← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 209 OF 211

Sashe 209

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Saboda aikin da aka mata yasa aka ɗaga yin taron suna sai bayan sati biyu ita Fanan ɗin ma cewa tayi a bar taron ba sai anyi ba amman kowa ya nuna yana so, gaba ɗaya satin Fatuu bata samu komawa Zaria ba tana gida sunata zaman jego sai ranar lahadi ta tafi, hidima ba yar kaɗan ba Hajiya Maryam tayi ma jaririn don shima saida tayi mashi dozin ɗin akwatunan kaya sannan tayi ma Fanan kayan fitar suna ciki harda wata danƙareriyar sarƙar zinari ta miliyoyin kuɗi hatta Haisam da Fatuu ma saida tayi masu kayan fitar suna haka su twins ma tayi masu kayan fitar sunan sannan kowannen su ta siya mashi abunda yace yana so a Asibiti hatta Abie ta siyo mashi robobin ba yaro ruwa masu tsananin kyau yan ƙasar waje da zasu kai goma sannan Fatuu ma tasa an kawo mata Motar data bata itama mai jegon ta canza mata tsadaddiyar Mota, kowa yaji daɗin abunda tayi duk da haka kuma Haisam ma saida yayi masu kayan fitar sunan shima, waɗannan kayan fitar sunan dai ban tunanin za'a iya saka su gaba ɗaya ranar sunan don sunyi masu yawa, Ranar Alhamis Fatuu ta dawo nan suka shiga hidiman sunan da za'a yi ran Asabar a maimakon ranar litinin saboda ranar ta kama ta aiki duk mutane suna zuwa wurin aiki, Washe gari Juma'a su Gwaggo suka iso da Haulat da Husnah harda Aunty Mareeya da Feenah sosae Fanan da Fatuu suka ji daɗin zuwan nasu, a daren ranar sunan aka kira Haisam a waya cewa saƙon shanu daga Yola ya iso wanda Baffan Fatuu ne ya aiko mashi dashi a yanka ma yaro, har Fatuu bata san da aiken ba saida Haisam ya kirata a waya ya sanar mata aiko taji daɗin hakan da yayi sosae, Alhamdulillah Allah ya kawo mu ranar suna hidima ta kankama ba kama hannun yaro, a ranar da safe sai ga su Yadikko da Yaya da Mairo sun iso harda dawon furarsu mai uban yawa da kuma Nono sai zuma da ƙwai masu yawan gaske, zo kaga murna wurin su Aysha da Mino anga Mahaifiya, bayan sallar azahar gida ya fara cika da yan suna mai jego da Fatuu da kuma yaransu suna ta cin uban gayu, zuwa sallar la'asar taro yayi taro malam hidima data amsa hidiman manyan masu kuɗi ake har bansan ma ta yadda zan bayyana yadda hidiman ke wakana ba don abun na neman fin ƙarfin al'ƙalamina kawai sai na koma yar kallo, ina cikin kallon manyan Hajiyoyin Abuja dake ta zuwa kwatsam sai ga Hajiya Kubra wato Momy ta iso a Motarta harda iyalanta suma sun zo suna, ina hangota cikin Washe baki na nufeta muka gaisa nace ashe zata zo sunan cikin fara'ar ta tace man ai ita tana yin Fanan sosae dama tana cikin wanda suka damu da halin rashin haihuwarta lokacin data ji labarin haihuwar sosae tayi farinciki ta kuma yi godiya ga Allah dama ance shi maharƙuci tabbas mawadaci ne nace wannan gaskiya ne Momy Allah ya ƙara mana haƙuri da kuma dangana ta amsa da Amin kafin suka shiga ciki ni kuma naci gaba da baza idanu ina ganin danƙara ɗanƙaran, jibga jibgan Motoci masu numfashi dake ta sawo kai cikin harabar yayin da wasu kuma ke tafiya, a taƙaice dai Abuja ce ta haɗu a gidan Haisam don First lady na nan da sauran matan muƙarraban shugaban ƙasa. Alhamdulillah taro ya tashi lafiya yaro yaci sunan Haisam suna ce mashi Junior, an ci an sha anyi wadaƙa da nishaɗi sannan an raba kayan suna masu ɗauke da sunan Baby kawai ba'a saka hoton shi ba, a bangaren maijego Fanan ta samu kayan suna kai kace zata buɗe ƙaton shago ne ita kanta saida tayi mamakin kayan da aka tara mata, a daren ranar su Fatuu da Farha harda Aunty Mareeya suka shirya kayan kafin su kwanta, Washe gari Lahadi yan Katsina da Yola suka koma duk an cikasu da abubuwan arzuƙi, haka sauran yan'uwan su Haisam yan Katsina da Daura da suka sauka a Villa duk suma sun tafi, Fatuu ma taso tafiya Zaria a ranar saidai da sauran abubuwan da zatayi a gidan dole ta bari sai gobe da sassafe sai ta koma, kusan raba kayan da Fanan ta samu nata tayi taba Fatuu duk yadda taso taƙi kar6a Fanan ɗin ta kafe, har rage kayan tayi ta maida mata wasu amman taƙi kar6a ƙarshe ma sai ta nuna mata 6acin ranta sosae hakan yasa dole ta amsa tayi mata godiya da kuma Addu'oi.

