Sashe 78
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
har zasu fita daga cikin wurin Hajiya ta kai idonta kan wata Mota dake a lullu6e da tamfal, dakatawa tay ta nuna Motar da sandar ta tace ma Tk wannan fa yace mata Tahir ne ya kawo ta kusan fin wata kenan yace Ya Haisam ne yace ya kawo, jinjina kai tay tace ko Mota ya canza ne Tk d'in yace bai sani ba, kallon Fatuu tay tace "Mijin ki ya fad'a maki yayi sabuwar Mota ne" shiru ta d'an yi kafin tace a'a bata san ko tashi bace amman dai ya nuna mata hoton motoci yace ta za6a tun ranar da su gwaggo suka dawo Hajiyar tace to k'ilan tata d'in ce, da sauri Tk yace bari ya bud'e taga in itace yace ma Amadu ya kama mashi, lokacin da suka bud'e Motar har saida gaban Fatuu ya fad'i ganin jigunannar Motar matsayin tata don ta shaida wadda ta za6a d'in ce, gaba d'aya maido idanun su sukai kan Fatuu suna son jin tata d'in ce saida Tk yace mata itace sannan ta d'aga mashi kai alamar eh jiki a mace, da tsananin mamaki duk suka shiga bin Motar da kallo don ta had'u dai ba k'arya,
"Yanzu kina nufin wannan jibgegiyar Motar taki ce?" Amadu ne ya tambayi Fatun da mamaki, murmushi kawai take ta kasa magana don itama sosae taji Al'ajabin ganin Motar a matsayin tata, Hajiya ce tay d'an murmushi tace "tunda ta fad'a tata d'in ce, ai ba abun mamaki bane Ahmad, ko kamanta Mijinta sune Mota" Murmushi yay tare da jinjina kai Hajiya tayi mata Allah ya sanya Alkhairi suma suka shiga yi mata Mino sai washe baki take tana ta6a jikin Motar haka Fauzy ma taji ma Fatun farinciki sosae, Saude ce ta k'araso wurin don bata san sun iso ba tana d'akinta acan baya saida Officer ya kirata yay mata Albishir d'in dawowar Hajiyar, cikin washe baki ta gaishe da ita tare da an dawo lafiya Hajiya na murmushi ta amsa tay mata ya gida Sauden tace "gidan duk ba dad'i wllh da baku nan" yar dariya Hajiya tay tace to ai gata ta dawo sai su dasa daga inda suka tsaya Saude ta fad'ad'a dariyarta, kallon Fatuu dake kallonta tana mata murmushi tay suka gaisa itama tay mata an dawo lafiya da ya k'arfin jiki, maida idonta tay kan Motar da taga ana kallo Hajiya tace mata wai Motar Fateema ce suka tsaya kallo Sauden tace "Ma sha Allah, ashe ta Fateema ce amma dai Motar tayi kyau wllh" kallon Fatuu tay tayi mata Allah ya sanya Alkhairi ta amsa tana murmushi, nufar barin wurin Hajiya tay tana fad'in ita dai ta wuce in sun gama ganin Motar sun shigo Saude ta bi bayanta,
tana barin wurin Mino ta had'e hannuwanta ta hau yin d'an tsallen Murna tana fad'in yanzu wannan Motar ta Adda Fatuu ce, dafa Shoulder d'inta Fauzy tay suka kalli juna tace mata ta taya ta murna wllh Allah ya sanya Alkhairi ya tsare ta amsa da Amin tare da Fad'in " kema Allah ya maida ke a damshi na" Fauzy tace "Wai.....to Amin dai" duk sukai yar dariya,
