Sashe 44
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washe gari bayan sun tashi sallar Asuba kowa ya ganta sai ya tambayi ina taje ne jiya ba'a kwanta da ita ba cikin kama kai take basu amsa da sun fita ne bayan sun dawo kuma ta tsaya d'akin Jidderh fira, bayan ta gama sallar ta d'auki wayar Fatuu don ta kai mata, lokacin data je d'akin su Jidderh ma basu dad'e da gama sallar ba sun koma gado bayan sun gaisa ta tambaye ta Fatuu nan ta sanar mata ba a gidan ta kwana ba, bayan ta fito zata koma part d'in su a ranta ta shiga raya dama dalilin kiran da Ya Haisam ke ta mata kenan tay d'an murmushi, tana shiga cikin parlon suka had'e da Aunty Mareeya tana sanye da doguwar rigar bacci kanta sanye da hula har saida gaban ta ya fad'i, tana ganinta ta tsaya Fauzyn ta tunkareta tana k'ak'alallen murmushi, gaishe da ita tayi ta amsa tana mata wani kallo tace mata ina taje jiya, rasa amsar da zata bata tayi ta fara yan kame kame, tunanin ko tace mata tare suka fita da Zarah tay sai kuma ta tuna da har yanzu ita bata gidan k'ilan kuma Aunty Mareeyar tasan ba gidan zata kwana ba, hannu ta kai ta kama kunnanta tace "fad'i man ina kika je jiya har aka kwanta baki dawo ba, kuma na kira wayar ki baki d'aga ba k'arshe ma dana sake kira sai kika kashe" yamutsa fuska Fauzy tay alamar tana jin zafin kama kunnanta da tayi, hakanan taji bata son fad'i mata abunda ya faru don bata san ya zata d'auki zancen kai ta wani gida da Sameer yayi ba, k'ara murd'e kunnan tayi ta saki yar k'ara tace zata fad'i mata don Allah kar ta tsinka mata kunne, cikin yar in ina tace mata dama da wani abokin Ya Haisam ne suka fita, waro ido Aunty Mareeya tayi ta saki kunnan nata da alamun Mamaki tace "kuka fita ku ka je ina?" tana kikkafta ido tace gari suka fita ya zagaya da ita, hannu Aunty Mareeya ta hau tafawa da alamun d'an tashin hankali tace zaga gari shine har wurin sha biyu bata dawo ba don ma taji Zarah itama bata nan shiyasa hankalinta ya d'an kwanta tayi tunanin suna tare, abu Fauzy ta had'iya a ranta ta raya don ma bata san k'arfe nawa ta dawo ba, daga Maganar da Aunty Mareeya d'in tayi ta samu k'aryar da zata mata tace ai daga zaga garin wurin su Zarah d'in suka wuce, tambayar ta ina Zarah d'in taje tayi tace suna tare da Ya Haisam a wani gidan su, gaba d'aya tayi kalar rashin gaskiya don hakanan ta fad'i hakan bata san ina Fatun suka je ba, murmushi Aunty Mareeya tay tace "Uhm su Malam miskili kenan gaba d'aya yana neman takura ma Yarinyar Mutane" murmushi Fauzy tay cikin alamun kunya tace "to Aunty Mareeya ba duk ke ce ba" hannu ta kai zata kai mata bugu tana fad'in ita uban mi tayi Fauzy ta goce tana dariya, tambayar ta tay shi wanda suka fitan cewa yay yana son ta Fauzyn ta d'an girgiza kai tace a'a kawae dai sun fita ne, harara ta wurga mata tace ita kuma ga mara aji kawai sai ta bishi zararai zararai Fauzyn tay dariya,
"Amman gaskiya Fauziyya yakamata kiyi saurayi ko kema Kya zo kiyi aure don Allah Zarah bata burge ki ba" tana murmushi tace "ta burge ni sosae Aunty, kuma dama tun lokacin data tare naji nima ina son in yi auren to amman ni fa har yanzu banda saurayi...." A hasale Aunty Mareeya ta katse ta "ta gidan uban wa zaki saurayin bacin har yanzu kin kasa cire wanccan shashashan mayaudarin daga cikin Zuciyar ki" yanayin fuskar Fauzyn ne ya canza cikin karyayyar murya tace "Aunty dole fa Mujaheed ya tsaya man a rai ko ya ya ne, kar ki manta bansan soyayyar kowa ba sai tashi, tun bansan kai na ba nasan miye soyayya ya koya man son shi daga shi kuma ban k'ara son wani abu, tsawon lokaci muna tare" idanunta har sun ciko tab da k'walla, ta6e baki Aunty Mareeya tay tace "Shikenan kada Allah yasa ki cire shi daga ran naki kiyi ta zama kar ki yi aure har mahadi ya bayyana" tana gama Maganar ta juya zata tafi da sauri Fauzy ta k'ank'ameta ta baya