Sashe 116
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ya akai bakai bacci ba kai da kake gauro" Haisam ya fad'a yana murmushi Sameer d'in yay d'an guntun murmushin da iyakar shi lips d'in shi slowly yace mashi yana shan coffee ne Haisam d'in ya jinjina mashi kai suka d'an yi shiru kafin Sameer d'in ya tambayi ya Babies d'in su ya bashi amsa da suna lafiya, ce mashi yay yaga sak'on kud'i yanzu shiru Sameer din ya d'an yi kaman bazai ce mashi komai ba can yace mashi ya d'auki 1 million yaba wife en shi 500k yaran shi kuma a fad'i masu zai musu zuwa na musamman, murmushi Haisam yay yayi mashi godiya kafin ya tambayi bazai zo suna ba yace mashi yaso hakan amman aiki yayi mashi yawa amman yana nan zuwa bada dad'ewa ba Haisam yace Ok Allah ya taimaka ya amsa mashi da Amin, tambayar shi yay ina Amarya ya d'an ta6e baki ya bashi amsa da yanzu suka gama magana Haisam na murmushi yace abun nata matsowa Allah ya nuna masu can kasan mak'oshi Sameer ya amsa da Ameen suka dan k'ara yin shiru,
"Ina son zaka taimaka man da abu" Sameer ya fad'a Haisam ya jinjina kai tare da dan gyara zaman shi ya tambayi miye yace mashi dama yana son zai siya ma su bride d'in tashi gida ne, kai Haisam ya d'aga kafin ya tambayi to wane taimako yake son yayi mashi yace bai san taya zai yi hakan ba tunda shi ba sanin garin su yayi ba kuma bai san kowa ba so yana son ya bashi shawarar yadda za'ai Haisam yace ya yi Maganar da Fauzy ne ya girgiza mashi kai alamar a'a kafin yace yafi tunanin yin Maganar da wani babba ba ita ba, shiru Haisam yay alamar tunani can yace mashi ya bari zasu yi Maganar da Wife d'in shi sai ta kira Yayarta tayi mata Maganar Sameer d'in yace Ok zai jira shi ya fad'i mata in tayi ma Yayar tata Maganar tace mata su duba gidan da suke so mai kyau in za'a samu Haisam yace Ok, hira suka d'an k'ara yi yawanci duk akan bikin Sameer d'in ne daga baya sukayi sallama, suna gama yin wayar ya kira Fatuu lokacin suna zaune a Bedroom d'inta da su Aunty Laila anata shirya yadda za'ai suna, bayan tayi picking tambayar ta yay tana tare da mutane ne tace mashi eh yace Ok bari zai tura mata sak'o ta WhatsApp tace to, lokacin da ta karanta sak'on daya turo matan d'an waro ido tay alamar mamaki sai kuma ta hau yin d'an murmushi, sai wuraren k'arfe goma da rabi sannan duka aka watse daga hirar da ake a d'akin Jidderh ma da anan take kwana tace ma Fatun bari taje ta dawo, suna tafiya cike da zumud'i ta shiga kiran Aunty Mareeya, saida ta kusa yankewa sannan ta d'auka bayan sun gaisa ta tambayi twins Fatun tace mata k'ilan ma har tayi bacci ta tada ita ko tace mata a'a bata kusa da wayar ne, tambayarta ina Fauzy tay tace mata tana d'akin ta bata san ko tayi bacci ba ta tambayi ita zata ba wayar ne da sauri Fatun tace a'a dama sak'o ne aka bata da alamun d'an mamaki tace mata to waye ya bada sakon tace mata Sameer har saida Aunty ta maimaita sunan Sameer d'in kafin ta tambayi sak'on miye ya bada, bayanin da yayi Fatun tayi mata bayan ta gama da tsananin mamaki Aunty Mareeya ta maimaita abunda ta fad'a tace mata eh haka yace,