"Ikon Allah, Yanzu wannan bugaggar Motar ta wannan yarinyar ce da aka raina tare da ni" Kawu Amadu ne ya fad'a yana ta tatta6a Motar don ba K'aramin tafiya tay da shi ba duk sukai dariya Tk yace "baka ji ance dare d'aya Allah kan yi Bature ba" da sauri Amadu ya jinjina kai "tabbas na shaida hakan akan yar fillo" duk suka kwashe da dariya, cikin washe baki Mino tace yakamata a d'ana su, Tk yace yanzu tunda yamma tayi kuma ga su Fatuu basu dad'e da dawowa ba a bari sai gobe tunda Weekend ne sai su zagaya gari cike da murna tace to, fitowa sukai daga cikin parking space d'in suka nufi part d'in Hajiya sai santin Motar suke ba ma kamar Amadu har Tk na fad'in ya lura dae Motar tayi mashi yace wllh ai ta had'u ba k'arya,
"kuma kasan Motar can fa zata iya yin miliyan Ashirin wllh" Tk ne ya fad'a duk suka waro ido bama kamar Fatuu sai yanzu ta gane dalilin da yasa Haisam yak'i fad'i mata kud'inta, sosae suka jinjina kud'in Motar har Amadu na rok'on Fatuu akan wai tace a canzo mata guda biyu daidai kud'in wannan sai ta bashi d'aya harda cewa shi ko ma ba mai kud'i ba tata tafi tsada don Allah duk sukai dariya lokacin suka k'araso bakin entrance suka shige, lokacin da suka shiga Hajiya na zaune akan 2 seater gabanta Sofa table ne Saude ta kawo mata bottle water da cup har ta sha Saude na zaune kan one seater daga can gefe suna hira, ciki suka k'araso kowa ya samu wuri ya zauna aka cigaba da yin hirar, bada Jimawa ba gwaggo ta shigo da sallama tana sanye da dogon hijab Navy blue da ta fito da hasken ta sosae, da murmushi ta k'araso ciki duk idanunsu na akanta Fatuu na ganinta ta mik'e da sauri ta nufeta tana ga gwaggonta, tana isa gwaggon ta tareta ta hanyar ruk'e ta tana mata murmushi, a shagwabe tace "Don Allah gwaggota ki bari in rungume ki wllh nayi missing d'in ki sosae" yar dariya gwaggo tay Fatun ta k'arasa fad'awa jikinta, d'agota tay suka nufo ciki gwaggo na yar dariya Hajiya tace "ai ni dai bansan ranar da Fateema zata girma ba wllh, ga dai girman ya kamata amman tak'i ta gane" duk akai dariya, zama gwaggo tay ta shiga gaishe da Hajiya tare da yi mata an dawo lafiya bayan sun gama gaisawa Saude da Fauzy duk suka gaishe da ita da fara'a ta amsa masu, juyowa tay ta kalli Fatuu data sak'alo hannunta ta rungumo kafad'ar gwaggo suka bi juna da murmushi,
"Gwaggo kinga Kumatun Adda Fatuu kamar an tura biredi ko" Mino ce tayi Maganar duk suka kwashe da dariya, Saude tace ma Hajiya table a shirye yake ko ta kawo Abincin nan ta d'an girgiza mata kai "ni kam dai a k'oshe nike saida muka ci muka k'oshi muka taho kuma a jirgi ma mun ci Snacks sai dai ko su Ameenatu in zasu ci k'ilan kuma uwar biyu taci don ba mamaki ta fara jin yunwa yanzu" a d'okance Mino tace "Adda Fatuu yan biyu zata Haifa" d'an yarfa hannu Hajiya tay tace "wama ya sani, in don ta Abincin da take ci ne in akace yan hud'u ma zata Haifa ai ba'a gardama ba" duk akai dariya,
"Ga shi kun zo tarbar baki mu kuma ko tsaraba ba mu yi ba" duk suka ce a'a ba komai Hajiyar ta sake cewa "ai ko ba don ku ba ma dole in nemo tsaraba kafin yaran unguwa su fara shigowa" Saude tace aikuwa kullum ne akai akai ake shigowa tambayar Hajiya ta dawo,
