← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 71 OF 211

Sashe 71

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Fateema da kika ji ni shiru ba sai ki lek'o ba kiji lafiya ban taso ba ina can bacci ya fara d'aukata akan kujera" Hajiya ce data shigo tay Maganar tana yi tana hamma, gwalo ido Fatuu tay tayi shiru da sauri ta runtse idonta tana jin Hajiyar na fad'in ko bacci take a haka, gadon ta nufa bangaren da take kwanciya ta hau ta kwanta sai zabga uwar hamma take, tana kwanciya taci gaba da baccin dama da k'yar ta kawo kanta d'akin yau dai ko zaman yin Addu'a bata yi ba, Fatuu na jin saukar numfashinta da k'arfi ta gane tayi bacci, tashi tay zaune idonta akan Hajiya sai kace ta dad'e a kwance a yadda take baccin, hannu ta kai ta d'aukko wayarta ta duba time har k'arfe sha d'aya tayi, tunanin ta k'ara bata time tayi tay zaune tana yi tana kallon ta gaba d'aya ma sai taga time d'in bai gudu, bayan kaman minti goma ta yanke ta tafi sai kuma tay tunanin ta gwada tashin Hajiyar ta gani ko baccin bai yi nauyi ba in ta tashi sai tace mata dama taga bata canza kaya bane, da wannan tunanin ta mik'e ta zagaya side d'in da take ta fara kiran sunanta shiru hannu ta kai ta d'an bubbuga hannunta tana cigaba da kiran nata nan ma shiru, d'agowa Fatuu tay tana murmushi ta nufi wurin kayanta ta curo Hijab, bayan ta saka ta nufi bakin gadon ta d'auki wayarta, saida ta je ta ja duvet ta rufe ma Hajiyar rabin jikinta ta kashe wutar d'akin sannan ta nufi hanyar fita, a parlon ma saida ta kashe kayan kallon da hasken cikin shi sannan ta nufi hanyar fita, saida ta tsaya ta lallek'a ta tabbatar ba kowa sannan ta fito sauri sauri gudu gudu ta nufi hanyar baya, tana tafiya zuciyarta na raya mata to yanzu in Hajiyar ta farka kuma fa, girgiza kai tay ta tabbatar ma kanta tunda maganin yayi aiki bazata farka ba tasan har ta koma don maganin nada k'arfi gashi biyu ta saka mata,

Lokacin data haye benen k'opar parlon nashi a rufe take, da sauri ta d'ago wayarta ta shiga k'ok'arin kiran shi, yana yin picking tun kafin yace wani abu tace mashi yazo ya bud'e mata k'opa saida yaji mamakin hakan ya tambayi wace k'opa tace mashi ta shigowa part d'in shi ta baya, yana bud'e kopar suka had'a ido ta sakar mashi murmushi yana sanye da rigar bacci kimono broad chest d'in shi a bud'e, d'an waro ido yay alamar mamaki da sauri ta fad'a mashi ya kai hannu ya rungume ta, komawa yay ciki da ita bayan ya tura k'opar ya d'ago ta har lokacin murmushi take, da alamun mamaki yace mata ya akai tazo nan yanzu, farko shiru tay ta shiga tunanin bazata ce mashi magani ta bata ba sai kawai tace mashi ba tun d'azun take fama da ita ta barta tazo ta had'a mashi kaya ba amman ta k'iya shine yanzu da taga tayi bacci ita kuma ta taho, d'age gira yay sai kuma yay faffad'an murmushi yace mata bata tsoron ta tashi taga bata nan ta d'an tura mashi baki bata ce mashi komai ba,

"Yanzu kayan kika zo had'a man kenan?" ta d'aga mashi kai wani kallo ya bita dashi ta tura mashi baki, d'an murmushi yay yace mata to ai shi ya riga ya had'a kayan nashi ya za'ai kenan da sauri ta fad'a jikinshi tana fad'in suje a wargaza su ta sake had'a mashi, sosae yake dariya sai mutsu mutsu take mashi da kanta a chest nan take ta fara turning nashi on, hannu ya kai ya murd'a key k'opar ta rufe ya kai hannu ya d'auketa ya nufi ciki da ita. Duk yadda Haisam yaso kar ya xamo uncontrollable kaman yadda yake duk ya kasance da ita abun ya ci tura ba kamar kuma daya kasance ga halin da take ciki gaba d'aya ta canza mashi, bayan ya samu natsuwa hak'uri ya shiga bata yana tambayar is she Ok, shiru bata amsa mashi ba ta duk'unk'une guri guda, Jijjiga ta ya shiga yi yana kiran sunanta amman shiru, da sauri ya sauka daga saman gadon ya je ya kunna Switch, har saida gaban shi ya fad'i ganin yadda tay ta runtse ido hannunta guda dafe da cikinta, wani irin bugu gaban shi yay a rud'e ya dawo ya hau gadon, d'ago ta yay ya fara tambayarta lafiya miya faru shiru bata ce komai ba sosae ya razana, maida ta yay ya kwantar ya fara k'ok'arin sauka yana fad'in bari ya kaita hospital, ji yay ta ruk'e mashi hannu da sauri ya kai idon shi kanta kawae sai gani yay ta kyalkyace da dariya, wani kallo yake bin ta da shi ya d'an yamutsa fuska ta d'age mashi gira kawai sai ya yarfa hannu yace "Zarah wannan wasa ne?" Yadda ya kwa6e fuska yasa ta k'ara kyalkyacewa da dariya, hannu ya kai ya dafe goshin shi ya maida idon shi k'asa, da sauri ta tashi zaune ta kai hannu tana k'ok'arin cire mashi hannun tana fad'in yayi hak'uri, k'in bata dama yay ta cire hannun a shagwabe tace in bai hak'uri ba Baby zai fito ya bashi hak'uri yanzun, juyowa yay yayi mata wani kallo idanunshi sun d'an yi ja, wara mashi ido tay tana murmushi ya d'an harareta, ta6e baki tay ta kai hannu ta kama kunnuwanta ta furta "i'm very sorry My Hubby bazan k'ara ba" yadda tayi ne ya bashi dariya yayi har fararen hak'oran shi suka bayyana ya kai hannu ya jawota ya rungume ta a wurin kunnanta ya rad'a mata so take tasa heart d'in shi tay bursting ne da sauri ta girgiza mashi kai yace to karta k'ara mashi irin wannan wasan da sauri ta d'aga kai, tambayar ta yay wai yaushe zata girma ne tana murmushi tace mashi ba rana, zamewa yay ya kwanta tare da ita ta yadda kanta na a saman chest d'in shi, shafa kanta ya shiga yi wani irin nishadi suke ji suna haka taji ya furta Allah yay mata Albarka tana murmushi idanunta a lumshe ta amsa tace shima Allah ya yi mashi Albarka ya amsa da Amin a haka bacci yay awon gaba da ita, jin saukar numfashin ta a hankali yasa shi kwantar da ita ya saukko ya nufi toilet,

