Sashe 129
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Washe gari Friday ya kama saura sati biyu cuf d'aurin auren Fauzy da Sameer, a ranar ne aka tura wasu daga cikin akwatunan lefen Fauzy set biyu guda goma cuf wai nan kayan da zata ci biki ne sauran sai an kaita kamar dai yadda Hajiya Zainab ta fad'a ma Aunty Mareeya harda invitation cards masu kyaun gaske aka had'o, akwatuna ne ubansu su kan su abun kallo ne kai da gani ba sai an fad'a maka ba kasan zasu yi kud'i saima da aka bud'e kayan ciki Naira ta sha kashin gaske don kaya ne na gani na fad'a kuma duk a d'inke suke a ciki harda wanda Fauzy ta saka suka yi hotuna, kowa ya gani cikin yan uwansu cewa yake yo iya wannan ma ai lefe ne na gaske, lokacin da aka tura ma su Aunty Mareeya kayan zo kaga murna ita kanta fad'i take yanzun duk wannan uban kayan har sai an k'ara wasu, itama Fauzy har ta kasa rufe bakinta don farinciki koda ta tura ma Fatuu ita kanta ta yaba sosae anan take tambayarta sai yaushe zata tafi Funtua d'in ne tace mata sai zuwa jibi Lahadi akwae shirye shiryen da Aunty take son k'arasawa, itama Fauzy ta tambayi Fatun sai yaushe zata je can tace mata sai satin bikin ana saura kwana biyu aikuwa Fauzy tace ita dai bata yarda ba gaskiya inama laifin ana saura sati d'aya ta taho, dariya Fatuu ta saka tace wannan sai kace ita ce dai Amaryar inama laifin ana saura kwana biyun Fauzy ta kafe kan ita dai yayi kad'an Fatun tace mata gaskiya daga haka bazata k'ara ba don Lokacin Hubby dinta ya dawo taya zata taho ta barshi, dariya Fauzy ta saka tace ai sai ta fito tayi mata bayani ba taita yan kame kame ba duk suka yi Dariya. Ranar Lahadi tunda safe su Aunty suka d'auki hanyar Funtua a cikin Motar Fauzy driver d'in da ya koya mata Motar ne zai kai su. Alhamdulillah sun isa lafiya anata murnar ganin su ba kamar Fauzy Amarya sai faman nan nan da ita ake, sosae sukai mamakin yadda aka canza ma gidansu fasali duk da sun gani a waya amman yanzu da suka ganshi a zahiri sai suka fi ganin kyaun shi ya zama gidan yan gayu sosae wanda kaf layin su da duk ma rukunin su ba gida tamkar shi kai a yanzu ma yana d'aya daga cikin jerin gidaje masu kyau in za'a lissafa a garin, shirye shiryen hidima sun kan kama sosae bayan zuwan nasu duk da ba wani abu da Fauzyn zata yi anan Funtua Sameer har magana yayi mata kan ko zasu yi wani event tace mashi a'a abar wanda su zasu yi kawai wato Dinner bayan an kaita sai kuma Walima wadda za'a yi matsayin bud'ar kai. Ranar Laraba Haisam ya iso yana dawowa washe gari suka tafi Abuja da Fatuu harda Hajiya acan ma dai duk shirye shiryen bikin aketa yi, Ana saura kwana biyu bikin ya kama ranar laraba kamar yadda Fatuu tace Haisam yasa driver ya tafi da ita harda Jidderh, Bayan sun isa Fauzy tayi murna da ganin su sosae haka Aunty Mareeya da sauran yan gidan sai faman nan nan ake da su anata nuna Fatuu ana cewa itace k'awar Fauzy wadda zata auri d'an uwan mijinta nan fa akai ta yi ma Fatuu godiya hatta Mahaifinsu da kanshi yazo inda suke yay masu sannu da zuwa shima saida yayi mata godiya da Addu'ar Allah ya bar zumunci haka yayye da k'annen Fauzy duk saida suka zo suka gaishe da ita hadda Yaya Mubarak ma fuska a sake Fatuu ke amsa masu ana ta son a d'auki twins amman sun ki yarda sai faman fad'in Tubarkallah ake dama lokacin sun k'ara girma sosae, Yaya Fareeda harda cewa Allah yasa Fauzy itama ta haifi irin su anata dariya aka amsa da Amin. Hidima ta kan kama tun a ranar Jami'an tsaro keta faman sunturi a cikin garin ana ankarar da mutane hatta gidan su Fauzy an zuba security, Washe gari Alhamis su gwaggo suka iso tare da Kawu Amadu da Mino harda Haulat da Saude bayan zuwan su kuma su Zainab Muhammadu da wasu daga cikin k'awayen su ma suka zo haka makwabtan Aunty Mareeya ma su Maman taufiq suma sunzo gida dai ya cika sai zuwa ake.