"Kinga Zarah wllh nama rasa mi zance maki tsabar Al'ajabi, yanzu duk uban hidiman da yake ma Fauziyya kuma harda wannan gingimemiyar dawainiyar Gida fa!" Dariya Fatuu tay jin yadda tayi Maganar tace " Wllh Aunty, yana da halin ne kuma k'ilan yana son canza gidanne Saboda bikin tunda kinga ba k'aramar hidima za'ai ba manyan mutane zasu zo" Aunty tace "hakane kam, dama muma munata shirin yin gyaran gidan don har an gama Magana ma da masu gyaran za'ai gyara sosae Saboda hakan yanzu kuma kinga ga Maganar da yayi ni bamma san to mi zan ce ba, amman abunda za'ai Zarah zan kira babban yayanmu sai muyi magana kan hakan tunda ma gobe zamu taho nan in muka zo komi mukai dashi zan fad'i maki sai ki fad'i ma Mijin naki" amsa mata da to Fatun tay tace Allah ya kawo su lafiya duk ta k'agara ta gan su wllh Auntyn na dariya tace suma bata ga yadda suka k'agara da su ganta ba amman sun fi k'agara da suka ga twins d'in su Fatun nata dariya Aunty Mareeyar ta k'ara cewa "ni kinsan abunda ma yafi damuna Zarah?" Kai Fatuu ta girgiza kafin tace mata a'a,
"Wllh abunda nike gudu kada sai mun zo munyi kayan d'aki suce basu so tunda kinsan Manyan nan yadda suke" kai Fatuu ta jinjina tace hakane kuma fa, Aunty tace wllh abunda take ta tunani kenan, shiru Fatun ta d'anyi kafin can tace mata to ko tayi ma Ya Haisam magana kan hakan da sauri Aunty tace "kice mashi mi Zarah! A'a kada kiyi mashi magana kan hakan kada kuma aga kamar so muke ace kada ayin, za'a yi mata komai iya karfin mu dama mun yanke za'a siya mata kayan ne kawai Babanmu ya yanke zai siyar da gonakin shi guda biyu sai a had'a da sauran kud'in da aka tanada in sha Allahu za'ai komai yadda yakamata" Fatuu tace Allah ya bada iko ta amsa da Amin,
"Ni kinsan ma abunda nafi so wllh shine in da zai yuwu da yaje Funtua sun gaisa dasu don duk fa ba wanda ya san shi in ba a hoto da aka nuna masu shi ba to kuma hakan nasan da kamar wuya tunda yanzu ma bai K'asar tun kafin ya tafi nayi ma Fauziyya Maganar kan tasa shi yazo sai ce man tayi wai ita gaskiya bata iyawa ni in yi mashi, to wai kar aga kai talaka ka zaqe yasa ban yin ba kuma ma dai nima nasan halin surukin nawa baud'add'e ne" Dariya Fatuu tasa Auntyn tace Allah kuwa yanzu dai ai sai kawai da biki sun gan shi, hira suka d'an k'ara yi kafin sukai sallama ta kira Haisam d'in tayi mashi bayanin abunda Aunty tace yace Ok Allah ya kaimu goben ya kawo su lafiya, cikin yar shagwaba ta tambayi yana ina yana murmushi yace mata gashi a part d'in shi tace mi yake ya bata amsa da yana wani aiki ne tay shiru yayin da zuciyarta ta shiga raya mata kilan ma a part d'in shi Fanan ke kwana jin tayi shiru yasa shi tambayar ta koda wani abu ne da sauri tace mashi a'a tayi mashi saida safe yana murmushi ya amsa har zata kashe taji yace tana tare da mutane ne a hankali tace mashi a'a ita kad'ai ce Jidderh taje ta dawo yace Ok bari yazo suyi bankwana da Babies tay d'an murmushi tace to, aje wayar tayi ta juya tana kallon yaran dake kwance saman gadon suna bacci sam basu da rigima da sun yi kuka yawanci yunwa suke ji, bada jimawa ba sai gashi ya shigo cikin d'akin da sallama ta d'aga kai ta kalle shi ya sakar mata murmushi itama haka, cikin d'akin ya nufo ya tsaya d'an nesa da ita yace bazatai welcoming nashi ba tunda shi bak'o ne yanzu, yar dariya tayi ta mik'e ta nufe shi tana zuwa gabanshi ta fad'a jikin shi ya rungumeta