Sashe 207
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Wait Dr, wai abunda kake son faɗi mana shine kana nufin ita Fanan ɗin ke ɗauke da ciki?" da tsananin mamaki Hajiya Maryam ta tambaya cikin girmamawa yace mata eh haka sakamakon ya nuna tana dashi na sati ukku yay maganar tare da miƙo mata wata farar takarda da aka naɗe, har saura kaɗan ta saki wayarta dake a hannunta wurin rawar hannun ta amsa, bayan ta buɗe Mom da Fatuu suma suka shiga dubawa nan idonsu ya tabbatar masu, da tsananin farinciki suka shiga washe baki Fatuu harda sa hannu guda ta rufe bakinta alamar mamaki, nan fa aka shiga yin murna su Esha harda tsalle suna faɗin Momy is pregnant zata haifa masu baby Allah ya amshi addu'ar su, nan fa aka fara kiraye kirayen waya ana ma yan'uwa albishir, ko ban faɗa ba ansan dole ai tsananin farincikin samun cikin, Mom ce ta kira Haisam lokacin ma yana kan hanyar zuwa tayi mashi albishir to shima dai ba ƙaramin mamaki da murna yay ba , kan kace mi ɗakin ya cika har Hajiya tazo da Farha anata farinciki, kyautar miliyan guda Hajiya Maryam tayi ma likitan daya faɗi masu zancen cikin Haisam ma ya ƙara mashi wata miliyan guda ɗin kakar likita ta yanke saƙa har ya rasa irin godiyar da zai yi, Mom na dariya tace to ai itama yakamata a bata kyautar tunda ita ta kirata ta sanar mata zancen ciwon duk akai dariya Hajiya Maryam ɗin tana dariya tace to ta bata kyautar Mota duk akai shewar murna, Mom nata dariya tace ita ta yafe Doughter yakamata a ba kyautar tunda ita ta kawota asibitin Hajiya Maryam ɗin tace to ta ba Fatun Motar, da sauri Fatuu tace a'a ta barta ai duk abun farincikin nasu ne Hajiya Maryam ɗin tace ta riga ta bata in bata so sai ta bayar, Esha na jin haka ta ruƙe ƙugu tace to ai suma tare dasu aka kawo Momyn a basu kyautar, hannu Hajiya maryam ta kai ta ɗan ja kumatunta tace ta faɗi abunda duk take so da sauri tace stroller take so da zata rinƙa tura baby aikuwa mi za'ai in ba dariya ba Hajiya Maryam ɗin tace an gama in ma guda goma take so zata siya mata ta juya kam Adam tace shi mi yake so yace kayan wasa da zai rinƙa yima Baby wasa harda Mota da zasu rinƙa shiga tare suna zagaye gida tace to shima za'a siya mashi, juyawa tay kan Abie da yayi shiru kai kace babu shi a wurin tana dariya tace "kai kuma miskilin mu mi kake so?" shiru yay yana bin ta da idanunshi da suke a ɗan lumshe duk da idanun nasu manya ne amman wani lokacin sai su lumshesu kamar dai yadda na Haisam ke yi, shiru yay bai tanka mata ba duk idanunsu na akan shi ana son aji mi zai ce don Magana mugun wuya take mashi wannan da alama ma sai yafi Haisam miskilanci dama ance wai kyawun magaji ya zarta, ganin baida niyyar magana yasa tace mashi in fa bai faɗi mi yake so ba to in aka haiho Babyn saidai ya rinƙa kallonshi do n baza'a bashi ba ya ɗauka balle har ya yi mashi wasa, ana jin abunda tace su Mom suka ce mashi ya faɗi mata ko so yake su Esha su rinƙa ɗaukar baby suna mashi wasa banda shi, a hankali ya fara motsa baki kafin da ƙyar cikin sanyayyar muryarshi ya furta Water Bottle yake so da zai rinƙa ba Babyn ruwa aikuwa mi za'ai in ba dariya ba har Haisam saida yayi dariyar Hajiya dake zaune tace ai shine Water Bottle ɗin aka ƙara yin dariyar, Fatuu dake zaune gefen Fanan ta lura da ita kamar bata farincikin samun cikin don ko uffan bata ce ba duk abun nan tana kwance sai ɗan murmushi da take in anyi abun dariya hakan yasa ta dafata tace "Aunty Fanan ya naga kamar baki farincikin samun cikin ko jikinne?" wannan Maganar da tayi ce ta maido hankulan yan ɗakin kan su Hajiya Maryam tace itama ta lura don ta ɗauka jin zancen cikin zai sa ma ta wartsake, ganin duk sun zuba mata ido yasa tayi ɗan faffaɗan murmushi tace tana farinciki mana saidai ita a wurinta already tana da yara so