Sashe 195
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Saida ta gama Magana ta fahimci gaba ɗaya kuka suke jin sheshshekarsu tay shiru tana kallon su dama itama ƙarfin hali kawai take, bayan wani lokaci tace "To duk kun tasani a gaba kunata kuka ko nima so kuke ɗan ƙarfin halin da nike in karaya in sa kukan ne?" a tare suka haɗa baki cikin muryar kuka suka ce "a'a......" tace to su daina suyi haƙuri don Allah tun farko tasan dama dole suji ba daɗi to amman sai ayi haƙuri wataƙil dama Allah ya ƙaddaro zamanta Abujan ne tunda tuntuni suke son ta koma taƙi hardai yanzu sukai galabar sata ta koma suyi haƙuri ai ba'a rabu ba kenan kamata yay ma su gode ma Allah daya sa ta miƙe, nasiha sosae tayi masu suna ta sharar ƙwalla daga ƙarshe tace suje, har zasu miƙe tace to su basu yafe matan ba wannan magana ba ƙaramin ta6a masu zuciya tayi ba duk suka ce mata su wllh ba abunda ta ta6a yi masu ba daidai ba tace duk da haka dai su yafe mata, a tare suka haɗa baki suka ce sun yafe mata tare da yi mata Addu'o'i, bin su tayi da ido lokacin da suka nufi ƙopa, bayan fitar su ta maido idonta tana kallon gabanta can ta sa hannu ta ɗaga gilashin idanunta ta goge ƙwallan da suka gangaro mata...........
104
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
.........Suna fitowa Tk ya wuce ɗakin su Saude kuma ta nufi baya inda ɗakinta yake, a bakin gado ya zauna yaci gaba da yin kukan mai cin rai yana haka Husnah ta shigo ciki ma gareta har ya girma, zama tayi a kusa dashi fuskarta ɗauke da damuwa ta shiga bashi haƙuri kai kawai yake ɗaga mata, da yake tasan wurin Hajiya suka je cike da damuwa ta tambayeshi tafiyar dai zata yi da gaske ya ɗaga mata kai alamar eh ta ɗan girgiza kai itama duk wani iri take ji can ta kai hannu ta fara goge mashi ƙwallan tana bashi haƙuri, Saude ma tana komawa ɗakinta ta faɗa gado ta saka kuka mai sauti gwanin ban tausayi, ta ɗan ɗauki lokaci kafin Officer ya shigo ya isketa a haka, da alamun tashin hankali ya nufi bakin gadon ya zauna ya kai hannu yana ta6ata tare da kiran sunanta yana tambayarta lafiya miya faru, cikin kuka tace mashi da gaske Hajiya tafiya zata yi, cikin sanyin jiki yace mata eh yasani nan da sati guda ya shiga bata haƙuri yana nuna mata ai ba an rabu ba kenan za'a cigaba da zumunci yanzu ma daga wurinta yake tace ma zasu iya cigaba da zama a gidan, haƙuri yaci gaba da bata can ta ɗago idanunta sunyi jajir ta saukko daga saman gadon a tunanin shi wani wuri zata ko toilet kawai sai gani yay ta duƙa a gabanshi cikin kuka a marairaice tace mashi don Allah tana neman alfarma a wurin shi tana rokon ya dubi girman Allah yayi mata, gaban shi ne ya fara faɗuwa yace mata in sha Allah in bata fi ƙarfin shi ba zai yi mata, a marairaice tace mashi tunda dama a nan gidan suka haɗu har sukai aure kuma Allah bai sa sun samu rabon haihuwa ba don Allah tana roƙon shi ya sawaƙe mata Allah ne shaidarta tana jin Hajiya har cikin ranta bata jin zata iya cigaba da zama a gidan nan ba tare da ita ba, shiru yay yana kallonta duk da yaji ba daɗi data yi Maganar amman ta bashi tausayi yace mata yanzu in ya sawaƙe matan garinsu zata koma kenan tace a'a zata roƙi Hajiyar ne ta tafi da ita, shiru yay yana kallonta ta langa6ar da kai tana mashi magiya can yay yar ajiyar zuciya yace mata shikenan ta bari sai da safe zasu yi Maganar tunda yanzu dare yayi ya kama hannunta ya miƙar da ita yace suje ta wanke fuskarta. A wannan daren baccin su gaba ɗaya harda Tk ragagge ne, Washe gari Officer na dawowa daga sallar Asuba part ɗin Hajiya ya wuce, bayan ya ƙwankwasa ƙopar daga ciki ya jiyo muryarta tana bashi izinin ya shigo, zaune take kan darduma hannunta ruƙe da cazbaha, da hannu tayi mashi alamar ya shigo ya nufi inda take ya duƙa a kan carpet, bayan