Sashe 58
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
cire hannun tayi har lokacin sai yamutsa fuska take shi kuma sai dariya yake, ce mashi tay don Allah yaran su sun isa haka tun kan ta rufe baki ya hau girgiza mata kai yana mata wani kallo yace "indai irin yaran da kike Haifa man ne basu ishe ni ba ina buk'atar K'ari" Murmushin jin dad'i tay ba tace komai ba ya d'age gira yace za'a k'ara Haifa mashi ko, d'an rolling eyes d'in ta tay tace Shikenan amman saidai tun daga rainon cikin har zuwa haife shi ba'a K'asar nan zata yi ba da sauri yace in hakan yayi mata ai ba matsala bane duk inda take so sai akaita kuma zai bi ta, dariya tay ta girgiza kai, tambayar shi tay ta k'ara mashi shayin ya d'aga mata kai, tashi tay daga saman jikin shi ta k'ara mashi, bayan ya shanye ta k'ara tambayar a k'ara yace a'a ya isa, mik'ewa tay zata dauke flask din yana kallon ta yace ta bari sai da Safe mana ta fitar da shi, mik'ewa tay tana d'auke da tray d'in tace mashi tana son taje ta tambayi Daughter ko akwae abunda take so kafin tay bacci ya jinjina kai ta juya, bin ta yay da kallo tana tunkarar hanyar fitan a kullum gani yake ta na k'ara mashi yarinta a maimakon manyanta, in yace ga wani nakasu nata daya sa shi k'ara Aure to yayi k'arya kawai dai yasan duk abunda Allah ya k'addaro ma bawan shi to tabbas sai ya faru da shi amman yana matuk'ar k'aunar matar shi a yanzu kam sam baida ma ra'ayin k'ara aure, su yar Munah da bahillot sai a fidda rai🤧
Misalin k'arfe goma sha d'aya da wasu mintuna su Fauzy na zaune a parlor suna kallo ita da Mino da Zainab Haulat dai tunda ta tafi kwantar da babynta bata dawo ba da alama tayi bacci, harda su Aunty Mareeya da su Yadikko ake ta kallon Film d'in, Fauzy na zaune jikinta sanye da doguwar rigar atamfa ta soke d'aurin kallabi ta yadda gashinta ya fito ta k'asa, wayarta ce dake a gefenta ta fara ringing ta kai idon ta, d'aukko wayarta tay ta zuba ma kwankwatsattsen glass d'in ido tana kallon bak'uwar lambar da ake kiran nata da ita, kaman bazata d'aga ba sai kuma tay picking, karata tay a kunne ba tare data ce komai ba tana jiran taji mi za'a je, jin shirun yayi yawa yasa tay sallama,
"Meet me in the parking lot" shine taji an fad'a da yar kakkausar murya daga haka kuma akai cutting kiran, cire wayar tay daga kunnanta ta bita da ido, tunanin waye wannan da yace ta iske shi a wurin ajiye motoci ta shiga yi, tunanin muryar waye ta fara yi can zuciyarta ta raya mata ta Sameer ce har saida gabanta yay wani bugu, kokonto ta shiga na anya kuwa shida sun tafi kuma in ma shine ta ina ya samu lambarta, zuciyar ta ce ta raya mata taje ba sai ta ga koma waye ba, mik'ewa tay ba wanda hankalin shi ya kawo kanta duk idanunsu na akan Tv, d'aki ta nufa ta d'aukko gyale ta yafa sannan ta fito tana ruk'e da wayar, tana a kan hanyar zuwa aka k'ara kira da lambar, tana d'agawa taji ance "Don't waste my time!" tana jin hakan ta tabbatar da Sameer, sauri ta shiga yi gabanta na d'an fad'uwa sai fargabar dalilin kiran nata take, lokacin data k'araso tsaye tay tana kallon cikin parking space d'in wanda yake dankam da motoci rasa a ina yake tay sai faman waige waige take, horn d'in da taji anyi ne yaja hankalinta da sauri ta kai idon kan Motar da taga ta saki danja wadda ke a d'an gabanta daga wajen parking space d'in, nufar Motar tayi a d'arare ta zagaya d'ayan 6angaren, tsaye tay a bakin kopar ta sake ji anyi horn hakan yasa ta kai hannu har rawa yake ta bud'e k'opar, wani irin k'amshi ne ya bugi hancinta ta d'an lek'a kanta yana zaune a driver seat jikinshi sanye da k'ananun kaya, murya na rawa ta gaishe dashi yay shiru tamkar bai ji ta ba kuma bai kalle ta ba, saida ya mula sannan taji yace