosae" Fatuu na dariya tace "kice dai Ya Sameer ya Magantu yadda Aunty Mareeya ke so" Dariya Fauzy ta saka tace wllh ita farko ma yay ta bata mamaki sai kace ba shi ba Fatuu dake ta dariya tace haka suke fa miskilan nan dama Aunty Mareeya ta faɗa ta haka ake jin bakin su,
"Amman dai ba wata matsala da kike fuskanta a wurinshi ko" Fatuu ta tambaya bayan sun gama yin dariyar, girgiza mata kai Fauzy tay tace "Wllh baida wata matsala gaba ɗaya yadda nayi tunanin shi ba haka ba, sosae yake sake man yana bani kulawa dana nuna inason abu sai yayi man in kuma na nuna banso shikenan, kamar farko kinga mata na kiranshi har ya amsa wayar a gabana tunda na nuna 6acin raina shikenan ya daina lokacin harda bani haƙuri don fushi nayi dashi duk ya ruɗe tun daga lokacin bai hana ni ɗaukar wayar shi da kaina nabi na goge duk lambar wata mace da saƙonni kuma bai ce man komai ba, ko tari nayi sai ya tambaye ni lafiya haka in ina wani abun yana taya ni duk da ba wani aiki ma nike ba da nace ya sallami mai mashi girki in rinƙa yi to yanzu saboda cikin nan ma yace ba za'a sallame shi ba harda mace ma ya ƙaro man da take man aikin gida",
tunda ta fara magana Fatuu keta faman sakin murmushin farinciki har ta gama tace amman taji daɗin labarin nan sosae wllh wani hanin ga Allah baiwa ne da bawa yayi haƙuri sai yaga ya kai matakin da bai ta6a zato ba,