← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 211

Sashe 56

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Bayan Nameer ya shigo gidan daga Masallaci direct d'akin Hajiya ya wuce lokacin daya shiga parlon su gwaggo na zaune bata dad'e da gama yin salla ba suka zauna suna kallo ita da wasu yan uwan su da suke a part d'in Hajiyar, tsayawa yayi suka gaisa kafin ya wuce Bedroom, da sallama ya shiga ya hangota zaune akan prayer mat ta jingina da gado, wurinta ya nufa yana zuwa shima ya zauna a k'asa kan Carpet kusa da ita tana ta kallon shi fuskar ta a sake, ganin yayi shiru yasa ta ce mashi ya akai, gaishe da ita yay ta amsa, jimm yay sai d'an murmushi yake yama rasa ta ina zai fara, sake tambayar shi tay wai lafiya yazo ya tasata a gaba sai wani murmushi yake kaman wani zautacce, ce mata yay dama zuwa gaishe da ita yay ta d'an harare shi ya d'age gira yace ko bata so, d'an ta6e baki tay tace to ta gode sai kuma mi, saida ya d'an sosa k'eyar shi sannan ya fara Magana da yar in ina yace mata dama ya samu wacce yake so ne a wurin bikin nan kuma har sun daidaita ma to shine yake son don Allah tay ma Dad magana sai ayi magana da parents d'in ta, zuru tay tana kallon shi har ya gama tay d'an murmushi tace wacece ya ke son, fad'i mata yay k'anwar bride d'in Ya Haisam da d'an alamun mamaki tace wacce k'anwar tata yace mata Mino, d'an wara ido tay tace "Kai yaushe har kasan Ameenatun da zaka ce kana son ta kuma kun daidaita?" Fad'i mata yay anan bayan sun zo, shiru tay ta d'an jinjina kai idonta akan carpet shi kuma yanata kallonta yana jiran ya ji mi zata ce, maido idon tay kan shi tace Yanzu in aka yi magana da iyayen nata aurenta zai yi da sauri ya d'aga mata kai, d'an shiru ta k'ara yi sai kuma tace "ni da nayi tunanin kai ma yar gida za'a yi kai da yar'uwar matar yayan taka Farha" wata yar zabura yay ya bita da wani kallo na baka tsammaci jin abu ba, tana murmushi tace mashi eh ba sai a k'ara yin yar gida ba a k'ara dankon zumunci, da sauri ya girgiza mata kai yace "ni gaskiya bazan iya auren ta ba yarinyar da bata girmama mutane ko gaishe ni fa bata iya yi in ma na samu tayi man kallon arziki, d'auka na take wani tsaranta taya zamu yi aure haka, kuma ma dai ai saida soyayya ake aure ko to ni gaskiya ban mata irin wannan son" ya k'arasa Maganar ya d'an 6ata fuska, kallo kawai Hajiya ta bi shi dashi sai k'ara 6ata rai yake, jimm tay can ta tambaye shi ita Minon ya tabbatar suna son juna ba sai anyi magana ba kuma azo kuma daga baya wani cikin su ya canza ra'ayi da sauri yace mata wllh duk suna son juna sosae sun ma yima juna alk'awarin kan haka, harara Hajiya ta wurga mashi ya sunnar da kai yana dariya, ajiyar zuciya ta sauke tace Shikenan zata yi ma Baban nashi magana tana rufe baki ya matsa ya rungumeta yana fad'in shiyasa yake son ta, ture shi ta fara yi tana fad'in ba wani dad'in bakin da zai yi mata ina wani so yake yana k'ok'arin yi mata kishiya, sakin ta yay yana dariya har zai mik'e sai kuma ya dakata yace mata don Allah koda Dad zai k'i tay convincing nashi wllh yarinyar bata da matsala in ya aureta ya dace mata, hannu tasa ta ruk'e ha6a alamar mamaki ya mik'e yana dariya ya nufi k'opa yana fad'in Allah yasa yaji Alkhairi, bayan ya fita Hajiya ta d'an girgiza kai.

