← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 148 OF 211

Sashe 148

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Washegari bayan sun gama yin breakfast ita da Mino ta shirya suka tafi gidan gwaggo don anjima zasu tafi siyayyar kayan ɗakin Mino kamar yadda suka tsara jiya da gwaggon da har tace ta bari sai gobe lokacin ta ƙara huta gajiya Fatun tace a'a gara su tafi ayi komai a gama don bikin nata matsowa, bayan sallar azahar Aunty mareeya ta iso dama ita suke jira ruƙe da babban kwali Kawu Amadu da Kamalu sun kamo mata suka shigo, a falo suka zauna aka shiga gaisawa ta ƙara yi ma Fatuu sannu da zuwa dama jiya tayi mata a waya, sai gashi ita lafiya lou su twins sun yarda da ita ta ɗauke su harda Abie su gwaggo sukai ta mamaki Aunty Mareeyar na dariya tace ai ita dama da wuya yara suyi mata ƙyuya Mino tace kuma dama itama fara ce ƙilan shiyasa suka yarda da ita da mamaki Aunty mareeya ta waro ido tace tsoron baƙaƙe suke ne aka ce mata eh aikuwa ta ƙyalƙyace da dariya tace bata ga laifin su ba wake son baƙi duk akai dariya, bayan an gama gaishe gaishen Gwaggo tasa Mino ta zubo mata abinci da sauri ta dakatar da ita tace wllh a ƙoshe take don daga kan abinci ta taso Fatuu tace to ai dai ko lemu tasha tace to a bata, bayan ta gama sha ne ta buɗe jakar ta ta fiddo kuɗi bandir biyar, miƙewa tay ta matsa daga gefen gwaggo ta aje bayan ta dawo ta zauna tace gashi nan gudunmawarta ce ita da Fauzy ga kuma wasu kayan Kitchen nan a haɗa ayi mata amfani dasu, gaba ɗayan su waro ido sukai suna kallonta da tsananin mamaki gwaggo ta kama baki kafin tace "Ƴata wannan gudunmawa haka ai tayi yawa gaskiya" tana dariya tace a'a ba wani yawan da tayi in so samu ne ma ai tafi haka tunda duk hidimarsu ce, Fatuu na niyyar yin magana Aunty Mareeyar ta dakatar da ita harda zare mata ido duk ta basu dariya, godiya sosae Gwaggo ta shiga yi mata tana addu'ar Allah ya bar zumunci haka Fatuu ma, tambayar yanayin yadda za'a siya kayan ɗakin Aunty Mareeya tayi Fatuu ta faɗi mata kowanne set biyu tace hakan yayi amman fa za'a sha kuɗi gaskiya don kaya yanzu sai Addu'a ko dai a siya set ɗin kujeru ɗaya masu kyau sai ayi gado biyu gwaggo tace ita da cewa tayi ma a yi kowanne seti ɗaya Auntyn tace a'a ayi dai gadon biyu sai kujeru ɗaya sai sauran kayan Kitchen da electronics suma nan ba ƙaramin kuɗi za'a kashe ba ga kuma labulaye, tambayar Fatuu tayi tasan yanayin gidan da za'a kaita ne don asan yawan labulayen da za'a siya tace a'a gaskiya Aunty tace yakamata kuma a sani ko akwae wanda zata iya tambaya, shiru ta ɗan yi kafin tace gashi Jidderh bata nan itace zata iya tambaya lafiya lau Aunty Mareeya tace ko ta kira Laila sai ta nuna mata labulaye ne ake son yi ai ba wani abu bane tace to, bayan ta kira Laila ɗin sun gaisa tayi ma Fatun an zo lafiya ta amsa itama tayi mata ya shirye shiryen hidima Laila tace Alhamdulillah Fatuu tay fatan Allah ya nuna masu ta amsa da Amin, tambayarta tay kamar yadda Aunty Mareeya tace Laila ta bata amsa da gidan bene ne ta fasalta mata yadda tsarin gidan yake Fatuu tayi mata godiya har zasu yi sallama Laila ta dakatar da ita tace amman fa saman benen Nameer yasa mashi kaya kar suce zasu yi kaya harda nan kuma duka gidan ma an sa labulayen ƙasa da sama sai dai kawai in zasu ƙara mata ne Fatun na murmushin jin daɗi tace to