ta saki kuka tana fad'in don Allah tayi hak'uri wllh a yanzu a shirye take da tayi Aure indai ta samu mai son ta tsakani da Allah kuma itama taji tana son shi, juyowa tay ta rungume ta ta kai hannu tana goge mata hawayen tana fad'in ya isa, bayan ta yi shiru tace "Yanzu shi wanda kuka fita d'in da gaske bai ce yana son ki ba?" Kai ta d'aga mata ta sake cewa "to in yace yana son ki zaki amince" shiru Fauzy tay a ranta ta shiga tunanin to waima ita waye zai ce yana son nata Sameer dai tasan ko fad'uwa zatai a gaban shi tana mashi magiyar ya so ta ba son ta zai ba balle har ayi Maganar aure shiyasa ma bata sa ma ranta wai taji ko tana son shi ba, ganin ta kafeta da ido yasa tayi d'an murmushi ta jinjina mata kai alamar eh, sakinta Aunty Mareeya tayi ta d'aga hannuwa ta fara fad'in,
"Ya Ubangiji ina rok'on ka da sunayen ka tsarkaka da suffofinka mad'aukaka, ga kanwata nan ka bata miji nagari wanda zai so ta Saboda kai, Ya Allah Idan wanda suka fita tare Alkhairi ne a tattare da ita kasa mashi son ta da k'aunar ta a zuciya ta yadda har Al'amarin zai kai su da Aure Alfarmar Annabin rahama SAW" a hankali Fauzy itama ta fad'i S.w.a ganin Aunty Mareeyar ta shafa itama ta shafa tana d'an murmushi ita tausayi ma Aunty Mareeyar ta bata wllh ganin ta shirga mata k'arya kuma ta yarda, a hankali tace mata ta gode da kaunarta da take tana dariya tace mata ai wannan dole ne ita dai fatanta ta cika masu burin su tace mata in sha Allah daga haka ta juya tana mata k'orafin Saboda ita bata koma bacci ba ta nufi hanyar Bedroom Fauzyn nata kallon ta har ta shige sannan ta sauke ajiyar zuciya ta juya.
Misalin k'arfe goma sha d'aya na safen Haisam da Fatuu zaune a saman Carpet cikin parlon gidan da suka je wanda d'aya ne daga cikin gidajen estate d'in Dad d'in shi su suke amfani da shi, gaba d'aya ta shige cikin jikin shi kamar wata yar mage breakfast suke yi wanda da kan shi ya had'a masu tana ta bacci saida ya gama ya tasheta jikinta sanye da rigar bacci kanta ba kallabi sai sumar ta dake a fake, bayan sun gama ta mik'e ta fara tattara kayan, d'aukar babban tray d'in tayi ta juya zata kai kitchen ya bi bayan ta da kallo Fuskar shi cike da annuri, shi kad'ai yasan yadda yake jin yarinyar a cikin ranshi kullum da kalar nishad'in da yake samu a wurin ta, dawowa tay idon shi akanta yana mata murmushi itama murmushin take sakar mashi, ware mata hannuwan shi yay ta tafi da sassarfa ta fad'a mashi ya maida hannuwan ya rungumeta sosae ta d'ago fuska tana kallon shi, kai fuskar shi yay ya had'e da tata yana d'an danna hancin ta da dogon hancin shi, dariya tay tace "kai Hubby in ka k'ara shigar man dashi fa dama kana ganin shi d'an bajajje" yar dariya yay ba tare da ya raba fuskar tasu ba yace mata shi haka ganin shi yake yafi na kowace mace a duniya kyau, d'an bud'a ido tay har zata fad'i wani abu sai kuma tay shiru, sun d'an d'auki lokaci a haka suna ta shan love sai zuba ma juna sweet nothings suke suna dariya, d'agota yay yace taje ta shirya su koma gida aikuwa ta tura mashi baki ya d'age gira ya tambayeta minene a shagwabe tace "ni dai Allah bazan koma ba, kawai yanzu kowa ya tashi ansan ba gidan na kwana ba sai a ganni tsugui tsugui na dawo hakan ma ai rashin kunya ne" gaba d'aya ya zuba ma bakinta ido har ta gama idanu a lumshe yace mata ai ba wani rashin kunya don tana tare da mijin ta kuma ai su ba yanzu ne sukai auren ba ko" shagwaba ta shiga yi mashi harda su mak'e kafad'a sai sakin k'ayataccen murmushi yake, tambayar ta yay yanzu ya take so ayi tace ita dae bazata koma ba sai dare yace ta manta yau akwai dinner ne tace to ai tasan bada wuri za'a tafi ba in akayi Magrib lokacin gari ya d'an yi duhu sai su koma, d'aga mata kai yayi alamar za'a yi hakan can kuma tace koma kawai ta shirya daga nan sai ya kira Aunty Laila yayi mata magana yace Ok.
