← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 174 OF 211

Sashe 174

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Bayan wata guda aka fara aikin gidan nasu gadan gadan lokacin har Baban su Umar ya samu gida an siya mashi sun tashi Tk ma an saka ranar aurenshi daidai dana Amadu wato rana ɗaya za'a ɗaura masu aure, 6angare guda aka ware masu suke zaune kafin aikin yazo inda suke. Cikin sa'a Kamalu ya rubuta Jamb ya samu point da ake buƙata don yin karatu a Jami'ar daya cike wato Umaru Musa Yar'adua University Katsina (Umyuk), bayan sun yi post Utme cikin sa'a ya samu Admission don fara karatu inda zai yi Degree akan Computer Science, a lokacin sosae suke waya da Farha sun shaƙu da juna ta kai har kuɗi ta turo mashi don ya canza waya saboda in suna yin Vedio call wani lokacin wayar shi na basu matsala, lokacin daya yi ma kawu Amadu magana kan ya rakashi su sayi wayar jin itace ta turo mashi kuɗin saida ya tambayeshi mike tsakaninsu wai dama yana lura da yawan wayar da suke, Kamalun bai 6oye mashi yadda sukai da ita ba na cewa da tayi tana son su zamo abokai, sosae kawu Amadu yayi mamakin jin hakan, bayan an siyo wayar ne suka je nuna ma Gwaggo itama dai tayi mamakin jin Farha ce ta turo mashi kuɗi ya siya saida ta tambayi yadda akai suka san juna ya faɗi mata, sam Gwaggo bata kawo komai ba a ranta tayi tunanin jinin su ne ya haɗu tayi mashi Allah ya sanya Alkhairi, lokacin daya fara karatu ita kuma ta gama Degree ɗinta a Jami'ar Lagos ta nemi da a turo ta Katsina bautar ƙasa da yake suna da hanya sai gashi an turo ta Katsinar har saida Hajiya tayi mamaki lokacin da Hajiya Maryam ta sanar da ita zancen zuwan Farhar wurinta ta zauna don yin service kuma ita ta za6i hakan, lokacin da za ta zo harda uban sababbin kayan sawa da takalma da jakuna irin wanda samari ke amfani dasu a Makaranta ta kawo ma Kamalu, ranar data zo ta kama Friday da rana tunda Tk ya ɗaukkota daga Airport tasha gayun ƙananun kaya ta tambayeshi Kamal yace bai san ko yana nan ba amman bari in sunje bakin shagonsu sai su duba, lokacin da suka iso Kawu Amadu ne kawai a ciki Tk ya tambayeshi Kamalu yace bai nan yana School Farhar harda gaishe da kawu Amadun ba laifi ya ɗan saki fuska ya amsa mata tare da yi mata sannu da zuwa, bayan ta amsa ne ta tambayi kaman zuwa ƙarfe nawa zai dawo yace mata sai anyi La'asar daga haka suka wuce, suna zuwa parlon Hajiya lokacin tana zaune Farhar ta nufeta da gudu taje ta rungumeta Hajiya ta nuna farincikin zuwan ta sosae Tk ya tambayi ina zai kai kayanta Hajiya tace ya kai su Visitor room, bayan sun gama gaisawa Hajiya tayi mata Maganar abinci tace mata bata jin yunwa sai anjima tace to taje ta huta ko, koda taje ɗakin wanda tuni an gyara mata shi ta kwanta a gado kasa yin baccin tayi don ba wanda take son gani irin Kamal ƙarshe sai ta ɗauki wayarta ta shiga lallatsawa, tana haka akayi la'asar ta miƙe ta nufi toilet tayo wanka, shiryawa tayi da atampa mai kyau anyi mata straight gown ta kamata sosae tayi ɗaurin kallabin Zarah Buhari a wurin Fanan taga tana yawan yin shi kuma yana mata kyau shine itama take yi kuma yana mata kyau sosae harda yar kwalliya tayi duk da ita bata cika son yin kwalliya a fuskarta ba kamar Fanan, tana cikin shiryawa Hajiya ta shigo cikin ɗakin da sallama ta juyo tana kallonta da murmushi Hajiyar tace "au ni nayi zaton ma kina nan kinata bacci naga anyi La'asar gashi baki ci komai ba nace bari in zo in tashe ki ashe ke kina nan kina ta rangaɗa kwalliya", still murmushin take yi bata ce komai ba,