"Ai na sani, bari kiga asan na dawo yanzu a cika parlon anzo yi ma Hajiyar sanata sannu da zuwa" in ji Hajiya, Fatuu ce tace tana da su biscuits da chocolates a cikin kayanta da akayo gaba dasu sai a basu, tana rufe baki Hajiya tace "a'a ruk'e abun ki ban shirya ma rikicin mai juna biyu ba, yanzu in amsar maki abu kizo ki burkice man ke sai irin su kike so ni ina zan nemo maki su tunda ga Ahmad nan yaje shago ya kawo man hankalina a kwance" gaba d'aya aka sa dariya harda Fatun, mik'ewa gwaggo tay zata tafi tay ma Hajiya Allah ya huta gajiya zumbur Mino ta mik'e tana fad'in suje taga hadaddar Motar da aka Siya ma Adda Fatuu, da alamun mamaki tace Mota tayi kenan Amadu yace "Mota kam mai sunan Mota wllh" murmushin farinciki gwaggo tay kafin tayi Allah ya sanya Alkhairi ta juya kan Hajiya ta hau yin godiya Hajiyar tace "to miye na yin godiya kuma Dije don miji ya siya ma Matar shi abu, nima bansan da ita ba sai yanzu da na gani, kinsan ya samu sabbin jini ya watsar da ni" duk akai dariya Gwaggo tace aikuwa dole zai dawo mata don da tsohuwar Zuma ake Magana Hajiya ta ta6e baki tace bata so ta yafe masu shi, k'ok'arin mik'ewa tay itama tana fad'in bari ta shiga ciki Magrib ma ta kawo jiki, a tare da gwaggo duk suka fito suka nufi parking space,
Tk da Amadu ne suka bud'e mata Motar ta gani ta hau yin faffad'an murmushi Mino tace "gwaggo ya kikab ga Motar?" jinjina kai tay tace "Ma sha Allah, tayi kyau sosae wllh, Allah ubangiji yasa Alkhairi ya kuma tsare" duk suka amsa da Amin harda Fatun, Amadu ne yace ta matso ta ta6a tasa Albarka Mino harda fad'i mata kud'in da Tk yace Motar take sosae gwaggo ta jinjina kud'in, bayan ta gama gani an maida an rufe suka fito daga cikin parking space d'in Tk yay masu sallama ya nufi baya inda d'akin shi yake, Fatuu tace ma gwaggon tazo suje part d'in ta tana murmushi tace tayi mata mi tace su k'ara gaisawa sai tayi salla a can, girgiza mata kai tay tace ta dawo wani lokacin a shagwabe tace ita da ba wani zuwa take ba, magiya ta fara yi mata gwaggon tace bafa zata je ba tunda dai sun gaisa, sallama sukai da ita ta tafi tare da Amadu su kuma suka nufi part d'in su Fatuu,
"Yanzu kina nufin wannan jibgegiyar Motar taki ce?" Amadu ne ya tambayi Fatun da mamaki, murmushi kawai take ta kasa magana don itama sosae taji Al'ajabin ganin Motar a matsayin tata, Hajiya ce tay d'an murmushi tace "tunda ta fad'a tata d'in ce, ai ba abun mamaki bane Ahmad, ko kamanta Mijinta sune Mota" Murmushi yay tare da jinjina kai Hajiya tayi mata Allah ya sanya Alkhairi suma suka shiga yi mata Mino sai washe baki take tana ta6a jikin Motar haka Fauzy ma taji ma Fatun farinciki sosae, Saude ce ta k'araso wurin don bata san sun iso ba tana d'akinta acan baya saida Officer ya kirata yay mata Albishir d'in dawowar Hajiyar, cikin washe baki ta gaishe da ita tare da an dawo lafiya Hajiya na murmushi ta amsa tay mata ya gida Sauden tace "gidan duk ba dad'i wllh da baku nan" yar dariya Hajiya tay tace to ai gata ta dawo sai su dasa daga inda suka tsaya Saude ta fad'ad'a dariyarta, kallon Fatuu dake kallonta tana mata murmushi tay suka gaisa itama tay mata an dawo lafiya da ya k'arfin jiki, maida idonta tay kan Motar da taga ana kallo Hajiya tace mata wai Motar Fateema ce suka tsaya kallo Sauden tace "Ma sha Allah, ashe ta Fateema ce amma dai Motar tayi kyau wllh" kallon Fatuu tay tayi mata Allah ya sanya Alkhairi ta amsa tana murmushi, nufar barin wurin Hajiya tay tana fad'in ita dai ta wuce in sun gama ganin Motar sun shigo Saude ta bi bayanta,