suna ta sakin murmushi ga k'amshin jikinsu ya cika ma kowa hanci, d'agowa tay tace mashi ya zauna atare suka zauna idon shi akan yaran ya tambayi ya suke itama kallon su take tace mashi lafiya lou, juyowa tay suka had'a ido ta d'an langa6ar da kai cikin lumshe ido Slowly ya furta mata "I'm missing you" dan buda ido tayi still da murmushi akan Fuskar ta k'asa k'asa tace "ba gani a kusa da kai ba" d'age gira yay yace ba shi ba itama ta d'age mashi tace wanne, wani irin kashe mata ido yay ta saki dariya shima yar dariyar yay ya jawota jikin shi, kai hannu tayi
tana shafa beard cikin salo tace "na gode ma Allah dayasa na haihu lafiya naci gaba da yin rayuwa da kai" lumshe mata ido yay a hankali yace shima haka tana niyyar k'ara yin magana suka ji an shigo a tare suka kai idon su kan kopar Jidderh ce tayi shirin bacci tana ganin su ta dan waro ido tana murmushi kunya ce ta kama Fatuu ta fara k'ok'arin raba jikinta da nashi saidai yak'i bata dama ganin haka yasa Jidderh cewa ta bashi 10 minutes zata je ta dawo harda jaddada mashi da hannu duk sukai yar dariya, bayan ta fita Fatuu ta maida idonta kan shi tace tana son yi mashi wata Magana ya d'aga kai kafin yace yana ji,
"Dama so nike in ce kaman yakamata Ya Sameer yaje Funtua su gaisa da iyayen Fauzy Saboda ba wanda yasan shi fa" shiru yay idon shi akanta can yace mata sun yi magana kan hakan ne da sauri tace a'a kawai itace tayi tunanin hakan, Wani kallo yay mata yace "Kai yar fillona yaushe kika iya yin wannan tunanin" dariya ta saka tace mashi tunda tay hankali ya d'age gira yace to shi miyasa bata ta6a ce mashi yakamata yaje garin su ba da sauri tace "to ai kai kaga Baffana ya sanka tun ma kafin muyi aure kuma gwaggota ma ta san ka amman shi fa ba wanda ya san shi gashi yanzu bai fi saura wata ukku ba bikin" shiru yay da alama nazarin Maganar yake can yay sigh yace mata yanzu dai bai K'asar amman yace zai zo bada dad'ewa ba in yazo zai ga abun da za'ai ta d'aga kai sai kuma tace "amman in kaga fa kaman da takura ko kawai ka bar Maganar in yaje bikin sun ganshi, kai ya girgiza mata yace ai yakamatan yaje saidai yazo,
"Ina son zaka taimaka man da abu" Sameer ya fad'a Haisam ya jinjina kai tare da dan gyara zaman shi ya tambayi miye yace mashi dama yana son zai siya ma su bride d'in tashi gida ne, kai Haisam ya d'aga kafin ya tambayi to wane taimako yake son yayi mashi yace bai san taya zai yi hakan ba tunda shi ba sanin garin su yayi ba kuma bai san kowa ba so yana son ya bashi shawarar yadda za'ai Haisam yace ya yi Maganar da Fauzy ne ya girgiza mashi kai alamar a'a kafin yace yafi tunanin yin Maganar da wani babba ba ita ba, shiru Haisam yay alamar tunani can yace mashi ya bari zasu yi Maganar da Wife d'in shi sai ta kira Yayarta tayi mata Maganar Sameer d'in yace Ok zai jira shi ya fad'i mata in tayi ma Yayar tata Maganar tace mata su duba gidan da suke so mai kyau in za'a samu Haisam yace Ok, hira suka d'an k'ara yi yawanci duk akan bikin Sameer d'in ne daga baya sukayi sallama, suna gama yin wayar ya kira Fatuu lokacin suna zaune a Bedroom d'inta da su Aunty Laila anata shirya yadda za'ai suna, bayan tayi picking tambayar ta yay tana tare da mutane ne tace mashi eh yace Ok bari zai tura