"To wannan kwalliyar ta mecece daga zuwa kodai angon nawa anan yake shine zai zo yin sannu da zuwa?" dariya Farhar tayi tace mata No kawai tayi ne kuma tana son ta fita jikinta ya ɗan saki Hajiyar tace to ita ina ta sani da zata je, ɗan jimm tay kafin tace ko gidan su Zarah sai ta gaishe da Granny ɗinta, sosae Hajiya taji daɗin jin hakan don ya tabbatar mata da Farhar ta canza da gaske tace mata to tazo ta fara cin abinci kafin ta tafi suka nufi ƙopar fita harda kama Hajiyar tace wai bari ta taimaka mata taga bata yin tafiyar sosae Hajiya na dariya tace da wannan sandar tata sai tayi tafiyar da ita bata iya yi, lokacin da suka fito daga cikin corridor Saude na niyyar shiga Kitchen ganin su yasa ta dakata tana murmushi tana niyyar gaishe da Farha sai ji tayi ta rigata gaishe da ita Sauden ta amsa tare da yi mata anzo lafiya da tambayar yan'uwanta da Momynsu duk tace mata suna lafiya Hajiya ta tambayi Farhar a dining zata ci abincin tace a'a a kawo mata a parlor yadda tana ci suna hira Saude ta juya da sauri tana faɗin to bari ta kawo mata can suma suka nufo cikin parlon, a saman c-table aka shirya mata kayan abincin bayan tayi serving nata tace mata aci lafiya Farhar na ɗan murmushi tayi mata godiya, lokacin da Saude ta nufi hanyar Kitchen sosae take mamakin canzawar Farhar a ranta, ba wani sosae taci ba tace ta ƙoshi Hajiya dake yin kallo ta kalleta tace dama wannan ɗamammiyar rigar ai bazata bari taci wani abinci sosae ba basu son suna ɗinka wadatattun kaya suyi ta faman takura kai, murmushi kawai Farhar tayi itama ta maida idonta kan Tv tana kallon abunda Hajiya ke kallo can bayan wani ɗan lokaci ta miƙe ta nufi hanyar bedroom, bada daɗewa ba ta fito tana ruƙe da ƙatuwar leda mai tambarin Shopping Mall ɗin Mamanta, cikin parlon ta dawo daga bakin kujeru ta tsaya tace ma Hajiya zata je ta dawo ta ɗaga mata kai har zata juya tace mata to ina mayafi kuma ta kalleta tana ɗan yamutsa fuska tace takura mata yake gashi sai yayi ta faɗuwa saboda bata saba sakawa ba Hajiya tace mata amman bai kyautu kuma ai ta fita haka ba tana yar musulma kuma ma ba kyau fita hakan ai ta sani tunda tana zuwa islamiyya su kan su waɗannan kayan bai kamata tana saka su ba ta fita indai ba lullu6e jikinta zatayi ba komi mutum zai yi ya rinƙa tuna lahirar shi, ɗan murmushi tayi tace Ok zata gyara ta aje ledar ta juya don ta ɗaukko mayafi Hajiya ta bita da kallo tana murmushi sosae take jin daɗin yadda ta canza don inda da ne tayi mata Maganar shigar da tayi yamutsa fuska zatayi kuma bazata canza ba, gyale ta yafo daya shiga da atamfar saman kafaɗa duk da baida wani girma yadda ta yafan ya rufe mata bayanta bayan ta ɗauki ledar tayi ma Hajiya sai ta dawo, ko a bakin gate saida su Officer sukai Maganar canzawarta bayan ta gaishe su ta wuce, tana zuwa saitin shagon kallo ɗaya tayi ma na ciki ta gane Kamalun ne duk da ya juya baya yana sanye da riga da wando na light blue shadda, tsayawa tayi tana murmushi cikin zazzaƙar muryata tace a bata Sweet yace wane iri saida ta wurga idonta saitin ledojin Sweet ɗin taga wani ansa mango da sauri tace mashi shi yace Ok guda nawa tana yar dariya tace pack guda, ɗaukko jakar Sweet ɗin yayi yana juyowa idanunshi suka shiga cikin nata har saida yay alamun tsorata Farhar ta saka dariya, da tsananin mamaki yace da gaske itace tana murmushi ta ɗaga mashi gira tare da furta yes,

"Amman yaushe kika zo?" still da mamaki ya tambaya tace mashi ɗazun ai tazo nan ta tambaye shi Uncle nashi yace bai dawo ba bai faɗi mashi bane yace mata lokacin daya dawo daga School ɗin shi kuma ya tafi kasuwa to basu haɗu ba shiyasa bai san data zo ba,

"Amman ko fa yau da safe munyi waya baki faɗi man yau zaki zo ba" ɗan farfar tayi da ido tace "i want to give you a surprise" yana murmushi yace aikuwa gashi ta bashi shi har tsoro ma yaji daya ganta tana yar dariya tace ai ta gani, shiru sukai ta shiga jefa mashi wani kallo shi kuma yana ɗan murmushi can tace "Ka ƙara kyau" yar dariya yay duk dimples ɗinshi suka lotsa yace "ina wani kyau kullum ina zaryar School rana yana buguna" tace duk da haka ita taga ya ƙara kyau kodai saboda ya fara zuwa University yana haɗuwa da yan'mata shiyasa yake gyara masu kanshi, tayi Maganar tana mashi wani kallo yay yar dariya yace shida bai daɗe da fara zuwa ba kuma shi karatunshi ya saka a gaba ba ruwan shi da wasu yan'mata ta ɗan yamutsa fuska tace Allah yasa gaskiya yake faɗa mata, rantse mata yay kan shi ba ruwan shi da wasu yan'mata ta ɗan yi murmushi ta furta Better gara ya maida hankali yayi karatu ya bar duk wani shiriritar yin yan'mata ya furta mata in sha Allah,
Chapter 174 · 0% Book details