← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 82 OF 211

Sashe 82

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

90

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

..........Washe gari Fatuu na gama sallar Asuba ta tashi Mino suka fara shirin tafiya Makaranta, Mino ce ta shiga Kitchen don ta had'a masu breakfast ita kuma Fatuu ta shiga wanka, bayan ta fito ta fara shiryawa itama Mino ta shiga tayo wankan, anan ta shirya dama tun jiya da daddare taje gida ta d'aukko Uniform d'inta, saida suka gama shiryawa sannan suka yi Breakfast suna gamawa Fatuu ta kira Tk ta sanar dashi sun shirya yace to su fito, a cikin Motar ta suka tafi saida aka fara ajiye Mino kaman ko yaushe sannan aka wuce da Fatun, lokacin data je sosae yan class d'in su suka nuna murnar ganinta aka shiga zuwa yi mata sannu da dawowa da tambayar jikinta, bata dad'e da zuwa ba Fauzy ma ta zo. Bayan an tashi Tk yazo ya d'auketa suka biya suka d'auki Mino, a gida Mino tace a ajiye ta sukai sallama da Fatuu tace sai ta dawo islamiyya zata zo suka wuce, part d'in Hajiya ta nufa bayan sun isa gidan don wata irin yunwa take ji a haka ma wai taci Abinci sosae da break sannan gab da za'a tashi ma saida tasha youghort da cake da ta aje Saboda in taji yunwa, saida ta cika cikinta sannan ta koma part d'in su tana zuwa ko Uniform bata cire ba ta haye gado ta hau yin bacci, saida akai sallar la'asar sannan ta farka ta nufi toilet, wanka tayo ta dauro Alwala ta fara shiryawa cikin doguwar rigar Atamfa ta kabbara salla, bayan ta gama gaban mirror taje ta shafa yar powder da lip glow tana yi tana murmushi itama tana ganin canzawar da tayi sosae, gyale ta d'aukko ta yafa ta d'aukko jakar Makarantarta ta nufi part d'in Hajiya, lokacin data isa Hajiyar na zaune a parlon ta nufo ciki da sallama ta juyo tana amsa mata, kujera ta nufa ta zauna idon Hajiya a kanta ta gaishe da ita ta amsa kafin tace "an dawo" kai Fatuu ta d'aga "Eh tun d'azu nan ma na fara zuwa lokacin kina bacci naci Abinci sannan na tafi" kai ta jinjina mata, tana k'ok'arin fiddo littafi taji tace "Yanzun wannan rigar da kika saka baki ji kin takura ba, illar matsattsun kayan kenan dole wani lokacin kana ji kana gani baka iya saka su yanzun d'an nan gaba kad'an ya za'ai ki saka wannan rigar ai bata sanyuwa a wurin ki kinga da wadatattu ne ko yaushe zaki saka abun ki amman irin wad'annan kayan ko bayan kin haihu da k'yar in zasu yi maki don wani lokacin k'ibar ciki bin mutum take" shiru Fatuu tay idon ta akan littafin data fito tana d'an murmushi,

"Sauran kayan da ba'a d'inka ba ki bada ayo maki wadatattun dinkuna da ko cikin naki ya tsufa zaki iya sakawa" d'agowa tay ta kalleta ta d'aga mata kai, karatu ta fara yi ita kuma Hajiyar na kallo can tace mata ko akawo mata fruit zata shi ta d'aga mata kai, Saude ta fara k'wala ma kira jin shiru bata amsa ba tace k'ilan tana baya jin haka yasa Fatun mik'ewa tace bari taje ta d'aukko har zata fita daga wurin kujerun ta dakata ta tambayi Hajiyar itama ta kawo mata tace eh, a cikin bowls ta yayyanko ta dawo saida ta fara aje ma Hajiya nata akan c-table sannan ta koma ta zauna, kallon Fruit d'in Hajiya tay ganin harda abarba ta d'ago ta kalli Fatun tace badai itama harda abarbar ta yanko ba tace mata a'a ai tun Abuja bata shan ta ta jinjina kai, cigaba da karatun tayi ta haye saman kujerar gaba d'aya tana yi tana shan fruit d'in, suna haka suka ji an yi sallama alamar wani ya shigo, a Kusan tare suka kai idanun su saitin k'opar suna kallon wanda yay sallamar, nufo ciki yay saida ya matso sannan Fatuu ta gane ko waye har saida gabanta ya d'an fad'i ganin shi, Gaye ne yana sanye da riga da wando na yadi kan shi ba hula harda agogo sanye a hannun shi yana ruk'e da leda gari yayi zafi, da murmushi ya k'araso inda suke ganin yana k'ok'arin duk'awa k'asa yasa Hajiya nuna mashi kujera tace ya zauna mana, bayan ya zauna ya gaishe da ita fuskarta a sake ta amsa ya juya suka had'a ido da Fatuu still da murmushi a fuskar shi itama ya gaishe da ita ta amsa a hankali tana d'an murmushi, hakanan taji wani iri ganin shi a parlon duk da suna had'uwa a hanya a haka ma don bata san da Hajiya tasan abunda ya ta6a faruwa tsakanin su ba,