FRIDAY....
Alhamdulillah Allah ya kawo mu ranar d'aurin aure, a ranar tunda farar safiya jiniya ta fara tashi ta ko ina wurin k'arfe sha d'aya na safe Abbas ya iso tare da Feenah, tuni Amarya Fauzy tasha had'addan k'unshi an kuma gyara mata kai haka jikinta ma yasha gyara don tun a Katsina ake ta mata gyaran jiki skin d'inta tayi wani irin sumul sai shek'i take, zuwa k'arfe sha biyu da rabi na rana garin Funtua ya cika makil da jama'a ba abunda kake ji sai jiniya ga kuma jibga jibgan motoci masu numfashi dake ta kai kawo a saman tituna da tuni an rufe su an hana mutanen garin bin su saidai suyi zagaye, kamar yadda Ango Sameer yaci alwashin bazai k'ara zuwa a Mota ba hakan ce ta faru don kuwa a helicopter suka zo harda Haisam bama su kad'ai ba wasu daga cikin manyan mutane ma a helicopter d'in suka zo daga filin da suka sauka ne Motoci na Alfarma suka daukko su, Jama'a kuzo kuga ango Sameer yasha kyau har ya gaji yana sanye da rantsattsiyar shadda light ash d'inkin yar ciki da babbar riga ba K'aramin kyau ya k'ara ba a cikin kayan ko don bai saba sakawa ba ne, su Haisam angwaye suma babbar rigar shadda duk suka saka gaba d'ayansu Abokan ango iri daya sukai suma tasu ash ce amman tafi ta Angon cizawa ba K'aramin tsaruwa sukai ba dama duk gasu yan Madara harda Abokan shi turawa da suka zo suma duk shigar suka yi abun dai sai wanda ya gani, shima Mahaifin Sameer d'in His Excellency da muk'arraban shi duk sun iso gaba d'aya jiniya ta karad'e ko ina a lokacin harabar Masallacin Juma'an da za'a d'aura auren ta cika makil da Jama'a kama daga manyan yan siyasa masu Mulki da masu Sarauta, manyan yan kasuwa da sanannun masu kudi, Manyan Mutane wanda sune Nigeria aka had'a a wurin wasu sun zo da kan su wasu sun turo wakilci taro dai yay taro malam Yan Jarida ko ta ina suna d'aukar rahoto nima dai ina daga cikin su inata rubuto maku rahoton cike da taka tsantsan gudun kada in sha na jaki a wurin jami'ai dake ta kai kawo a wurin don na lura a fusace suke duk suna ruk'e da manyan makamai gaba d'aya sun yi shirin ko ta kwana. Daga cikin wad'anda suka zo bikon Amarya harda su Mom da Aunty Laila Aunty Mareeya ta shiga gabatar dasu wurin yan uwansu tana ce masu yadda suka ga Mom haka Mahaifiyar Angon take don yan biyu ne, sosae Mom ta sakar masu fuska anata faman kawo mata gaisuwa tare da yi mata godiya da murmushi take fad'in ba komai duk an zama daya. Ana gama sallar Juma'a dubban mutane suka shaida d'aurin auren Sameer da Fauzy wanda Aminin Governor wato Senator Ali Adamu Zakee ne ya kar6a mashi akan sadaki Naira dubu d'ari biyar kamar yadda iyayen Fauzy suka buk'ata Jama'a sai fatan Alkhairi suke ma Governor mahaifin Sameer da Mahaifin Fauzy da kuma shi kanshi Angon da ba laifi ya saki fuska yana d'an murmushi haka Haisam ma sai murmushi yake shima ana mashi Allah ya sanya Alkhairi, ana