Wuraren k'arfe goma da yan mintuna Senator ya dawo gidan yana sanye da babbar riga da yan ciki na brown shadda kan shi sanye da hula mahad'in kayan haka agogon shi da takalman shi da alama Haisam gadon yin to match yay, ta main parlor ya shigo bai bi ta k'opar da ke kai shi part d'in shi ba kamar yadda yake yi in ya dawo da daddare, hannuwan shi ruk'e da fararen ledoji nasu d'auke da tambari a jiki ya nufi part d'in Mom, Fatuu zaune a saman gado har tayi wanka ta saka doguwar rigar bacci kanta sanye da hula su twins da Abdul da Noor zagaye da ita gaba d'aya idanun su na akan tv d'in cikin d'akin suna kallon cartoon da akai ma Fatuu dole take kallo, da Sallama ya shigo duk suka kai idanun su kan shi aikuwa da sauri su twins suka sauka daga kan gadon suka nufe shi da gudu suna fad'in "Oyoyo Daddy" bud'a masu hannuwa yay suna zuwa a tare suka fad'a ya rungume su yana dariya, d'ago kai yay ya kalli su Abdul da suma suka saukko daga kan gadon daga d'an gaban su suka tsaya suna kallon su da murmushi, ce masu yay su bazasu yi welcoming d'in shi ba Noor ta ruga itama ya rungume ta ganin haka yasa Abdul ma yaje shima aka had'a dashi aka rungume, sakin su yay yana fad'in to su shiga ciki Mubeen da Mubeena suka kai hannu suna fad'in ya kawo su ruk'e ya sakar masu leda guda d'aya yace to su je su kai ma Yayar su ta saman gado, da gudu suka juya suna zuwa suka mik'a mata ta amsa tana murmushi, nufo ciki yay ya tsaya daga gaban gadon Fatuu ta gaishe da shi Fuska a sake ya amsa yay mata ya karfin jikin tace Alhamdulillah, tambayar ta yay taci Abinci ta ce mashi eh yace sosae tana murmushi ta k'ara cewa eh,

"To ga Fura nan sai ki k'ara" kai ta jinjina a hankali tace ta gode, su twins ne suka dawo gaban shi Mubeena ta kai hannu tana k'ok'arin amsar leda guda tana fad'in suma a basu fura d'in, janye ledojin yay ya 6oye su a bayan shi yana fad'in babu na su, wani kallo Mubeen yay mashi ya turo baki yace to wannan duk na waye yace mashi d'aya na Hajiyar shi ne d'aya kuma shi zai sha, a shagwabe Mubeena tace to ya basu nashi furan, wani kallo yay masu mai kaman harara yace to shifa, har suna had'a baki wurin fad'in sai yayi hak'uri, girgiza kai yay ya d'an tura baki irin yadda suke yace "ni bazan hak'uri ba gaskiya ai don in sha na siyo ko, wai yama akai baku yi bacci ba?" dariya yadda yayi ya basu Mubeena tace rabon zasu sha furan ne yasa basu yi bacci ba yace to kuwa bazasu sha ta ba,

k'ok'arin kamo ledar suka fara yi ta bayan shi yana kaucewa can ya d'age su sama yace in suka kama to zai basu, tsalle suka fara yi harda Noor da Abdul Fatuu sai dariya take sosae abunda suke ya saka ta nishad'i, ganin sun kasa kamowa don Dad d'in nasu ba gajere bane tur6une fuska su twins sukai suka hau yi mashi magiyar ya basu, suna haka Mom ta fito daga toilet tana sanye da bathrobe kanta ta nad'o towel, nufo su tay fuskarta da murmushi ta tsaya gefe, sannu da zuwa tay mashi ya amsa ta kalli su twins ta tambayi ya akai, kafin su bashi amsa Dad d'in yace fashi suke son yi mashi na furar shi kuma bada su ya siyo ba, yar dariya tayi tace a taimaka a basu tun da sun gani suka had'a baki suna rok'on shi ya basu, kwa6e fuska yay alamar zai yi kuka yana fad'in bazasu tausaya mashi ba su bar mashi furar shi, Noor da Abdul ne suka ce sun bar mashi ya sha su twins kuwa girgiza kai sukai suna bubbuga k'afa, mik'a masu leda guda yay suka saki k'arar murna Mom tace to suje Parlor su sha suka nufi hanyar fita daga d'akin suna fad'in "Thank you Daddy, We love you" yana dariya yace tunda sun raba shi da abun shi ba, wucewa Mom tay wurin mirror tana yar dariya ya kalli Fatuu ganin ta aje ledar yace ta sha yanzu Saboda ta bi jikinta cikin girmamawa tace to ta kai hannu ta fiddo robar furar ta fara bud'ewa, tambayar ta yay ko a kawo mata cup da sauri tace a'a zata sha a robar, jinjina kai yay sai kuma yace ta saki jiki duk abunda take so tayi magana sannan kada ta cika yin zirga zirga zuwa ta samu lpy sosae a hankali tace to, kai idon shi yay kan Mom dake yin shafa ta cire towel d'in kanta tana taje sumarta Tubarkallah gashin har k'ugunta gashi bak'i wuluk, maido idon shi yay kan Fatuu yayi mata sai da Safe ta amsa ya juya ya nufi hanyar fita idon ta akan shi tana murmushi.
Chapter 56 · 0% Book details