Sashe 158
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
"Kusan hakan, kinsan fa koda muna London bayan mun dawo daga Honeymoon in zaije wani wuri indai kwana zai yi dani yake tafiya, ai Honey ba sauƙi sai da na samu cikin nan ne ganin ina wahala ake ɗan raga man" Fatuu na dariya tace ai hakan ake so a damu da kai sai ta dage taita gyara kanta don ma halin da take ciki ba komai zata iya sha ba Fauzyn tace eh tama daina shan wani magani Aunty ma tace a halin da take ciki ba sai tasha komai ba, bada jimawa ba Sameer ɗin ya kirata ya sanar mata gashi a gaban entry hall, tare da Fatuu suka fito tayo mata rakiya suna ƙarasowa gaban Motar ya buɗe Motar tun kafin ya idasa fitowa ƙamshin turarenshi ya karaɗe wurin, sanye yake cikin ƙananan kaya Fuskarshi tayi wani irin Fresh har yar ƙiba ya ƙara da yake wurin fayau yake da haske, bayan ya fito gaisawa sukai da Fatuu fuskarshi a sake yay mata ya hidima ta amsa da Alhamdulillah yace Allah yasa alkhairi, bayan ta amsa ya ambayi ina yaranshi tace suna wurin Mom yace a gaishe mashi dasu, maida idon shi yay kan Fauzy data jingina da Motar ta langa6ar da kai slowly yace "hope u'r Ok?" lumshe mashi ido tay ta ɗan ɗaga mashi kai yace to suje tare da yi mata alama da kai, tare suka zagaya ɗayan bangaren ya kai hannu ya buɗe mata ƙopar saida ta juyo ta kalli Fatuu dake tsaye tana ta murmushi ta ɗan ɗaga mata hannu itama ta ɗago mata sannan ta shige ya maida ƙopar ya rufe bayan ya zagayo driver side yayi ma Fatuu sallama ya buɗe ya shige, saida yaja Motar sannan ta juyo komowa cikin gidan tanata murmushin daɗi ganin yadda Sameer yake kulawa da Fauzy harda su buɗe mata ƙopa abunda bata ta6a zaton zai yi ma mace ba, bayan sun hau titi sosae ya juya ya kalli Fauzy data kwantar da kanta jikin headrest ya kai hannun shi dake gefenta ya kamo nata daga yadda take ta juyo da kan ta kalle shi yace mata ko jikin ne ta girgiza mashi kai alamar a'a ya sake cewa ko tana jin yunwa ne nan ma ta girgiza mashi kai yaci gaba da driving da hannu ɗaya ɗayan kuma yana ruƙe da nata can bayan wani ɗan lokaci ya sake juyowa ya kalleta ya tambayi ko tana son wani abu ta ɗan yi shiru kafin tace tana son ice cream yay ɗan shiru tare da maida idon shi kan hanya taji yace tana shan abu mai sanyi sosae ba ba'a son suna sha ba, ɗan yamutsa fuska tayi ta sigar shagwa6a tace to ai cikin ne yake mata zafi sai tasha abu mai sanyi take jin sauƙi ya jinjina kai, a bakin wani babban cold store ya parker tare da buɗe Motar yace mata yana zuwa ta ɗaga mashi kai, nufar shiga wurin yay tanata kallon shi ta glass wata irin ƙaunar shi na ratsata, After few minutes ya fito ruƙe da leda mai tambarin wurin ya dawo wurin Motar, bayan ya shiga ya miƙa mata ta amsa tare da furta "thank you Honey" jinjina mata kai yay ya ja suka tafi, bude ledar tayi ta fiddo roba ɗaya bayan ta buɗeta fara sha, tana cikin sha ta ɗebo ta kai bakin shi idon shi akan hanya ya buɗe ta zuba mashi bayan ya shanye ya furta mata "Love you Babes" tana murmushi tace "love you too Honey.....the best Husband ever" ɗan juyowa yay yayi mata wani kallo tana murmushi ta kashe mashi ido yay faffaɗan murmushi tare da maida idon shi kan titi bayan ɗan lokaci suka iso gidan su inda ya ta6a kawota.