tana barin wurin Mino ta had'e hannuwanta ta hau yin d'an tsallen Murna tana fad'in yanzu wannan Motar ta Adda Fatuu ce, dafa Shoulder d'inta Fauzy tay suka kalli juna tace mata ta taya ta murna wllh Allah ya sanya Alkhairi ya tsare ta amsa da Amin tare da Fad'in " kema Allah ya maida ke a damshi na" Fauzy tace "Wai.....to Amin dai" duk sukai yar dariya,
"Ikon Allah, Yanzu wannan bugaggar Motar ta wannan yarinyar ce da aka raina tare da ni" Kawu Amadu ne ya fad'a yana ta tatta6a Motar don ba K'aramin tafiya tay da shi ba duk sukai dariya Tk yace "baka ji ance dare d'aya Allah kan yi Bature ba" da sauri Amadu ya jinjina kai "tabbas na shaida hakan akan yar fillo" duk suka kwashe da dariya, cikin washe baki Mino tace yakamata a d'ana su, Tk yace yanzu tunda yamma tayi kuma ga su Fatuu basu dad'e da dawowa ba a bari sai gobe tunda Weekend ne sai su zagaya gari cike da murna tace to, fitowa sukai daga cikin parking space d'in suka nufi part d'in Hajiya sai santin Motar suke ba ma kamar Amadu har Tk na fad'in ya lura dae Motar tayi mashi yace wllh ai ta had'u ba k'arya,
"kuma kasan Motar can fa zata iya yin miliyan Ashirin wllh" Tk ne ya fad'a duk suka waro ido bama kamar Fatuu sai yanzu ta gane dalilin da yasa Haisam yak'i fad'i mata kud'inta, sosae suka jinjina kud'in Motar har Amadu na rok'on Fatuu akan wai tace a canzo mata guda biyu daidai kud'in wannan sai ta bashi d'aya harda cewa shi ko ma ba mai kud'i ba tata tafi tsada don Allah duk sukai dariya lokacin suka k'araso bakin entrance suka shige, lokacin da suka shiga Hajiya na zaune akan 2 seater gabanta Sofa table ne Saude ta kawo mata bottle water da cup har ta sha Saude na zaune kan one seater daga can gefe suna hira, ciki suka k'araso kowa ya samu wuri ya zauna aka cigaba da yin hirar, bada Jimawa ba gwaggo ta shigo da sallama tana sanye da dogon hijab Navy blue da ta fito da hasken ta sosae, da murmushi ta k'araso ciki duk idanunsu na akanta Fatuu na ganinta ta mik'e da sauri ta nufeta tana ga gwaggonta, tana isa gwaggon ta tareta ta hanyar ruk'e ta tana mata murmushi, a shagwabe tace "Don Allah gwaggota ki bari in rungume ki wllh nayi missing d'in ki sosae" yar dariya gwaggo tay Fatun ta k'arasa fad'awa jikinta, d'agota tay suka nufo ciki gwaggo na yar dariya Hajiya tace "ai ni dai bansan ranar da Fateema zata girma ba wllh, ga dai girman ya kamata amman tak'i ta gane" duk akai dariya, zama gwaggo tay ta shiga gaishe da Hajiya tare da yi mata an dawo lafiya bayan sun gama gaisawa Saude da Fauzy duk suka gaishe da ita da fara'a ta amsa masu, juyowa tay ta kalli Fatuu data sak'alo hannunta ta rungumo kafad'ar gwaggo suka bi juna da murmushi,