Kiran sallar Farko ya farka kamar koda yaushe, tashi yay zaune ya kai hannu ya kunna lamp, juyowa yay ya sauke idon shi a kan Fatuu dake ta shan bacci, ji yay kamar ya k'yale ta amman bai son Hajiya ta tashi taga bata nan ya zama wani issue kuma duk da bai san ma ko ta tashi ba, tashin Fatun yay bayan ta bud'e ido yace ta tashi ya rakata kar Hajiya ta tashi tana jin hakan da sauri ta mik'e, tare suka fito ta baya, lokacin da suka shigo cikin main parlon a d'arare Fatuu take, tare suka shiga cikin parlon Hajiya ya tsaya anan yace ta duba taga ko ta tashi, gabanta na d'an Fad'uwa ta nufi Bedroom, cikin sand'a ta zagaya side d'in da take kwanciya saida ta d'an saurara sannan ta kai hannu ta kunna lamp d'in wurin,tsaye tay tana kallon Hajiya dake kwance kan gado tana ta bacci, d'an murmushi tay don ta fahimci bata tashi ba don data canza kaya zuwa na bacci Saboda bata kwanciya ba tare data saka kayan bacci ba, juyawa tay ta koma parlon ta fad'i mashi bacci take ya jinjina kai sai kuma yace mata to in ta tashi da daddare fa bata gan ta ba, d'an waro ido tay sai kuma tace ita dai in tayi mata magana kan hakan to zata ce shi yazo tana bacci ya d'auketa, yar dariya yay ya kai hannu ya kamo ta jikinshi yace sharri ko tanata dariya, saida yay pecking kumatunta sannan ya juya ya tafi ita kuma ta nufi Bedroom d'in, bayan ta shiga cikin sand'a ta nufi side d'in da take kwanciya ta cire Hijab d'in jikinta sannan ta hau gadon ta kwanta, tunawa tay da she needs to take bath a hankali ta tashi saida ta kallo Hajiya sannan ta mik'e ta nufi toilet, tana fitowa aka fara kiran salla na biyu nan take alarm d'in wayar Hajiya ya fara k'ara da sauri har tana yin tuntube da carpet taje ta haye gadon ta cure guri guda tana zare ido, har alarm d'in ya yanke ya sake fara wata k'arar shiru bata ji Hajiya ta tashi ba, a saninta tunkafin lokacin salla Hajiya ke tashi tayi raka'atanil fajr a wurin zata zauna har lokacin salla yayi, a ranta ta raya to miyasa yau bata tashi ba, bata kawo komai a ranta ba ta saukko ta nufi wurin kayanta, doguwar riga ta saka ta maida Hijab d'in data dawo da ita ta kabbara salla, har ta gama Hajiya bata ko motsa ba, tana zaune akan prayer mat ta kai idonta kan Hajiyar a cikin ranta ta fara raya to wai lafiya bata tashi ba, zuciyarta ce ta bata taje ta tashe ta, tun Fatuu na kiran sunanta har ta kai ta fara d'an bubbuga hannunta, tsoro ne ya kama Fatuu ganin yadda take ta tada Hajiyar amman ko motsi bata yi ba, tun tana bubbuga ta har takai ta fara jijjigata tana fad'in Hajiya ki tashi don Allah, gaba d'aya Fatuu ta kid'ime tuni ta fara kuka Fuskar ta share share da hawaye zuciyarta ta shiga raya mata kodai maganin nan data bata ya kashe ta, da sauri ta kai hannu ta ta6a saitin Zuciyar ta sam ta kasa gane komai, kai kunnanta tai saitin fuskar ta taji gaba d'aya bata numfashi, d'agowa tay a gigice ta d'aura hannuwa a saman kai tana fad'in ta bani ta lalace badai ta kashe Hajiya ba, Haisam ne ya fad'o mata a rai ta juya tana laluben wayarta don ta kira shi sai dai bata gan ta ba can ta tuna ta baro ta a part d'in shi, a sukwane ta sauka daga saman gadon ta nufi hanyar fita da gudu.............

88

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
Chapter 71 · 0% Book details