ta shafa Addu'a ta kalleshi da ɗan murmushi da sauri ya gaishe da ita ta amsa tayi mashi ya suka tashi ya amsa da Alhamdulillah daga haka yay shiru idon shi akan carpet, daga yanayin shi ta fahimci da wani abu tana ɗan murmushi tace mashi tana fatan dai lafiya ko da wani abu, dagowa yay a nutse yace mata dama Saudatu ce jiya da daddare ta roƙeshi kan yay mata wata alfarma to yace ta bari sai zuwa da safe shine yaga ya dace ya fara tuntu6arta gudun yay mata ba daidai ba, kai Hajiya ta jinjina ta tambayi wace alfarma take son ya yi mata ne nan ya faɗi mata duk yadda sukai da Sauden,
"Humm, Saudatu Kenan, to yanzu kai ka amince zaka sawaƙe matan ne?" Hajiya ta faɗa tana ɗan murmushi idonta akan shi, ɗan shiru yay farko kafin yace tunda ta nuna hakan take so zai mata Hajiyar tace bai son auren ne ko kuwa, da sauri da alamun damuwa yace wllh yana son zamanshi da ita Allah ya sani kawai dai ya fahimci in bai yi mata yadda take so ba ba lalle zaman nasu yaci gaba da yin daɗi ba don ta nuna bazata iya cigaba da zama ba tare da ita ba, yar ajiyar zuciya Hajiya ta sauke ta juya ta kai hannu ta ɗaukko wayarta ta shiga kiran layin Saude bayan ta ɗaga tace mata tazo dakinta tana son ganinta, ba'a ɗau lokaci ba Sauden ta shigo cikin ɗakin da sallama tana sanye da doguwar Hijabi duk suka amsa mata ta nufo ciki, gefen Officer Hajiya ta nuna mata alamar ta zauna, bayan ta zauna ta gaishe da Hajiyar tare da yi mata an tashi lafiya da tambayar ƙarfin jikinta duk ta amsa mata daga haka Sauden ta sunkuyar da kanta idon Hajiya a kanta tana ɗan murmushi, a nutse cikin dattako ta fara magana tace taji yadda sukai da maigidanta saidai sam bata jin daɗin jin hakan ya fito daga bakinta ba a matsayinta na wadda take gani mai hankali taya zata tunkari mijinta da zancen ya saketa kenan ta za6i bauta a ƙarƙashin wani fiye da ubangijinta, da sauri ta girgiza mata kai alamar a'a,
"Aure shine mutuncin kowace mace Saudatu, nasan saboda kauna da sabo yasa kika za6i hakan saidai ni a wurina zaman ki a ɗakin mijinki shine abun alfaharina ba kamar in na tuna a gidana kuka haɗu har akai auren, kiyi haƙuri don na tafi ba yana nufin shikenan an rabu ba in sha Allahu za'a cigaba da yin zumunci in dai da rayuwar" ɗagowa Sauden tayi idanunta sharkaf da ƙwalla ta ɗaga mata kai kafin cikin disashshiyar murya tace mata to zata koma Daura,
"To auren fa Saudatu, taya zaki koma can bacin ga mijin ki anan?", shiru ta ɗan yi idonta a ƙasa kafin tace "Hajiya don Allah ki bari in koma Allah ne shaidata bazan iya cigaba da zama ba a gidan nan in baki nan" shiru Hajiya tayi tana ɗan murmushi idonta a kan ta, cikin sigar rarrashi tace mata ta dai yi haƙuri ta zauna saboda aurenta Sauden tayi shiru tana matsar kwalla can Officer yace in hakan take so lafiya lou shi ya amince ta koma Daura din Hajiya tace to ya za'ai hakan yace ba komai indai hankalinta zai fi kwanciya sai ya rinƙa zuwa, ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tace shikenan bari ta gani in zata iya neman alfarma sai a maida shi Daura da aiki dama tuntuni abunda yasa ya daɗe anan gidan ita ta roƙi alfarmar abar mata shi yanzu abunda za'ayi tunda dama zata siya ma Sauden gida in ta amince sai a siya mata acan Daurar sai su zauna a cikin shi, da sauri Sauden ta ɗaga kai alamar ta amince Hajiyar tayi murmushi tace to wurin ina take son a siya mata gidan tasa a bincika mata Sauden ta ɗago ta faɗi mata tace shikenan, kallon Officer tay tace ya jirata Maganar canjin wurin aiki ya yi kuma Addu'a Allah yasa a maida shi can yace Amin ta ƙara ce mashi zata turo mashi saƙon kuɗi sai ya juya ya haɗa da aikin nashi Allah ya ƙara rufa asiri ya amsa da Amin tare da yi mata godiya da addu'o'i ta amsa tare da cewa shikenan zasu iya tafiya.