mata sak'o ta WhatsApp tace to, lokacin da ta karanta sak'on daya turo matan d'an waro ido tay alamar mamaki sai kuma ta hau yin d'an murmushi, sai wuraren k'arfe goma da rabi sannan duka aka watse daga hirar da ake a d'akin Jidderh ma da anan take kwana tace ma Fatun bari taje ta dawo, suna tafiya cike da zumud'i ta shiga kiran Aunty Mareeya, saida ta kusa yankewa sannan ta d'auka bayan sun gaisa ta tambayi twins Fatun tace mata k'ilan ma har tayi bacci ta tada ita ko tace mata a'a bata kusa da wayar ne, tambayarta ina Fauzy tay tace mata tana d'akin ta bata san ko tayi bacci ba ta tambayi ita zata ba wayar ne da sauri Fatun tace a'a dama sak'o ne aka bata da alamun d'an mamaki tace mata to waye ya bada sakon tace mata Sameer har saida Aunty ta maimaita sunan Sameer d'in kafin ta tambayi sak'on miye ya bada, bayanin da yayi Fatun tayi mata bayan ta gama da tsananin mamaki Aunty Mareeya ta maimaita abunda ta fad'a tace mata eh haka yace,
"Kinga Zarah wllh nama rasa mi zance maki tsabar Al'ajabi, yanzu duk uban hidiman da yake ma Fauziyya kuma harda wannan gingimemiyar dawainiyar Gida fa!" Dariya Fatuu tay jin yadda tayi Maganar tace " Wllh Aunty, yana da halin ne kuma k'ilan yana son canza gidanne Saboda bikin tunda kinga ba k'aramar hidima za'ai ba manyan mutane zasu zo" Aunty tace "hakane kam, dama muma munata shirin yin gyaran gidan don har an gama Magana ma da masu gyaran za'ai gyara sosae Saboda hakan yanzu kuma kinga ga Maganar da yayi ni bamma san to mi zan ce ba, amman abunda za'ai Zarah zan kira babban yayanmu sai muyi magana kan hakan tunda ma gobe zamu taho nan in muka zo komi mukai dashi zan fad'i maki sai ki fad'i ma Mijin naki" amsa mata da to Fatun tay tace Allah ya kawo su lafiya duk ta k'agara ta gan su wllh Auntyn na dariya tace suma bata ga yadda suka k'agara da su ganta ba amman sun fi k'agara da suka ga twins d'in su Fatun nata dariya Aunty Mareeyar ta k'ara cewa "ni kinsan abunda ma yafi damuna Zarah?" Kai Fatuu ta girgiza kafin tace mata a'a,
"Wllh abunda nike gudu kada sai mun zo munyi kayan d'aki suce basu so tunda kinsan Manyan nan yadda suke" kai Fatuu ta jinjina tace hakane kuma fa, Aunty tace wllh abunda take ta tunani kenan, shiru Fatun ta d'anyi kafin can tace mata to ko tayi ma Ya Haisam magana kan hakan da sauri Aunty tace "kice mashi mi Zarah! A'a kada kiyi mashi magana kan hakan kada kuma aga kamar so muke ace kada ayin, za'a yi mata komai iya karfin mu dama mun yanke za'a siya mata kayan ne kawai Babanmu ya yanke zai siyar da gonakin shi guda biyu sai a had'a da sauran kud'in da aka tanada in sha Allahu za'ai komai yadda yakamata" Fatuu tace Allah ya bada iko ta amsa da Amin,
"Ni kinsan ma abunda nafi so wllh shine in da zai yuwu da yaje Funtua sun gaisa dasu don duk fa ba wanda ya san shi in ba a hoto da aka nuna masu shi ba to kuma hakan nasan da kamar wuya tunda yanzu ma bai K'asar tun kafin ya tafi nayi ma Fauziyya Maganar kan tasa shi yazo sai ce man tayi wai ita gaskiya bata iyawa ni in yi mashi, to wai kar aga kai talaka ka zaqe yasa ban yin ba kuma ma dai nima nasan halin surukin nawa baud'add'e ne" Dariya Fatuu tasa Auntyn tace Allah kuwa yanzu dai ai sai kawai da biki sun gan shi, hira suka d'an