"Gwaggo kinga Kumatun Adda Fatuu kamar an tura biredi ko" Mino ce tayi Maganar duk suka kwashe da dariya, Saude tace ma Hajiya table a shirye yake ko ta kawo Abincin nan ta d'an girgiza mata kai "ni kam dai a k'oshe nike saida muka ci muka k'oshi muka taho kuma a jirgi ma mun ci Snacks sai dai ko su Ameenatu in zasu ci k'ilan kuma uwar biyu taci don ba mamaki ta fara jin yunwa yanzu" a d'okance Mino tace "Adda Fatuu yan biyu zata Haifa" d'an yarfa hannu Hajiya tay tace "wama ya sani, in don ta Abincin da take ci ne in akace yan hud'u ma zata Haifa ai ba'a gardama ba" duk akai dariya,
"Ga shi kun zo tarbar baki mu kuma ko tsaraba ba mu yi ba" duk suka ce a'a ba komai Hajiyar ta sake cewa "ai ko ba don ku ba ma dole in nemo tsaraba kafin yaran unguwa su fara shigowa" Saude tace aikuwa kullum ne akai akai ake shigowa tambayar Hajiya ta dawo,
"Ai na sani, bari kiga asan na dawo yanzu a cika parlon anzo yi ma Hajiyar sanata sannu da zuwa" in ji Hajiya, Fatuu ce tace tana da su biscuits da chocolates a cikin kayanta da akayo gaba dasu sai a basu, tana rufe baki Hajiya tace "a'a ruk'e abun ki ban shirya ma rikicin mai juna biyu ba, yanzu in amsar maki abu kizo ki burkice man ke sai irin su kike so ni ina zan nemo maki su tunda ga Ahmad nan yaje shago ya kawo man hankalina a kwance" gaba d'aya aka sa dariya harda Fatun, mik'ewa gwaggo tay zata tafi tay ma Hajiya Allah ya huta gajiya zumbur Mino ta mik'e tana fad'in suje taga hadaddar Motar da aka Siya ma Adda Fatuu, da alamun mamaki tace Mota tayi kenan Amadu yace "Mota kam mai sunan Mota wllh" murmushin farinciki gwaggo tay kafin tayi Allah ya sanya Alkhairi ta juya kan Hajiya ta hau yin godiya Hajiyar tace "to miye na yin godiya kuma Dije don miji ya siya ma Matar shi abu, nima bansan da ita ba sai yanzu da na gani, kinsan ya samu sabbin jini ya watsar da ni" duk akai dariya Gwaggo tace aikuwa dole zai dawo mata don da tsohuwar Zuma ake Magana Hajiya ta ta6e baki tace bata so ta yafe masu shi, k'ok'arin mik'ewa tay itama tana fad'in bari ta shiga ciki Magrib ma ta kawo jiki, a tare da gwaggo duk suka fito suka nufi parking space,
Tk da Amadu ne suka bud'e mata Motar ta gani ta hau yin faffad'an murmushi Mino tace "gwaggo ya kikab ga Motar?" jinjina kai tay tace "Ma sha Allah, tayi kyau sosae wllh, Allah ubangiji yasa Alkhairi ya kuma tsare" duk suka amsa da Amin harda Fatun, Amadu ne yace ta matso ta ta6a tasa Albarka Mino harda fad'i mata kud'in da Tk yace Motar take sosae gwaggo ta jinjina kud'in, bayan ta gama gani an maida an rufe suka fito daga cikin parking space d'in Tk yay masu sallama ya nufi baya inda d'akin shi yake, Fatuu tace ma gwaggon tazo suje part d'in ta tana murmushi tace tayi mata mi tace su k'ara gaisawa sai tayi salla a can, girgiza mata kai tay tace ta dawo wani lokacin a shagwabe tace ita da ba wani zuwa take ba, magiya ta fara yi mata gwaggon tace bafa zata je ba tunda dai sun gaisa, sallama sukai da ita ta tafi tare da Amadu su kuma suka nufi part d'in su Fatuu,