Zuwa Azahar duk an san Fatuu bata gidan, sam Fanan bata wani ji hakan ya dame ta ba don itama shekanjiya da ta zo ba gidan ta kwana ba tana tare dashi a wani gidan nasu wanda tana tunanin can ya tafi da Fatuu. Ana gama sallar Magrib aka fara shirin dinner lokacin Aunty Laila ta d'auki kayan da Fatuu zata sa ta tafi can gidan da take a Motar ta, saida ta biya ta d'auki wadda zata mata Make up suka tafi tare, lokacin da suka je Fatun ita kad'ai ce a gidan Haisam ya fita tana sanye da doguwar rigar material d'in data sa jiya da zasu taho, ba tare da 6ata lokaci ba aka fara mata make up d'in don dama tayi wanka kafin su zo, a can gida ma tuni shirin yayi nisa su Jidderh da Fauzy da Mino harda Haulat Nameer ya d'auke su ya kai su wurin make up wanda daga can zasu wuce tsadaddiyar Event Center d'in da aka kama hall d'in da za'ayi dinner d'in, aikin Abinci da abubuwan sha wata k'awar Mom da Sana'ar tace aka ba kwangila,
"Amman gaskiya Fauziyya yakamata kiyi saurayi ko kema Kya zo kiyi aure don Allah Zarah bata burge ki ba" tana murmushi tace "ta burge ni sosae Aunty, kuma dama tun lokacin data tare naji nima ina son in yi auren to amman ni fa har yanzu banda saurayi...." A hasale Aunty Mareeya ta katse ta "ta gidan uban wa zaki saurayin bacin har yanzu kin kasa cire wanccan shashashan mayaudarin daga cikin Zuciyar ki" yanayin fuskar Fauzyn ne ya canza cikin karyayyar murya tace "Aunty dole fa Mujaheed ya tsaya man a rai ko ya ya ne, kar ki manta bansan soyayyar kowa ba sai tashi, tun bansan kai na ba nasan miye soyayya ya koya man son shi daga shi kuma ban k'ara son wani abu, tsawon lokaci muna tare" idanunta har sun ciko tab da k'walla, ta6e baki Aunty Mareeya tay tace "Shikenan kada Allah yasa ki cire shi daga ran naki kiyi ta zama kar ki yi aure har mahadi ya bayyana" tana gama Maganar ta juya zata tafi da sauri Fauzy ta k'ank'ameta ta baya ta saki kuka tana fad'in don Allah tayi hak'uri wllh a yanzu a shirye take da tayi Aure indai ta samu mai son ta tsakani da Allah kuma itama taji tana son shi, juyowa tay ta rungume ta ta kai hannu tana goge mata hawayen tana fad'in ya isa, bayan ta yi shiru tace "Yanzu shi wanda kuka fita d'in da gaske bai ce yana son ki ba?" Kai ta d'aga mata ta sake cewa "to in yace yana son ki zaki amince" shiru Fauzy tay a ranta ta shiga tunanin to waima ita waye zai ce yana son nata Sameer dai tasan ko fad'uwa zatai a gaban shi tana mashi magiyar ya so ta ba son ta zai ba balle har ayi Maganar aure shiyasa ma bata sa ma ranta wai taji ko tana son shi ba, ganin ta kafeta da ido yasa tayi d'an murmushi ta jinjina mata kai alamar eh, sakinta Aunty Mareeya tayi ta d'aga hannuwa ta fara fad'in,
"Ya Ubangiji ina rok'on ka da sunayen ka tsarkaka da suffofinka mad'aukaka, ga kanwata nan ka bata miji nagari wanda zai so ta Saboda kai, Ya Allah Idan wanda suka fita tare Alkhairi ne a tattare da ita kasa mashi son ta da k'aunar ta a zuciya ta yadda har Al'amarin zai kai su da Aure Alfarmar Annabin rahama SAW" a hankali Fauzy itama ta fad'i S.w.a ganin Aunty Mareeyar ta shafa itama ta shafa tana d'an murmushi ita tausayi ma Aunty Mareeyar ta bata wllh ganin ta shirga mata k'arya kuma ta yarda, a hankali tace mata ta gode da kaunarta da take tana dariya tace mata ai wannan dole ne ita dai fatanta ta cika masu burin su tace mata in sha Allah daga haka ta juya tana mata k'orafin Saboda ita bata koma bacci ba ta nufi hanyar Bedroom Fauzyn nata kallon ta har ta shige sannan ta sauke ajiyar zuciya ta juya.
