← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 169 OF 211

Sashe 169

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 3 min read

A ranar Gwaggo taje ta sanar ma Hajiya itama tayi farinciki sosae tace Amadu ya kyauta Saude ma ta nuna farinciki, Tk na jin zancen Auren Amadun yace aikuwa bazai riga shi yin aure ba shima zaisa aje a nema mashi aure, da yamma Amadu na shago Haisam ya kira shi a waya cikin girmamawa ya gaishe dashi bayan ya ɗaga Haisam ɗin yace mashi yaji abun farinciki Allah yasa Alkhairi Amadun na murmushi ya amsa tare da yi mashi godiya, tambayarshi Haisam ɗin yay akwae gida na kusa da gidan su yana son sanin wanda ke ciki haya suke ko kuwa nasu ne da alamun rashin fahimta Amadun ya tambayi wanne ciki yace duka na left da right ya bashi amsa da na bangaren dama gidan kansu ne sai na hagu wato gidan su Umar su haya suke Haisam ɗin yace mashi yasan mai gidan yace mashi eh wani Alhaji Isah ne shima anan unguwar yake daga can ƙasa yace mashi yana da lambarshi Amadun yace a'a gaskiya, tambayar shi yay zai iya samo mashi lambar tashi da sauri Amadun yace eh yace Ok ya samo mashi harda ta shi wanda yake hayar gidan Amadun yace ita yana da ita yace to ya fara turo mashi ita kafin ya samo mashi ta mai gidan yace to zai tura mashi yanzu sukai sallama. Da yamma bayan sallar la'asar sai ga Baban su Umar yazo shagon Amadu cikin fara'a suka gaisa kafin cike da farinciki yake sanar dashi ɗazun mijin yar'uwar shi ya kira shi yake ce mashi yana buƙatar siyan gidan da yake ciki ne shine yace zai siya mashi gida da zai zauna har ma yace mashi ya nemi gidan da yake so in ya samu sai yayi mashi magana, sam Amadu bai kawo komai a
ranshi ba ya nuna ya taya shi murna sosae, Bayan sallar isha Tk ya samu Hajiya a parlonta daga gefenta ya zauna ya gaishe da ita tana murmushi ta amsa, shiru yay ya maida kan shi ƙasa yana wasa da yatsun hannunshi Hajiya ta lura da Magana yake son yi tace "Ya akai ɗan gidan Hajiyar Sanata mi ake son faɗi man ne?" ɗagowa yay yana murmushi ya kasa mata magana tace mashi ko sun fara yar kunya ne still murmushin yake bai ce mata komai ba tace kar yaji komai ya fadi mata abunda yake son fadi mata da ƙyar yana yar in ina yace dama so yake a je a nemo mashi Aure, ɗan buɗa ido tay tana kallonshi tace "Wato ashe dama kana da wadda kake so shine tuntuni kaƙi yin niyya sai yanzu da kaji abokin ka zaiyi kana gudun yayi ya barka ko" yana ɗan sosa kai yace a'a yaga bai fara aiki ba shiyasa bai yi niyya ba tace to yanzu aikin ya fara ne yay shiru yana murmushi,

"Ai ganin baka da niyya yasa banyi Maganar a nema maka aikin ba tunda mi zakai da aiki ba iyali amman yanzu tunda kayi niyya zanyi magana sai a nema maka sai kayi Addu'a Allah yasa a dace, Maganar zuwa nema maka aure kuma zan yi ma mahaifinka magana amman tukunna sai ansan wacece kake so tunda ba'a kama nema maka aure ba tare da anyi bincike ba" dakatawa tayi kafin ta tambaye shi sunan yarinyar da kuma yar gidan waye ya faɗi mata sunanta Asma'u tare suka yi karatu har ya kwantanta mata ita yace sun ta6a zuwa ta gaishe da ita Hajiyar tace ta ganeta yanzu zata sa ai bincike sosae kafin tayi ma Mahaifin nashi magana sai a turo mutum ɗaya ko biyu itama zata kira Kawu Mani sai su haɗu suje, Godiya yayi mata tare da Addu'o'i tana murmushi tace Allah ya nuna mata bikin Tukur ɗan autanta yana murmushi ƙasa ƙasa yace Amin kafin yayi mata sallama ya tafi.
Chapter 169 · 0% Book details