*BAYAN SHEKARU BIYAR*

Abubuwa da yawa sun faru a cikin waɗannan shekarun daga ciki abu na farko daya faru shine saukar President Ali Adamu daga kujerar mulki tuni kuma wata sabuwar gwamnatin ta hau, a lokacin daya sauka al'umma sunyi kukan rashin jajirtacce kuma nagartaccen shugaban ƙasa, bayan saukar shi Katsina suka koma da zama a gidansu dake G.r.a a lokacin tsohuwa mai ran ƙarfe wato Hajiyar sanata ta koma gidanta da zama saidai bana dundun dundun bane zo kaga murna a wurin yan unguwa karma Tk yaji, Saude da har zata dawo Hajiyar ta hana tace ai ba daɗewa zatayi ba tunda ga matar tukur nan lafiya lou tayi zamanta a ɗakin mijinta, shekara guda sukai a Katsina kafin suka koma Abuja.

Bayan saukar shi da shekara ɗaya Fatuu kuma ta gama karatunta cikin nasara har ta fara aiki bayan shekaru biyu da fara yin aikin nata ne ta ƙara haihuwar yan biyu duk mata an saka masu Khadija da kuma Fateema wato sunan Gwaggo da kuma Mom ɗin su Haisam, Esha tayi murna kamar kamar me da samun ƙanne mata, a lokacin wasu sun ƙara haihu wasu kuma nada ciki, a cikin wanda suka ƙara haihuwa harda Jidderh da kuma Fauzy ta ƙara haihuwar Namiji an saka mashi sunan mahaifin Sameer wato Bello, Aysha ma ƙanwar Mino a lokacin tayi haihuwarta ta farko ta haiho Baby girl an saka mata sunan Yadikko wato Jameela, Mino dai har lokacin bata ƙara haihuwa ba don tace ba yanzu ba bata manta kwakwar data ci ba ansamu dai ta amince zata ƙara yaronta yanzu shekararshi shidda, Farha ma ta ƙara haiho Namiji an saka mashi sunan Mahaifinsu wato Muhammad, Haulat ma ta ƙara haihuwar Namiji an saka mashi sunan mahaifinta wato ishaq, a bangaren Fanan kuwa ita bata ƙara samun cikin ba tun bayan Haisam Junior wanda yanzu shekararshi biyar da yan watanni, duk a cikin lokacin akai ma wasu aure ciki harda Yasmeen ƙanwarsu Haisam ta auri yaron Yayan Mahaifiyarta na Qatar mai suna Abdurrahman suna zaune a can ƙasar haka ƙanin Sameer wato Ashraf shi kuma ya auri Jahad itama ɗiyar yayansu ɗin na Qatar suna a Abuja zaune burin su Mom ya cika na son haɗa yaransu auren zumunci.
Chapter 209 · 0% Book details