bata jin wannan kamar a cikinta na farko, gaba ɗaya Maganar tayi masu daɗi Hajiya dake murmushi tace gaskiya ne Maganarta, Auntyn su Haisam ce tace ya kamata a barta ta huta sun zo suna ta surutu a kanta Mom tace abun farinciki ne ya samu dole ayi murna, tambayar likita Aunty tay in ba wata matsala zasu tafi da ita ta huta sosae yace eh lafiya lou zai bata magunguna saboda zazza6i da ciwon kan sai kuma na amai da take, bayan sun koma cikin Villa a ɗaki daban ta kwanta aka kawo mata abinci da ƙyar ta ɗan ci bayan ta gama Fatuu ta bata magunguna tasha ta buƙaci yin wanka Fatuu ta taimaka mata, bayan tayi wanka kwanciya tayi nan da nan bacci ya ɗauketa, a ranar iyalan cikin farinciki suka kasance koda aka sanar da Laila itama tayi murna har tana cewa wannan dole tazo ta dubata, Fatuu nata so ta sanar ma Gwaggo saidai ta baro wayarta a gida, anan suka wuni sai bayan Magrib suka shirya komawa gida Hajiya Maryam tace ma Fanan ita mi zai hana ta tsaya ta ɗan kwana biyu tunda ba sanin irin yanayin tayi ba zata fi samun kulawa anan tana murmushi tace ai sister Fatuu ta sani zata kula da ita tunda tana cikin hutu dole tayi shiru amman ba don taso Fanan ɗin ta tafi ba a lokacin, bayan sunyi sallama da kowa Haisam ya ɗaukko su a jigunannar Jeep ɗin shi da bai daɗe da siyanta ba ita kuma Motar Fanan aka barta anan, saida Hajiya Maryam ta rakasu bayan sun isa gidan haka tay ta faman faɗi ma Fanan ɗin abubuwan da zata kiyaye gudun kada cikin ya samu matsala tace ma Haisam aiki ma ta daina zuwa ta ɗauki hutu har zuwa ta ƙara warwarewa yace Ok, ta ƙara cewa abinci ma asata ta rinƙa ci akai akai koda tana amayar dashi wani zai tsaya nan ma yace mata to kafin ya sake cewa likita ma yace maganin daya bata zai sa ta daina yin aman ta rinƙa cin abinci sosae in ma baiyi mata ba akwae wanda Zarah tayi amfani dashi a Us yana da kyau sosae sai yasa akawo mata cikin nuna jin daɗi tace to daga baya tayi masu sallama kamar kar ta baro Fanan ɗin don gani take kaman cikin zai iya samun matsala haka dai ta taho Fatuu da Haisam suka yo mata rakiya ta tafi, bayan sun koma ciki gaba ɗayansu a bedroom ɗin Fanan suka zauna tana kwance su Esha sun zagaye ta, hira suka shiga yi cike da farinciki daga baya Fatuu ta tambayi ko tana son wani abu ta haɗa mata da sauri ta girgiza mata kai tace ai bata daɗe data ci abinci ba a Villa Fatun tace to bari ta kawo mata fruit ba tare data jira cewarta ba ta saukko daga gadon ta nufi ƙopa, bayan fitarta bin juna sukai da kallo ita da Haisam suna sakar ma juna ƙayaaccen murmushi, saida Fanan ɗin tayi bacci sannan Fatuu ta koma ɗakinta lokacin ta kira Gwaggo ta sanar mata samun cikin ai tana ji ta shiga yin hamdala cikin tsananin farinciki ta tambayi ina Fanan ɗin ta tayata murna da sannu da jiki tace tayi bacci Gwaggon tace to in Allah ya kaimu zata kira, bayan ta gama wayar da Gwaggo Aunty Mareeya da Feenah ta kira suma ta sanar masu kowa yayi farincikin jin zancen samun cikin suna ta addu'oin Allah ya inganta, daren ranar gaba ɗaya Fatuu da Haisam saida suka yi nafila tsakar dare suka gode ma Allah tare da Addu'ar Allah ya inganta masu cikin ya sauketa lafiya. Kulawa sosae suke ba Fanan ɗin ba laifi kuma maganin da take amfani dashi yana mata aiki don tana cin abinci, bayan hutun Fatuu ya ƙare tace ma Haisam ko yayi ma Mom magana a turo Iya ta dawo nan gidan tunda ita dattijuwa ce zata taimaka ma Fanan ɗin sosae yace Ok, koda akai ma Mom magana cewa tayi lafiya lou sai ta dawo nan ɗin, ana washe gari Fatuu zata tafi Iya ɗin ta dawo nan gidan hakan ya ƙara kwantar ma da Fatuu hankali da tana ta zullumin tafiya ta barta duk da suna da masu aiki har biyu amman tafi son ace akwae wani babba na jiki a tare da ita hakanne ma yasa tayi tunanin a maido Iya ɗin nan.