Misalin k'arfe goma sha d'aya na safen Haisam da Fatuu zaune a saman Carpet cikin parlon gidan da suka je wanda d'aya ne daga cikin gidajen estate d'in Dad d'in shi su suke amfani da shi, gaba d'aya ta shige cikin jikin shi kamar wata yar mage breakfast suke yi wanda da kan shi ya had'a masu tana ta bacci saida ya gama ya tasheta jikinta sanye da rigar bacci kanta ba kallabi sai sumar ta dake a fake, bayan sun gama ta mik'e ta fara tattara kayan, d'aukar babban tray d'in tayi ta juya zata kai kitchen ya bi bayan ta da kallo Fuskar shi cike da annuri, shi kad'ai yasan yadda yake jin yarinyar a cikin ranshi kullum da kalar nishad'in da yake samu a wurin ta, dawowa tay idon shi akanta yana mata murmushi itama murmushin take sakar mashi, ware mata hannuwan shi yay ta tafi da sassarfa ta fad'a mashi ya maida hannuwan ya rungumeta sosae ta d'ago fuska tana kallon shi, kai fuskar shi yay ya had'e da tata yana d'an danna hancin ta da dogon hancin shi, dariya tay tace "kai Hubby in ka k'ara shigar man dashi fa dama kana ganin shi d'an bajajje" yar dariya yay ba tare da ya raba fuskar tasu ba yace mata shi haka ganin shi yake yafi na kowace mace a duniya kyau, d'an bud'a ido tay har zata fad'i wani abu sai kuma tay shiru, sun d'an d'auki lokaci a haka suna ta shan love sai zuba ma juna sweet nothings suke suna dariya, d'agota yay yace taje ta shirya su koma gida aikuwa ta tura mashi baki ya d'age gira ya tambayeta minene a shagwabe tace "ni dai Allah bazan koma ba, kawai yanzu kowa ya tashi ansan ba gidan na kwana ba sai a ganni tsugui tsugui na dawo hakan ma ai rashin kunya ne" gaba d'aya ya zuba ma bakinta ido har ta gama idanu a lumshe yace mata ai ba wani rashin kunya don tana tare da mijin ta kuma ai su ba yanzu ne sukai auren ba ko" shagwaba ta shiga yi mashi harda su mak'e kafad'a sai sakin k'ayataccen murmushi yake, tambayar ta yay yanzu ya take so ayi tace ita dae bazata koma ba sai dare yace ta manta yau akwai dinner ne tace to ai tasan bada wuri za'a tafi ba in akayi Magrib lokacin gari ya d'an yi duhu sai su koma, d'aga mata kai yayi alamar za'a yi hakan can kuma tace koma kawai ta shirya daga nan sai ya kira Aunty Laila yayi mata magana yace Ok.
Zuwa Azahar duk an san Fatuu bata gidan, sam Fanan bata wani ji hakan ya dame ta ba don itama shekanjiya da ta zo ba gidan ta kwana ba tana tare dashi a wani gidan nasu wanda tana tunanin can ya tafi da Fatuu. Ana gama sallar Magrib aka fara shirin dinner lokacin Aunty Laila ta d'auki kayan da Fatuu zata sa ta tafi can gidan da take a Motar ta, saida ta biya ta d'auki wadda zata mata Make up suka tafi tare, lokacin da suka je Fatun ita kad'ai ce a gidan Haisam ya fita tana sanye da doguwar rigar material d'in data sa jiya da zasu taho, ba tare da 6ata lokaci ba aka fara mata make up d'in don dama tayi wanka kafin su zo, a can gida ma tuni shirin yayi nisa su Jidderh da Fauzy da Mino harda Haulat Nameer ya d'auke su ya kai su wurin make up wanda daga can zasu wuce tsadaddiyar Event Center d'in da aka kama hall d'in da za'ayi dinner d'in, aikin Abinci da abubuwan sha wata k'awar Mom da Sana'ar tace aka ba kwangila,