← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 81 OF 211

Sashe 81

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe gari bayan sun yi sallar Asuba komawa Fauzy tay ta kwanta Fatuu kau Kitchen ta nufa don ta samu abunda zata ci ita kuma Mino dama bata tashi ba don ba sallar take ba, sauran Abincin da suka ci jiya data ga bai yi komai ba ta d'umama sai ta had'a da tea, anan cikin kitchen d'in ta zauna taci bayan ta gama ta koma d'akin itama ta koma ta kwanta, wuraren K'arfe takwas saura Mino ta farka lokacin su Fatuu nata shan bacci ta wuce toilet, bata dad'e ba ta fito tayo wanka ta maida kayan baccin jikinta gaban mirror ta nufa ta shafa mai bayan ta gama ta juya ta nufi k'opa, a parlor ta d'auki hijab d'inta data cire da daddare ta saka sannan ta nufi gida don tayi shirin islamiyya.

Wuraren k'arfe sha biyu na rana suka fara shirin tafiya zaga gari kamar yadda akai jiya, bayan duk sun yi wanka suka shiga duba kayan da Fauzy zata saka saidai duk kayan Fatun bazasu yi mata daidai ba Saboda yanayin jikin su ba d'aya ba, k'arshe wata jallabiya suka samu da tayi mata daidai sabuwa ce acikin kayan lefenta da gani ita Fatun in tasa zata d'an yi mata yawa dama ko wadda taba Fauziyyar a Abuja itama tayi mata yawa yawanci dama da ganin dogayen rigunan wasu zasu yi mata yawa amman in ta saka takalma masu tsini ko tudu zasu iya yi mata daidai, itama Fatun shiryawa tay da riga half gown da straight skirt na atampa Fauzy ce tayi mata d'aurin kallabi mai kyau bayan an gama ta fiddo takalma da jaka da suka hau da atampar takalman masu dan tsini ne har Fauzy saida tay mata magana kansu tana murmushi tace ai tsinin nada gwa6i, rolling veil d'in jallabiyar Fauzy tay Fatuu kuma ta d'aukko mayafi daya hau da kayan sosae tayi kyau Fauzy ma ta yaba tace bari tayi mata hoto, atare sukai wasu hotunan bayan sun gama suka tafi gidan gwaggo don suga in su Mino sun shirya dama bayan sun yi Breakfast da suka je gaishe da Hajiya Fatuu ta sanar mata zancen fitar tasu. A can gidan suka ci Abincin rana lokacin Mino ta yi wanka kaya kawai zata saka haka Kawu Amadu ma ya shirya yana d'akin shi gwaggo ma da ita za'aje farko da tace bazata je ba suka matsa mata dole ta shirya, bayan kowa ya gama shiryawa Fatuu ta kira Tk ta sanar dashi yace gashi nan zuwa, bada jimawa ba yazo ya kira Kawu Amadu ya sanar dashi su fito, a tare duk suka fito gwaggo ta kulle gidan tana sanye da riga da zani na atampa tasa Hijab data hau da kayan hannunta ruk'e da purse, kowa fuskar shi da murmushi suka nufo Motar da sai shek'in sabunta take, ganin in suka zauna baya zasu iya matsewa yasa Kawu Amadu yace ma Mino tazo su zauna a gaba sai su kuma su ukku suka shiga baya, zagaya gari suka shiga yi suna hira cikin nishad'i ga Ac na ratsa sassan jikin su sai faman santin Motar suke ita dai Fatuu murmushi kawai take saki don ganin abun take kamar wasa wai wannan Motar ta ce, sosae suka zaga gari saida aka fara kiran sallar la'asar suka wuce gidan Aunty Mareeya, suna zuwa bakin layin gidan Fauzy ta kirata tace tazo ta tarbe su, Fauzy ce ta nuna ma Tk gidan yana Parker Motar gaban gidan sai ga Aunty Mareeyar ta fito tana sanye da doguwar rigar material ta yafa gyale saman kanta da ya bayyanar da gaban kanta daya sha kitso da alama dai tana son dogayen riguna koda yake mutane irin ta dama ita tafi dacewa da su don tana amsar su sosae, cikin washe baki ta nufo Motar duk suka bud'e suka fito, gaisawa suka shiga yi tana yi masu sannu da zuwa Fauzy ta nuna mata Motar tace ga Motar Zarah ta waro ido tana fad'in Don Allah wai wannan bugaggar Motar mai numfashi ce aka siya ma Zarah duk akai dariya, matsawa tay ta fara bin Motar tana dubawa sai faman fad'in ma sha Allah take tana zuba santi, bayan ta gama gani ta juyo tana fad'in wllh ta taya Zarah murna Allah yasa Alkhairi ya tsare gwaggo ta amsa tace masu suyi hak'uri tabar su a tsaye don Allah su shiga, a parlor duk suka zazzauna aka shiga k'ara gaisawa kafin ta mik'e tace ma Fauzy tazo suka nufi Kitchen, dawowa Fauzyn tay tana ruk'e da babban tray da aka jero kayan abinci Aunty Mareeyar ma ta biyo bayanta ruk'e da Warmers masu kyau babba da kuma madaidaiciya, tambayarta Fauzy tay ta kai dining table ne tace mata a'a akai cikin parlon yadda zasu fi jin dad'in bajewa su ci duk akai murmushi, farko cewa sukai duk basu jin yunwa don saida suka ci Abinci sannan suka fito Aunty tace ai tasan sun ci Abinci amman dole itama a ci nata ba kamar su Amadu da Tk da basu ta6a zuwa ba ta kalli