← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 200 OF 211

Sashe 200

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Washe gari bayan Haisam ya dawo daga sallar Asuba itama Fatun tayi sun koma sun kwanta ta tada kanta a saman jikinshi yake mata zancen son auren Aysha da Na'eem keyi ya faɗi mata yace mashi ya nemi amincewarta to har sunyi magana kuma ta amince, sosae Fatuu ta jinjina abun don ita koda ta gansu tare bata kawo komai a ranta ba saboda tasan Ayshar nada saurin sakin jiki da mutane ba kamar Mino ba, da alamun damuwa tace mashi amman bai ganin hakan zai iya haifar da matsala tsakaninsu da matar shi taga anyi mata ba daidai ba tunda sun san juna suna gaisawa, yana ɗan murmushi yace itama ba sun san juna ba da Fanan kuma ta aureshi, juyawa tay tayi mashi wani kallo tare da ɗan tura mashi baki tace to ai ita bata san da Auren ba ko ya ɗage mata gira yace data sani bazata amince ba kenan tay shiru tana kallon shi yace ta bashi amsa, yamutsa fuska tay ta sigar shagwa6a tace to tunda dai an riga anyi ya wuce miye na maido maganar, yana murmushi yace Ok tunda itama ya aureta kuma sun san juna da Fanan itama Ayshar ba wani abu bane don ta auri Na'eem, shiru Fatuu ta ɗan yi kafin tace ya sani fa Aunty Fanan daban take a cikin mata don da wuya a samu wadda zata iya jarumtar da tayi, shiru yay yana sakin murmushi yayin da zuciyarshi ta shiga dawo mashi da fuskar Fanan. Wuraren ƙarfe goma na safe suka zauna yin breakfast, kowa cikinsu yayi wanka Haisam da Na'eem na sanye da ƙananun kaya wando da riga Fatuu kuma da Aysha suna sanye da dogayen riguna masu taushi suna da gajerun hannuwa kowa ya saka hula a kanshi daga bayan hular yay tudu sosae saboda gashin su, bayan sun zauna a kujerun dining ɗin suka shiga gaishe da juna kafin Fatuu ta shiga yin serving nasu, bayan ta gama a nutse suka fara ci baka jin komai sai ƙarar cokulla sai kuma Ac dake a wurin tana ta aiki, bayan sun gama gaba ɗaya a falo suka zazzauna suna yin hira wadda Haisam da Na'eem sai Fatuu ne ke yi ita dai Aysha tayi shiru tana saurararsu akai akai kuma suke haɗa ido da Na'eem su sakar ma juna murmushi, suna cikin yin firar Na'eem yace ma Fatuu "Madam ko in ce Yayata, ina fatan Yalla6ai ya isar maki da saƙona na naga ƙanwarmu tayi man ina neman iri pls, yace man in nemi amincewarta da yake mu indai ta wannan bangaren ne bamu failing tuni har an amince man ance ana sona" ya kai idon shi kan Aysha yace "Ayshanah hakane ko, kin amince zaki aure ni ai ko?" ai tana jin abunda ya faɗa tay zumbur ta miƙe da gudu ta nufi hanyar bedroom duk suka bita da ido suna yar dariya, bayan barinta wurin ne Fatuu tace mashi sunyi Maganar da Hubby taji daɗi saidai tana gudun hakan ya haifar da matsala tsakaninsu da Fadeela tana iya ganin an yi mata ba daidai ba, yana murmushi yace mata kar ta damu zai faɗi mata shi yaga Aysha yaji yana sonta kuma akai sa'a itama tana son shi ba wanda ya haɗa su in sha Allah ba wata matsala da zata faru tsakaninsu Fatun tace Allah yasa, tambayar ta yay lokacin da zata gama School Fatun ta faɗi mashi yace Ok nan da sati ɗaya in sha Allah zaije Yola ya gaida Parents ɗin su Haisam yay mashi wani kallo kafin slowly yace mashi saurin mi yake ne tunda ta amince mashi yabi komai a hankali da sauri Na'eem ɗin yace ai ba mata irinsu ake bi a hankali ba wurin neman aurensu nan tana gama Secondary zaiga masu son ta suna ta kunno kai ƙarshe asamu wani yayi mashi overtaking shiyasa yake son tana gama School ɗin yayi wuff da ita duk sukai yar dariya, hira suka cigaba da yi bayan wani lokaci Haisam ya tambaye shi yaushe zai je gaida relatives ɗin nashi Na'eem ɗin ya duba agogon hannunshi kafin ya bashi amsa da zuwa ƙarfe sha biyu zai tafi Haisam yace Ok in lokacin ya ƙarasa sai suje ya raka shi,

"No, kai zaman ka kaida kazo Weekend Madam na buƙatar ka a kusa da ita koda yaushe ka ƙyale ni in je ni kaɗai, ko kuma tunda nima ga Amaryata sai ta rakani kawai kaga ma sai inyi amfani da daman in fara introducing nata ga Family na" Na'eem ya faɗa yana murmushi suma duk murmushin sukai basu ce komai ba, ganin lokacin fitar nashi ya ƙarato yasashi ce ma Fatuu pls yana neman alfarmar fita da Aysha tana murmushi tace an mashi yay mata godiya kafin yace to ta taimaka tayi ma Amaryar tashi mai kunya magana ta shirya tace to tana dariya tare da miƙewa shima Na'eem ɗin ya miƙe yace ma Haisam bari ya shirya ya ɗaga mashi kai, a bedroom ta iske Aysha kwance saman gado ta nufeta tana faɗin kwanciya tayi kenan Ayshar ta ɗago tana kallonta, a bakin gadon ta zauna tana kallonta da murmushi tace mata Amaryar Na'eem Ayshar tayi murmushi kawai, shiru Fatun ta ɗan yi kafin tace mata ta tabbatar da yayi mata tana son shi don shi da gaske yake aurenta zaiyi tana gama School, shiru Ayshar tayi tana kifce kifcen idanu Fatuu tace mata ta buɗe baki tayi mata magana, a hankali tace mata eh in dai baida wata matsala Fatun tace gaskiya Na'eem bata tunanin yanada wata matsala a yadda ita ta sanshi mutumin kirki ne kuma tasan da yanada matsala ma tun Farko Haisam bazai bashi damar ya nemi soyayyarta ba kawai inda take tunanin matsala wurin matarshi ne duk da itama tana da kirki to amman wata baka gane rashin kirkinta sai za'a mata kishiya kawai dai suyi addu'a Allah yasa ta fahimta ta kuma kar6i abun kamar yadda Aunty Fanan tayi Ayshar ta amsa da Amin kafin tace "amman fa Adda Fatuu wllh Aunty Fanan ta daban ce" murmushi Fatun tay tace ta sani samun irinta cikin mata da wuya in ma akwae duk da tasan akwai mata da yawa wanda in mijinsu yaje masu da zancen ƙara aure duk da basu so amman suna karbar abun a matsayin ƙaddararsu tunda sun san Allah ne ya halarta masu yin jayayya da hakan kuma wahalar da kai ne ƙarshe mutum ya jefa kan shi a halaka, faɗi ma Ayshar tayi zasu fita da Na'eem ɗin yana son zuwa da ita wurin danginshi ya gabatar masu da ita, tana jin haka ta ɗan zaro ido kafin tace amman da wuri haka, miƙewa Fatuu tay tana yar dariya tace shifa da gaske yake yace ma nan da sati ɗaya zaije Yola gaishe dasu Baffa don haka ta fara shiri don ita amarya ce,
Chapter 200 · 0% Book details