k'ara yi kafin sukai sallama ta kira Haisam d'in tayi mashi bayanin abunda Aunty tace yace Ok Allah ya kaimu goben ya kawo su lafiya, cikin yar shagwaba ta tambayi yana ina yana murmushi yace mata gashi a part d'in shi tace mi yake ya bata amsa da yana wani aiki ne tay shiru yayin da zuciyarta ta shiga raya mata kilan ma a part d'in shi Fanan ke kwana jin tayi shiru yasa shi tambayar ta koda wani abu ne da sauri tace mashi a'a tayi mashi saida safe yana murmushi ya amsa har zata kashe taji yace tana tare da mutane ne a hankali tace mashi a'a ita kad'ai ce Jidderh taje ta dawo yace Ok bari yazo suyi bankwana da Babies tay d'an murmushi tace to, aje wayar tayi ta juya tana kallon yaran dake kwance saman gadon suna bacci sam basu da rigima da sun yi kuka yawanci yunwa suke ji, bada jimawa ba sai gashi ya shigo cikin d'akin da sallama ta d'aga kai ta kalle shi ya sakar mata murmushi itama haka, cikin d'akin ya nufo ya tsaya d'an nesa da ita yace bazatai welcoming nashi ba tunda shi bak'o ne yanzu, yar dariya tayi ta mik'e ta nufe shi tana zuwa gabanshi ta fad'a jikin shi ya rungumeta suna ta sakin murmushi ga k'amshin jikinsu ya cika ma kowa hanci, d'agowa tay tace mashi ya zauna atare suka zauna idon shi akan yaran ya tambayi ya suke itama kallon su take tace mashi lafiya lou, juyowa tay suka had'a ido ta d'an langa6ar da kai cikin lumshe ido Slowly ya furta mata "I'm missing you" dan buda ido tayi still da murmushi akan Fuskar ta k'asa k'asa tace "ba gani a kusa da kai ba" d'age gira yay yace ba shi ba itama ta d'age mashi tace wanne, wani irin kashe mata ido yay ta saki dariya shima yar dariyar yay ya jawota jikin shi, kai hannu tayi
tana shafa beard cikin salo tace "na gode ma Allah dayasa na haihu lafiya naci gaba da yin rayuwa da kai" lumshe mata ido yay a hankali yace shima haka tana niyyar k'ara yin magana suka ji an shigo a tare suka kai idon su kan kopar Jidderh ce tayi shirin bacci tana ganin su ta dan waro ido tana murmushi kunya ce ta kama Fatuu ta fara k'ok'arin raba jikinta da nashi saidai yak'i bata dama ganin haka yasa Jidderh cewa ta bashi 10 minutes zata je ta dawo harda jaddada mashi da hannu duk sukai yar dariya, bayan ta fita Fatuu ta maida idonta kan shi tace tana son yi mashi wata Magana ya d'aga kai kafin yace yana ji,
"Dama so nike in ce kaman yakamata Ya Sameer yaje Funtua su gaisa da iyayen Fauzy Saboda ba wanda yasan shi fa" shiru yay idon shi akanta can yace mata sun yi magana kan hakan ne da sauri tace a'a kawai itace tayi tunanin hakan, Wani kallo yay mata yace "Kai yar fillona yaushe kika iya yin wannan tunanin" dariya ta saka tace mashi tunda tay hankali ya d'age gira yace to shi miyasa bata ta6a ce mashi yakamata yaje garin su ba da sauri tace "to ai kai kaga Baffana ya sanka tun ma kafin muyi aure kuma gwaggota ma ta san ka amman shi fa ba wanda ya san shi gashi yanzu bai fi saura wata ukku ba bikin" shiru yay da alama nazarin Maganar yake can yay sigh yace mata yanzu dai bai K'asar amman yace zai zo bada dad'ewa ba in yazo zai ga abun da za'ai ta d'aga kai sai kuma tace "amman in kaga fa kaman da takura ko kawai ka bar Maganar in yaje bikin sun ganshi, kai ya girgiza mata yace ai yakamatan yaje saidai yazo,