Fatuu tace Maman biyu kedai ai nasan zaki ci ko ta d'aga mata kai tana dariya, Aunty tace "haba ai ina ganin wannan kumatukan da kika aje Tubarkallah nasan bakya wasa da Abinci" duk akai yar dariya ta sake cewa "ai angode ma Allah ma gara laulayin cin Abincin da ai ta amaye amaye" gwaggo tace aikuwa hakan yafi, saida kowa yaci Abincin bayan sun gama Amadu da Tk suka tafi Masallaci yin sallar la'asar da aka kira su gwaggo ma suka mik'e Aunty ta kai ta d'akin ta ita kuma Fatuu ta nufi d'akin Fauzy, bayan duk sun yi sallar har su Amadu ma sun dawo a parlon suka zauna aka shiga hira Aunty Mareeya na ta sasu dariya, sai wuraren k'arfe biyar suka fito Aunty tace ma Fauzy ita ta dawo gida ko da sauri Fatuu tace a'a sai gobe zata dawo Aunty tace "an gama ranki ya dad'e uwar biyu farincikin ki shi muke buk'ata yanzu" duk akai dariya tace gaskiya itama ya kamata ta d'ana Motar Tk yace to ta shiga sai ya zagayo da ita tace Yauwa to, seat d'in baya ta shiga ta wani hakimce har saida ta basu dariya, tsayawa sukai yaje ya zagayo da ita bayan sun dawo ta fito tana k'ara yabawa da Addu'oi, sallama sukai da mata tayi masu godiya tana fad'in taji dad'i sosae wllh Allah ya bar zumunci duk suka amsa tace ma gwaggo sai tazo yi mata yini tana murmushi tace to tana jiran ta daga haka duk suka shiga cikin Motar suna d'aga ma juna hannu suka tafi, k'ara zagaya gari sukai sai gab da Magrib suka koma gida harda tsaraba suka yo, gwaggo da Amadu aka fara ajewa tay ma Tk godiya da Allah ya huta gajiya suka wuce, har bakin part d'in Hajiya ya kai su bayan sun fito suka shiga ciki don kai mata tsaraba. A part d'in sukai sallar Magrib da isha suka ci Abincin dare bayan sun d'an yi mata hira sannan suka komo part d'in su Fatuu. Washe gari Lahadi bayan sun ci Abincin rana sun shirya suka tafi gidan gwaggo har saida tay ma Fatuu Maganar zuwan tace ba jiya ta zo ba tace ai jiya ba nan suka zo ba don zasu fita ne yau ne zuwan nata Fauzy nata masu dariya, bayan sallar La'asar lokacin Mino ta tafi Makaranta Fatuu tace ma Fauzy suje su gaida innar su Haulat suka tafi, lokacin da suka isa gidan sosae tay murnar ganin su tace ma Fatuu maimakon ta bari ita tazo ta dubata ai bata san ta dawo bane da tazo tana murmushi tace mata ba komai, sai gab da Magrib suka baro gidan suka koma gidan gwaggo, ana gama sallar Magrib tace ma Fatuu ta koma gida suka tafi tare da Fauzy da Mino, bayan sun yi sallar isha Fauzy ta fara yin shirin tafiya gida don gobe Monday, rigar material d'inta ta maida Fatuu na fad'in ta bar ta jikinta amman ta k'iya, duk da haka saida ta bata kyautar kayan shafa da turare guda biyu harda panties da vest mai had'e da wando sai sark'a da yan kunne masu kyau, farko k'in amsa Fauzyn tay tace ai abun yayi yawa ina laifin duk abubuwan Alkhairin da aka yi masu acan Abujar, magiya Fatun ta hau yi mata kan ta amsa tana fadin ai don tana da su ne ta bata ko k'arshe saida ta nuna mata 6acin rai sannan ta amsa tayi mata godiya da Addu'ar Allah ya sauketa lafiya, Tk ta kira ta tambayi yana gida yace eh yanzu dai yake niyyar fita ta rok'e shi kan ya aje Fauzy gida yace Ok ta fito, tare suka fito harda Mino suka nufi part d'in Hajiya don tayi mata sallama, tana zaune a parlor suka shigo bayan duk sun zauna suka gaishe da ita ta amsa Fatuu tace mata dama Fauzy ce zata tafi shine tazo yi mata sallama Hajiyar ta tambayi taci Abinci ne Fauzyn tace eh sun ci a gidan gwaggo, ce mata Hajiyar tayi bari a kawo mata ta k'ara sai ta tafi tana murmushi tace ta k'oshi ai basu dad'e da suka ci ba, Tk ne ya kira Fatuu yace gashi yazo parking space bai ganta ba ko bata fito bane tace mashi gasu nan zuwa, kallon Fauzy tay tace suje ga Tk d'in can yazo duk suka mik'e Hajiya tace ta bari a bata kud'in Napep Fatuu tace ai Tk ne zai kaita gashi can ma ya fito tace to hakan yayi tay ma Fauzy godiya da Addu'ar Allah ya bar zumunci ta amsa tana murmushi suka tafi, lokacin da suka fito har Tk ya fiddo Motar Fatun cikin harabar, bayan sun k'arasa a gefen Motar suka tsaya suna k'ara yin sallama Fatuu tace mata sai sun had'u gobe a School Fauzy tace "ai nayi zaton zaki k'ara hutawa tunda ana maki komai online" ce mata tay a'a zata cigaba da zuwa tunda ta dawo dama ba wani jin dad'in karatun take ta online ba tunda ba haka ta saba ba kawai don ya zama dole ne tace Shikenan to sai sun had'u goben tay ma Mino sallama ta shiga gaban Motar dama Tk na driver seat yaja suka tafi su kuma suka koma part d'in Hajiya.....
Chapter 81 · 0% Book details