"kwana biyu Malam Ashiru ka daina lek'owa mu gaisa Allah yasa lafiya" Hajiya ta fad'a idon ta a kanshi yanata murmushi yace mata lafiya lou tace ma sha Allah, Fatuu dai sai kallon shi take abubuwa na dawo mata, mik'ewa yay ya matsa gaban Hajiya ya aje ledar daya shigo da ita ya koma ya zauna, kallon leda d'in tay ta ce "To, mi na samu haka" ta d'ago ta kalle shi yana murmushi yace mata yaje Jos ne kafin ya tafi ma yazo bata nan, jinjina kai tay tace sun je Abuja ne yace eh haka aka fad'a mashi,

"kace tsaraba ce aka kawo man kenan" yace eh, godiya tay mashi ta tambayi ya ya baro Mutan Jos d'in yace duk suna lafiya, shiru suka d'an yi can ta tambayi ya aiki da yake ta sa an samu mashi aiki yana teaching a primary, amsa mata yay da Alhamdulillah

"Yanzu sai aure ko tunda kana sana'a ga kuma aiki ai lafiya lou zaka iya rik'e iyali" yana murmushi cikin girmamawa yace mata sai nan gaba dai,

"To Saboda mi, ai aure shine cika kamalar mutum ko baka son yin Auren ne?" da sauri ya girgiza mata kai yana yar dariya yace ba wadda yake tare da ita ne yan mata basu son malamin Makaranta, har saida Fatuu tay yar dariya Hajiya tace "to don me, aikuwa inda wanda yakamata aso to bayan malami ne tunda ai shine tushen kowane aiki ko, kawai dai ba'a basu k'arfin da Yakamata bane wannan kuma saidai aita Addu'a Allah ya kawo Shuwagabannin da zasu duba masu, in dai mutum zai rik'e ka ya tsare maka hakkokin ka ai kuwa ba abun gudu bane kwanciyar hankali shi ne abun buk'ata a gidan aure kuma ba Arzik'i ne ke samar da wannan ba, gaba d'aya Arzik'in ma ai na Allah ne in akai hak'uri sai akai matakin da ba'a ma ta6a zato ba ga misalai nan akan masu Arzik'in, da yawa in kaji ta yadda suka faru sai ka jijjina kai don mamaki rabon mutum ai baya ta6a wuce shi" gaba d'aya sun yi shiru suna saurarenta har ta gama duk suka jinjina kai, jin ta gama Magana yasa shi kallon Fatuu yana murmushi yay mata Allah yasa Alkhairin Auren ta tana murmushi tay mashi godiya,

"In kana son yin Auren akwae yarinyar da zan had'a ka da ita bata da matsala akwai kyaun hali sai kaje in Allah yasa kun daidaita to sai muyi Addu'ar Allah yasa ayi damu" jinjina kai yay ta kai hannu gefenta ta d'aukko wayarta ta fara latsawa, alamun ya taso tayi mashi ya matsa daga gefen ta, mik'a mashi wayarta tayi tace ga Lambar yarinyar nan ya d'auka ranar da ya shirya zuwa su gana ya fara kiranta ya sanar mata yace to, bayan ya d'auka ya bata wayar cikin girmamawa yay mata sallama tace ya gaida Maman shi Allah yasa kuma su ji Alkhairi a kunyance ya amsa ya juya kan Fatuu dake cigaba da shan fruit idon ta akan shi itama yay mata sallama ya tafi ta bishi da ido gaba d'aya mamakin shi take sai ka rantse da Allah ba Gaye bane don sosae ya canza yay fresh hatta Maganar shi ma ta canza a nutse yake yin ta gashi kuma sam ba mummuna bane kuma yana da haske ashe dama can harda shaye shaye suka k'ara mashi bak'i. Bayan sallar Magrib Mino tazo har lokacin Fatuu na a part d'in Hajiya a d'akin Saude ta isketa lokacin bata dad'e da gama yin salla ba, suna anan d'akin aka yi sallar isha bayan Fatuu ta gama tace mata suje Parlor yunwa take ji, saida taje Kitchen ta zubo Abincin harda Mino sannan suka nufi cikin parlor don yanzu bata jin dad'in cin Abinci akan dining table, akan carpet suka zauna basu dad'e da fara ci ba Hajiya ta fito, bayan ta zauna Fatuu tace mata ta zubo mata Abincin ne tace a'a taci gaba da cin Abincinta in Saude ta zo ta zubo mata, bada jimawa ba Sauden ta shigo part d'in ta baya ta nufo cikin parlon, daga gefen Hajiya ta duk'a suka gaisa harda Mino kafin ta tambayi Hajiya a shirya table tace mata a'a waye mai ci a table d'in itama ta kawo mata nan tace to, bayan sun gama Mino ce ta kwashe kayan da sukai amfani dashi ta kai Kitchen ita kuma Hajiya tana cikin cin nata, suna Zaune suna yin kallo Tk ya shigo ta baya zai d'auki Abincin shi hango su da yay a zaune yasa shi nufo cikin parlon, daga bakin kujerun ya tsaya ya d'an rankwafa yana gaishe da Hajiya data juya tana kallon shi ta amsa Mino ma ta gaishe da shi,

"Tk yaushe zaka fara koya man Motan?" har zai juya Maganar Fatuu ta dakatar da shi kafin ya bata amsa Hajiya ta tambayi waye za'a koya ma Mota ne Fatuu tace mata ita, wani kallo ta bita dashi kafin tace "kaman dole, kina a cikin wannan halin za'a koya maki wata Mota, in kinyi hakuri Allah ya sauke ki lafiya ba sai a koya maki ba" yamutsa fuska Fatuu ta fara yi tace in aka koya mata yanzu lokacin tasan ta k'ware,
Chapter 82 · 0% Book details