104
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
.........Suna fitowa Tk ya wuce ɗakin su Saude kuma ta nufi baya inda ɗakinta yake, a bakin gado ya zauna yaci gaba da yin kukan mai cin rai yana haka Husnah ta shigo ciki ma gareta har ya girma, zama tayi a kusa dashi fuskarta ɗauke da damuwa ta shiga bashi haƙuri kai kawai yake ɗaga mata, da yake tasan wurin Hajiya suka je cike da damuwa ta tambayeshi tafiyar dai zata yi da gaske ya ɗaga mata kai alamar eh ta ɗan girgiza kai itama duk wani iri take ji can ta kai hannu ta fara goge mashi ƙwallan tana bashi haƙuri, Saude ma tana komawa ɗakinta ta faɗa gado ta saka kuka mai sauti gwanin ban tausayi, ta ɗan ɗauki lokaci kafin Officer ya shigo ya isketa a haka, da alamun tashin hankali ya nufi bakin gadon ya zauna ya kai hannu yana ta6ata tare da kiran sunanta yana tambayarta lafiya miya faru, cikin kuka tace mashi da gaske Hajiya tafiya zata yi, cikin sanyin jiki yace mata eh yasani nan da sati guda ya shiga bata haƙuri yana nuna mata ai ba an rabu ba kenan za'a cigaba da zumunci yanzu ma daga wurinta yake tace ma zasu iya cigaba da zama a gidan, haƙuri yaci gaba da bata can ta ɗago idanunta sunyi jajir ta saukko daga saman gadon a tunanin shi wani wuri zata ko toilet kawai sai gani yay ta duƙa a gabanshi cikin kuka a marairaice tace mashi don Allah tana neman alfarma a wurin shi tana rokon ya dubi girman Allah yayi mata, gaban shi ne ya fara faɗuwa yace mata in sha Allah in bata fi ƙarfin shi ba zai yi mata, a marairaice tace mashi tunda dama a nan gidan suka haɗu har sukai aure kuma Allah bai sa sun samu rabon haihuwa ba don Allah tana roƙon shi ya sawaƙe mata Allah ne shaidarta tana jin Hajiya har cikin ranta bata jin zata iya cigaba da zama a gidan nan ba tare da ita ba, shiru yay yana kallonta duk da yaji ba daɗi data yi Maganar amman ta bashi tausayi yace mata yanzu in ya sawaƙe matan garinsu zata koma kenan tace a'a zata roƙi Hajiyar ne ta tafi da ita, shiru yay yana kallonta ta langa6ar da kai tana mashi magiya can yay yar ajiyar zuciya yace mata shikenan ta bari sai da safe zasu yi Maganar tunda yanzu dare yayi ya kama hannunta ya miƙar da ita yace suje ta wanke fuskarta. A wannan daren baccin su gaba ɗaya harda Tk ragagge ne, Washe gari Officer na dawowa daga sallar Asuba part ɗin Hajiya ya wuce, bayan ya ƙwankwasa ƙopar daga ciki ya jiyo muryarta tana bashi izinin ya shigo, zaune take kan darduma hannunta ruƙe da cazbaha, da hannu tayi mashi alamar ya shigo ya nufi inda take ya duƙa a kan carpet, bayan ta shafa Addu'a ta kalleshi da ɗan murmushi da sauri ya gaishe da ita ta amsa tayi mashi ya suka tashi ya amsa da Alhamdulillah daga haka yay shiru idon shi akan carpet, daga yanayin shi ta fahimci da wani abu tana ɗan murmushi tace mashi tana fatan dai lafiya ko da wani abu, dagowa yay a nutse yace mata dama Saudatu ce jiya da daddare ta roƙeshi kan yay mata wata alfarma to yace ta bari sai zuwa da safe shine yaga ya dace ya fara tuntu6arta gudun yay mata ba daidai ba, kai Hajiya ta jinjina ta tambayi wace alfarma take son ya yi mata ne nan ya faɗi mata duk yadda sukai da Sauden,