ta shigo, a tsorace ta shiga ta zauna a kujerar gaban ba tare data rufe kopar ba hannun ta guda na ruk'e da ita, juyowa yay ya kalli kopar kafin ya kalleta ya d'aure fuska tamau nan take ta gane mi hakan ke nufi ta rufo k'opar, k'ara gaida shi tay yay d'an Jim sai kuma taga ya jinjina mata kai, shiru sukai sai Ac dake ta aiki tana bugun fuskarta, a k'alla sun d'auki wasu mintuna a haka ba tare da yace mata komai ba sai latsa waya yake tana ta d'an satar kallon shi saidai sam bata ji ta gaji da zaman ba, tana satar kallon nashi ta lura da wayar hannun shi kamar ba wadda ta fashe ba don wannan ta hango glass d'in ta lafiya lau, sai can sannan yay mata nuni da wani abu dake a gefen shi da Hannun shi taji yace ta d'auka cikin d'aurewar kai ta kai hannu ta d'aukko abun wadda yar jakar kwali ce k'arama tana da yan igiyoyin kamawa daga jikinta akwae hoto saidai bata duba ba balle ta gane ko ta miye, rik'e jakar tay a jikinta ta maida idon ta akan shi lokacin taji yace gashi nan ya biya ta damage d'in da yay ma wayarta saura ita, yamutsa fuska ta fara yi a marairaice ta fara bashi hak'uri tana fad'in Allah tasan bazata iya biyan shi ba, banza yay mata kuma har lokacin bai kalleta ba can tace mashi to ga wannan d'in ya bar shi ba sai ya biya ta ba Shikenan, kawai sai gani tay yay wani guntun murmushi wanda yafi kama da a kira shi na mamaki, sai lokacin ya juyo suka had'a ido gabanta yay wani irin bugu ganin yadda ya d'aure fuskar, "kina da waya ne?" Ya tambaya had'i da d'age mata gira wani miyau ta had'iya don ta fahimci tambayar yana nufin wayarta waya ce, a hankali ta girgiza mashi kai alamar a'a cigaba da kallon ta yay da yake wurin fayau yake da hasken fitilu kuma glass d'in Motar baida duhu sosae hasken ya d'an haska cikin Motar ba kamar da yake a inda suke akwae fitilar data haska saitin Motar, sai yan kame kame take ganin yadda ya kafeta da ido, janye idon yay taji yace ta tafi godiya tay mashi har ta juya zata bud'e Motar kamar daga sama taji yace "zaki aure yaushe?" Da sauri ta juyo ta kalle shi, sai ka rantse ba shi yay Maganar ba idon shi na akan Wayar shi, kokonto ta shiga yi na kodai kunnuwan ta ne suka ji mata ba daidai ba nan take ta gasgata hakan tana niyyar juyawa taji yace ba tambayar ta yay ba, maida idonta tay kan shi da tsananin mamaki take kallon shi har saida ta had'iyi abu kafin tace mashi ita ko rana ba'a saka mata ba ai,
"Why?" taji ya fad'a ba tare daya kalleta ba, ce mashi tay bata da wanda ta tsaida zata aura, shiru ya d'anyi kafin taji yace ko dai bata da masu sonta ne, har saida tay d'an murmushi tare da girgiza mashi kai tace mashi ana cewa ana sonta sosae itace dai bata bada dama Why, ya k'ara ce mata tay d'an jimm kafin tace akwae wanda ta tsaida zata aura amman sai ya guje ta ita kuma sai bata k'ara jin tana son wani ba, dakatawa yay da latsa wayar ya juyo ya kalleta suka had'a ido har lokacin Fuskar shi kaman a d'aure take har ta fara tunanin kodai haka yanayin fuskar tashi take, tambayar ta yay mi tay mashi ya gujeta idon shi a cikin nata, kikkafta idanu ta shiga yi ta fara bashi labarin tun farkon had'uwar ta da Mujaheed har zuwa lokacin da ta samu labarin auren shi sai dai a tak'aice take gaya mashi, lokacin data gama idanunta ne suka ciko da k'walla da sauri ta sunkuyar da kanta tasa gefen gyalenta tana goge kwallan, tana haka taji yace ai wannan ba wani abu bane he found someone da yake tunanin is better than her so he left her, da sauri ta d'ago ta kalle shi cikin muryar kuka tace "amman fa tsawon lokaci muna tare da shi in yasan bazai aure ni ba miyasa tun farko zai sa ni in yarda da shi har yayi man Alk'awarin Aure, Saboda shi bana saurarar kowa kuma yasan hakan