gama d'aurin auren aka nufi inda aka tanada don yin reception wasu dai da yawa tafiya sukai, manyan motoci ne masu d'auke da Abinci iri iri aka bud'e a bakin Masallacin nan aka shiga rabama mutane a nutse don da mutum yay wasa yaji saukar dorina a gadon bayan shi, har gidan su Fauzyn ma Motar Abinci taje an sauke masu abun dai sai godiyar Allah, cikin wanda suka halarci sallar Juma'a aka kuma d'aura aure dasu bayan an tantance su Saboda tsaro harda Mujaheed da tun bayan daya san da Maganar auren baida cikakkar lafiya, daga nesa ya tsaya shida Usman suna hango Sameer lokacin da ake d'aura auren bayan an gama Usman yace mashi su tafi fuska kamar zai yi kuka yace mashi don Allah ya za'ai ya ga Fauziyya, waro ido Usman yay ya maimaita abunda yace Mujaheed din yace eh yana son ganinta kafin ta bar garin, ce mashi Usman yay gaskiya ganinta a yanzu abu ne mai wahala gara kawai su tafi amman ya kafe kan ya taimaka mashi yana son ya ganta ido da ido ko ya nemi yafiyar ta watak'il ya samu sauk'in abunda yake ji, nuna mashi yay Fauzy bata da matsala yasan tuni ma ta yafe mashi don haka ya hak'ura da ganinta karma suje suja ma kan su matsala, kafewa Mujaheed yay harda k'wallar shi ba yadda Usman ya iya gashi ya bashi tausayi sosae hakan yasa yace mashi suje gidan nasu amman shi yasan ganin Fauziyya a yanzu ba abu bane mai sauk'i suka nufi Motar Mujaheed bayan sun shiga yaja suka nufi gidan su Fauzy.
FRIDAY....
Alhamdulillah Allah ya kawo mu ranar d'aurin aure, a ranar tunda farar safiya jiniya ta fara tashi ta ko ina wurin k'arfe sha d'aya na safe Abbas ya iso tare da Feenah, tuni Amarya Fauzy tasha had'addan k'unshi an kuma gyara mata kai haka jikinta ma yasha gyara don tun a Katsina ake ta mata gyaran jiki skin d'inta tayi wani irin sumul sai shek'i take, zuwa k'arfe sha biyu da rabi na rana garin Funtua ya cika makil da jama'a ba abunda kake ji sai jiniya ga kuma jibga jibgan motoci masu numfashi dake ta kai kawo a saman tituna da tuni an rufe su an hana mutanen garin bin su saidai suyi zagaye, kamar yadda Ango Sameer yaci alwashin bazai k'ara zuwa a Mota ba hakan ce ta faru don kuwa a helicopter suka zo harda Haisam bama su kad'ai ba wasu daga cikin manyan mutane ma a helicopter d'in suka zo daga filin da suka sauka ne Motoci na Alfarma suka daukko su, Jama'a kuzo kuga ango Sameer yasha kyau har ya gaji yana sanye da rantsattsiyar shadda light ash d'inkin yar ciki da babbar riga ba K'aramin kyau ya k'ara ba a cikin kayan ko don bai saba sakawa ba ne, su Haisam angwaye suma babbar rigar shadda duk suka saka gaba d'ayansu Abokan ango iri daya sukai suma tasu ash ce amman tafi ta Angon cizawa ba K'aramin tsaruwa sukai ba dama duk gasu yan Madara harda Abokan shi turawa da suka zo suma duk shigar suka yi abun dai sai wanda ya gani, shima Mahaifin Sameer d'in His Excellency da muk'arraban