"Humm, Saudatu Kenan, to yanzu kai ka amince zaka sawaƙe matan ne?" Hajiya ta faɗa tana ɗan murmushi idonta akan shi, ɗan shiru yay farko kafin yace tunda ta nuna hakan take so zai mata Hajiyar tace bai son auren ne ko kuwa, da sauri da alamun damuwa yace wllh yana son zamanshi da ita Allah ya sani kawai dai ya fahimci in bai yi mata yadda take so ba ba lalle zaman nasu yaci gaba da yin daɗi ba don ta nuna bazata iya cigaba da zama ba tare da ita ba, yar ajiyar zuciya Hajiya ta sauke ta juya ta kai hannu ta ɗaukko wayarta ta shiga kiran layin Saude bayan ta ɗaga tace mata tazo dakinta tana son ganinta, ba'a ɗau lokaci ba Sauden ta shigo cikin ɗakin da sallama tana sanye da doguwar Hijabi duk suka amsa mata ta nufo ciki, gefen Officer Hajiya ta nuna mata alamar ta zauna, bayan ta zauna ta gaishe da Hajiyar tare da yi mata an tashi lafiya da tambayar ƙarfin jikinta duk ta amsa mata daga haka Sauden ta sunkuyar da kanta idon Hajiya a kanta tana ɗan murmushi, a nutse cikin dattako ta fara magana tace taji yadda sukai da maigidanta saidai sam bata jin daɗin jin hakan ya fito daga bakinta ba a matsayinta na wadda take gani mai hankali taya zata tunkari mijinta da zancen ya saketa kenan ta za6i bauta a ƙarƙashin wani fiye da ubangijinta, da sauri ta girgiza mata kai alamar a'a,
"Aure shine mutuncin kowace mace Saudatu, nasan saboda kauna da sabo yasa kika za6i hakan saidai ni a wurina zaman ki a ɗakin mijinki shine abun alfaharina ba kamar in na tuna a gidana kuka haɗu har akai auren, kiyi haƙuri don na tafi ba yana nufin shikenan an rabu ba in sha Allahu za'a cigaba da yin zumunci in dai da rayuwar" ɗagowa Sauden tayi idanunta sharkaf da ƙwalla ta ɗaga mata kai kafin cikin disashshiyar murya tace mata to zata koma Daura,
"To auren fa Saudatu, taya zaki koma can bacin ga mijin ki anan?", shiru ta ɗan yi idonta a ƙasa kafin tace "Hajiya don Allah ki bari in koma Allah ne shaidata bazan iya cigaba da zama ba a gidan nan in baki nan" shiru Hajiya tayi tana ɗan murmushi idonta a kan ta, cikin sigar rarrashi tace mata ta dai yi haƙuri ta zauna saboda aurenta Sauden tayi shiru tana matsar kwalla can Officer yace in hakan take so lafiya lou shi ya amince ta koma Daura din Hajiya tace to ya za'ai hakan yace ba komai indai hankalinta zai fi kwanciya sai ya rinƙa zuwa, ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tace shikenan bari ta gani in zata iya neman alfarma sai a maida shi Daura da aiki dama tuntuni abunda yasa ya daɗe anan gidan ita ta roƙi alfarmar abar mata shi yanzu abunda za'ayi tunda dama zata siya ma Sauden gida in ta amince sai a siya mata acan Daurar sai su zauna a cikin shi, da sauri Sauden ta ɗaga kai alamar ta amince Hajiyar tayi murmushi tace to wurin ina take son a siya mata gidan tasa a bincika mata Sauden ta ɗago ta faɗi mata tace shikenan, kallon Officer tay tace ya jirata Maganar canjin wurin aiki ya yi kuma Addu'a Allah yasa a maida shi can yace Amin ta ƙara ce mashi zata turo mashi saƙon kuɗi sai ya juya ya haɗa da aikin nashi Allah ya ƙara rufa asiri ya amsa da Amin tare da yi mata godiya da addu'o'i ta amsa tare da cewa shikenan zasu iya tafiya.