amman ya yaudare ni, dama ashe yasan ba aure na zaiyi ba wai haka yace ma abokin shi daya fad'a man zancen yayi aure wai burge shi nike shiyasa yake tare da ni" har ta gama Maganar idon shi na akan ta, janye idon yay yana wani d'an murmushin bata san miye duniya ba shiyasa ta d'auki hakan wani babban abu, tanata goge k'walla ya juyo suka had'a ido cikin Maganar shi mai cike da isa yace mata in a relationship she shouldn't trust completely don abunda yafi hakan ma za'a iya mata koma miya faru da ita shi a wurin shi itace tay kuskure amman yasan hada don bata da wayau ne tana rayuwa a k'auye, shiru tay tana sauraran shi saidai sam bata ji komai ba a Maganganun da yayi don ita bata ma yi zaton zai iya yin magana da ita ba haka,
Misalin k'arfe goma sha d'aya da wasu mintuna su Fauzy na zaune a parlor suna kallo ita da Mino da Zainab Haulat dai tunda ta tafi kwantar da babynta bata dawo ba da alama tayi bacci, harda su Aunty Mareeya da su Yadikko ake ta kallon Film d'in, Fauzy na zaune jikinta sanye da doguwar rigar atamfa ta soke d'aurin kallabi ta yadda gashinta ya fito ta k'asa, wayarta ce dake a gefenta ta fara ringing ta kai idon ta, d'aukko wayarta tay ta zuba ma kwankwatsattsen glass d'in ido tana kallon bak'uwar lambar da ake kiran nata da ita, kaman bazata d'aga ba sai kuma tay picking, karata tay a kunne ba tare data ce komai ba tana jiran taji mi za'a je, jin shirun yayi yawa yasa tay sallama,
"Meet me in the parking lot" shine taji an fad'a da yar kakkausar murya daga haka kuma akai cutting kiran, cire wayar tay daga kunnanta ta bita da ido, tunanin waye wannan da yace ta iske shi a wurin ajiye motoci ta shiga yi, tunanin muryar waye ta fara yi can zuciyarta ta raya mata ta Sameer ce har saida gabanta yay wani bugu, kokonto ta shiga na anya kuwa shida sun tafi kuma in ma shine ta ina ya samu lambarta, zuciyar ta ce ta raya mata taje ba sai ta ga koma waye ba, mik'ewa tay ba wanda hankalin shi ya kawo kanta duk idanunsu na akan Tv, d'aki ta nufa ta d'aukko gyale ta yafa sannan ta fito tana ruk'e da wayar, tana a kan hanyar zuwa aka k'ara kira da lambar, tana d'agawa taji ance "Don't waste my time!" tana jin hakan ta tabbatar da Sameer, sauri ta shiga yi gabanta na d'an fad'uwa sai fargabar dalilin kiran nata take, lokacin data k'araso tsaye tay tana kallon cikin parking space d'in wanda yake dankam da motoci rasa a ina yake tay sai faman waige waige take, horn d'in da taji anyi ne yaja hankalinta da sauri ta kai idon kan Motar da taga ta saki danja wadda ke a d'an gabanta daga wajen parking space d'in, nufar Motar tayi a d'arare ta zagaya d'ayan 6angaren, tsaye tay a bakin kopar ta sake ji anyi horn hakan yasa ta kai hannu har rawa yake ta bud'e k'opar, wani irin k'amshi ne ya bugi hancinta ta d'an lek'a kanta yana zaune a driver seat jikinshi sanye da k'ananun kaya, murya na rawa ta gaishe dashi yay shiru tamkar bai ji ta ba kuma bai kalle ta ba, saida ya mula sannan taji yace ta shigo, a tsorace ta shiga ta zauna a kujerar gaban ba tare data rufe kopar ba hannun ta guda na ruk'e da ita, juyowa yay ya kalli kopar kafin ya kalleta ya d'aure fuska tamau nan take ta gane mi hakan ke nufi ta rufo k'opar, k'ara gaida shi tay yay d'an Jim sai kuma taga ya jinjina mata kai, shiru sukai sai Ac dake ta aiki tana bugun fuskarta, a k'alla sun d'auki wasu mintuna a haka ba tare da yace mata komai ba sai latsa waya yake tana ta d'an satar kallon shi saidai sam bata ji ta gaji da zaman ba, tana satar kallon nashi ta lura da wayar hannun shi kamar ba wadda ta fashe ba don wannan ta hango glass d'in ta lafiya lau, sai can sannan yay mata nuni da wani abu dake a gefen shi da Hannun shi taji yace ta d'auka cikin