shi duk sun iso gaba d'aya jiniya ta karad'e ko ina a lokacin harabar Masallacin Juma'an da za'a d'aura auren ta cika makil da Jama'a kama daga manyan yan siyasa masu Mulki da masu Sarauta, manyan yan kasuwa da sanannun masu kudi, Manyan Mutane wanda sune Nigeria aka had'a a wurin wasu sun zo da kan su wasu sun turo wakilci taro dai yay taro malam Yan Jarida ko ta ina suna d'aukar rahoto nima dai ina daga cikin su inata rubuto maku rahoton cike da taka tsantsan gudun kada in sha na jaki a wurin jami'ai dake ta kai kawo a wurin don na lura a fusace suke duk suna ruk'e da manyan makamai gaba d'aya sun yi shirin ko ta kwana. Daga cikin wad'anda suka zo bikon Amarya harda su Mom da Aunty Laila Aunty Mareeya ta shiga gabatar dasu wurin yan uwansu tana ce masu yadda suka ga Mom haka Mahaifiyar Angon take don yan biyu ne, sosae Mom ta sakar masu fuska anata faman kawo mata gaisuwa tare da yi mata godiya da murmushi take fad'in ba komai duk an zama daya. Ana gama sallar Juma'a dubban mutane suka shaida d'aurin auren Sameer da Fauzy wanda Aminin Governor wato Senator Ali Adamu Zakee ne ya kar6a mashi akan sadaki Naira dubu d'ari biyar kamar yadda iyayen Fauzy suka buk'ata Jama'a sai fatan Alkhairi suke ma Governor mahaifin Sameer da Mahaifin Fauzy da kuma shi kanshi Angon da ba laifi ya saki fuska yana d'an murmushi haka Haisam ma sai murmushi yake shima ana mashi Allah ya sanya Alkhairi, ana gama d'aurin auren aka nufi inda aka tanada don yin reception wasu dai da yawa tafiya sukai, manyan motoci ne masu d'auke da Abinci iri iri aka bud'e a bakin Masallacin nan aka shiga rabama mutane a nutse don da mutum yay wasa yaji saukar dorina a gadon bayan shi, har gidan su Fauzyn ma Motar Abinci taje an sauke masu abun dai sai godiyar Allah, cikin wanda suka halarci sallar Juma'a aka kuma d'aura aure dasu bayan an tantance su Saboda tsaro harda Mujaheed da tun bayan daya san da Maganar auren baida cikakkar lafiya, daga nesa ya tsaya shida Usman suna hango Sameer lokacin da ake d'aura auren bayan an gama Usman yace mashi su tafi fuska kamar zai yi kuka yace mashi don Allah ya za'ai ya ga Fauziyya, waro ido Usman yay ya maimaita abunda yace Mujaheed din yace eh yana son ganinta kafin ta bar garin, ce mashi Usman yay gaskiya ganinta a yanzu abu ne mai wahala gara kawai su tafi amman ya kafe kan ya taimaka mashi yana son ya ganta ido da ido ko ya nemi yafiyar ta watak'il ya samu sauk'in abunda yake ji, nuna mashi yay Fauzy bata da matsala yasan tuni ma ta yafe mashi don haka ya hak'ura da ganinta karma suje suja ma kan su matsala, kafewa Mujaheed yay harda k'wallar shi ba yadda Usman ya iya gashi ya bashi tausayi sosae hakan yasa yace mashi suje gidan nasu amman shi yasan ganin Fauziyya a yanzu ba abu bane mai sauk'i suka nufi Motar Mujaheed bayan sun shiga yaja suka nufi gidan su Fauzy.