tare da yin godiya, bayan sun gama yin wayar tayi ma su Gwaggo bayani gaba ɗaya suka washe bakin farinciki Aunty Mareeya tace yauwa sunga kujeru set ɗayan sun isa tace a bata takarda da biro suyi list ɗin abubuwan da za'a siyo yadda da sun je ba tare da 6ata lokaci ba su fara yin siyayyar Fatuu ta ƙwala ma Mino kira tace ta taho da paper da biro, tare suka shiga faɗin abubuwan da za'a siya tana rubutawa, bayan ta gama suka miƙe don tafiya dama Motar Fatuu na a ƙofar gida, su ukku suka fito Aunty Mareeya na ruƙe da Adam Fatuu kuma Abie aka bar Mino a gidan, bayan sun fito ne cike da farinciki gwaggo ta sanar ma Kawu Amadu gudunmawar su Aunty Mareeya shima sosae yaji daɗi yana ta faffaɗan murmushi ya shiga yi mata godiya tana faɗin haba ba komai ai an zama ɗaya. Lokacin da suka isa wurin siyayyar babban bene ne hawa ukku gaba ɗaya manyan show rooms ne a ciki shaƙe da ƙawatattun furniture da rantsattsun kayan adon gida na gani na faɗa, cikin haba haba mai wurin wadda babbar Hajiya ce da yaranta suka tarbe su tana ta washe masu baki harda yunƙurin ɗaukar su twins suka ƙi yarda, bayan sun gama gaisawa suka yi mata bayanin kaya suke so tace gasu nan sun zo gidan kaya masu kyau da Quality ta shiga nuna masu suna jinjina kai da yabawa don ba ƙarya akwae kaya a wurin Aunty Mareeya tace ai tasan suna da kaya masu kyau shiyasa tayo masu jagora Hajiyar ta shiga yi mata godiya, ba 6ata lokaci suka shiga za6a ba tare da wani yin ruwan ido ba don kowane kaya haɗaɗaɗun kan su ne, kamar yadda suka tsara gado biyu suka za6a sai set ɗin kujeru da labulaye harda Carpet da wasu kayan ƙawata falo da ɗaki harda kitchen da kuma wasu kayan Kitchen amman banda electronics don Fatuu tace su bari suje EE inda Haisam ke zuwa gym su siya acan don suna da sauƙin kaya, kaya masu sunan kaya suka zazza6a saidai an kashe kuɗi ba kaɗan ba, bayan sun gama siyayyar suka ce ma matar ba yanzu zasu tafi dasu ba in ba matsala a cikin satin nan da za'a shiga za'a zo a ɗauka da sauri tace lafiya lou ba damuwa da ta basu receipts shikenan za'a ware masu kayan yanzu, bayan sun biya ta basu shaidar siyayyar harda ba Aunty Mareeya tukuici tana dariyar jin daɗi tayi mata godiya itama tayi masu godiyar harda cewa tana fatan suma zasu kawo mata customers suka ce in sha Allah tunda ta duba masu, bayan sun bar nan wurin siyan electronics suka wuce nan ma suka siya kayan kallo da fridge, Electric cooker harda injin wanki da sauran su, saida suka siya komai da suke buƙata sai abunda ya rage wanda sai sunje kasuwa zasu siya harda kayan gara dana abincin da za'a ci da biki, a gida suka sauke Aunty Mareeya suna ta mata godiya tana faɗin haba ba komai ta tambayi lokacin da zasu je Kasuwar Gwaggo tace ita ta fidda lokacin da take da halin zuwa, a daren ranar bayan isha Kawu Amadu ya shigo bayan ya dawo daga Masallaci nan suka shiga tattaunawa kan gyaran da za'a ma gidan Fatuu tace da da hali ma da sababbin furniture aka saka gwaggo tace a'a a gyara su kawai hidiman da yawa don ma an samu gudunmawa sosae an gode ma Allah suma kuma sunyi ƙokari ita da Kawu Amadu haka suma iyayen su Baffa da Yadikko tace ba ƙaramin ƙokari sukai ba sun bada kuɗi da yawa, suna murmushi itama gwaggon suka yaba mata tayi murmushi tare da fatan Allah ya nuna masu bikin lafiya duk suka amsa.
Chapter 148 · 0% Book details