d'aurewar kai ta kai hannu ta d'aukko abun wadda yar jakar kwali ce k'arama tana da yan igiyoyin kamawa daga jikinta akwae hoto saidai bata duba ba balle ta gane ko ta miye, rik'e jakar tay a jikinta ta maida idon ta akan shi lokacin taji yace gashi nan ya biya ta damage d'in da yay ma wayarta saura ita, yamutsa fuska ta fara yi a marairaice ta fara bashi hak'uri tana fad'in Allah tasan bazata iya biyan shi ba, banza yay mata kuma har lokacin bai kalleta ba can tace mashi to ga wannan d'in ya bar shi ba sai ya biya ta ba Shikenan, kawai sai gani tay yay wani guntun murmushi wanda yafi kama da a kira shi na mamaki, sai lokacin ya juyo suka had'a ido gabanta yay wani irin bugu ganin yadda ya d'aure fuskar, "kina da waya ne?" Ya tambaya had'i da d'age mata gira wani miyau ta had'iya don ta fahimci tambayar yana nufin wayarta waya ce, a hankali ta girgiza mashi kai alamar a'a cigaba da kallon ta yay da yake wurin fayau yake da hasken fitilu kuma glass d'in Motar baida duhu sosae hasken ya d'an haska cikin Motar ba kamar da yake a inda suke akwae fitilar data haska saitin Motar, sai yan kame kame take ganin yadda ya kafeta da ido, janye idon yay taji yace ta tafi godiya tay mashi har ta juya zata bud'e Motar kamar daga sama taji yace "zaki aure yaushe?" Da sauri ta juyo ta kalle shi, sai ka rantse ba shi yay Maganar ba idon shi na akan Wayar shi, kokonto ta shiga yi na kodai kunnuwan ta ne suka ji mata ba daidai ba nan take ta gasgata hakan tana niyyar juyawa taji yace ba tambayar ta yay ba, maida idonta tay kan shi da tsananin mamaki take kallon shi har saida ta had'iyi abu kafin tace mashi ita ko rana ba'a saka mata ba ai,
"Why?" taji ya fad'a ba tare daya kalleta ba, ce mashi tay bata da wanda ta tsaida zata aura, shiru ya d'anyi kafin taji yace ko dai bata da masu sonta ne, har saida tay d'an murmushi tare da girgiza mashi kai tace mashi ana cewa ana sonta sosae itace dai bata bada dama Why, ya k'ara ce mata tay d'an jimm kafin tace akwae wanda ta tsaida zata aura amman sai ya guje ta ita kuma sai bata k'ara jin tana son wani ba, dakatawa yay da latsa wayar ya juyo ya kalleta suka had'a ido har lokacin Fuskar shi kaman a d'aure take har ta fara tunanin kodai haka yanayin fuskar tashi take, tambayar ta yay mi tay mashi ya gujeta idon shi a cikin nata, kikkafta idanu ta shiga yi ta fara bashi labarin tun farkon had'uwar ta da Mujaheed har zuwa lokacin da ta samu labarin auren shi sai dai a tak'aice take gaya mashi, lokacin data gama idanunta ne suka ciko da k'walla da sauri ta sunkuyar da kanta tasa gefen gyalenta tana goge kwallan, tana haka taji yace ai wannan ba wani abu bane he found someone da yake tunanin is better than her so he left her, da sauri ta d'ago ta kalle shi cikin muryar kuka tace "amman fa tsawon lokaci muna tare da shi in yasan bazai aure ni ba miyasa tun farko zai sa ni in yarda da shi har yayi man Alk'awarin Aure, Saboda shi bana saurarar kowa kuma yasan hakan amman ya yaudare ni, dama ashe yasan ba aure na zaiyi ba wai haka yace ma abokin shi daya fad'a man zancen yayi aure wai burge shi nike shiyasa yake tare da ni" har ta gama Maganar idon shi na akan ta, janye idon yay yana wani d'an murmushin bata san miye duniya ba shiyasa ta d'auki hakan wani babban abu, tanata goge k'walla ya juyo suka had'a ido cikin Maganar shi mai cike da isa yace mata in a relationship she shouldn't trust completely don abunda yafi hakan ma za'a iya mata koma miya faru da ita shi a wurin shi itace tay kuskure amman yasan hada don bata da wayau ne tana rayuwa a k'auye, shiru tay tana sauraran shi saidai sam bata ji komai ba a Maganganun da yayi don ita bata ma yi zaton zai iya yin magana da ita ba haka,