Bangaren Amarya Laila tuni suka isa Kano aka ɗaukko su daga Airpot a cikin jigunannun motoci masu numfashi, gidan su Angon aka nufa dasu dake a Nasarawa G.r.a, katafaren gida ne daya amsa sunan gidan masu kuɗi sosae gari guda zagaye shi a ƙafa ba ƙaramin aiki bane an narka uwar dukiya tun daga kan ginin, gidan yana da part part da yawa don matan Mahaifin Angon nata ukku surukar Laila ɗin ce ta farko hakan yasa gidan suna da ɗan yawa, a part ɗin Momyn Bashir ɗin wanda ƙarshe ne wurin haɗuwa aka saukesu sun samu kyakkyawar tarba daga danginsu, bayan sun huta aka kawo masu lafiyayyun abinci da abubuwan sha, misalin karfe biyar aka shiga shirin yin buɗar kai da za'ayi anan cikin harabar gidan har an yi haɗaɗɗan decoration gidan ya ƙara cika da Jama'a harda anko aka yi, bayan duk an shirya Amarya Laila ma ta canza shiga haka su Jidderh duk sun canza kaya ba 6ata lokaci aka shiga gabatar da buɗa kan, Sai bayan isha'i aka gama An ci an sha an yi hotuna da Vedios Sosae aka nishaɗantu, ana gama yin buɗar kan aka fara shirin kai Laila gidanta wanda shima ke anan cikin G.r.a ɗin dama duk mazan gidan masu aure anan unguwar gidajen su suke don Mahaifinsu nada gidaje a cikin unguwar sosae wasu hayar su ake, jerin motoci ne aka kawo don ɗaukar yan kai Amaryar bayan duk an shishshiga a tare motocin suka tafi, ba wata tafiya akai sosae ba aka iso gidan tun daga wajen gidan zaka shaida haɗuwarshi, gaba ɗaya motocin saida suka shige cikin harabar gidan don babbane sosae an ƙawata cikin harabar da shuke shuken fulawoyi masu kyau da tsari ga hasken fitulu sun haske ko ina, bayan duk an firfito Aunty na ruƙe da Lailar Hajiya Maryam na daga gefe suka nufi shiga cikin gidan wanda ginin bene ne, sosae su Hajiya Maryam suka yaba da tsarin gidan ita Aunty dama sun zo da aka kawo kayanta duk da basu ne suka shirya mata kayan ɗaki ba masu shirya gida aka ɗaukko suka yi aiki su kawai umarni suka rinƙa badawa, gidan Laila sai san barka an kashe naira ba ƙaɗan ba wurin yi mata kayan ɗaki sai yabawa ake, idan nace zan bayyana yadda tsarin gidan yake to kuwa ba ƙaramin lokaci zan ɗauka ba kawai dai abunda zance shine gidan Laila ƙarshe ne wurin haɗuwa Aljannar duniya ne an zuba mata kaya na gani na faɗa sai fatan Allah yasa gidan zamanta ne na har abada, tare dasu Aunty aka dawo gidansu Angon aka barota ita kaɗai anan zasu kwana gobe in Allah ya kai mu su juyo Abuja.
Bangaren Amarya Laila tuni suka isa Kano aka ɗaukko su daga Airpot a cikin jigunannun motoci masu numfashi, gidan su Angon aka nufa dasu dake a Nasarawa G.r.a, katafaren gida ne daya amsa sunan gidan masu kuɗi sosae gari guda zagaye shi a ƙafa ba ƙaramin aiki bane an narka uwar dukiya tun daga kan ginin, gidan yana da part part da yawa don matan Mahaifin Angon nata ukku surukar Laila ɗin ce ta farko hakan yasa gidan suna da ɗan yawa, a part ɗin Momyn Bashir ɗin wanda ƙarshe ne wurin haɗuwa aka saukesu sun samu kyakkyawar tarba daga danginsu, bayan sun huta aka kawo masu lafiyayyun abinci da abubuwan sha, misalin karfe biyar aka shiga shirin yin buɗar kai da za'ayi anan cikin harabar gidan har an yi haɗaɗɗan decoration gidan ya ƙara cika da Jama'a harda anko aka yi, bayan duk an shirya Amarya Laila ma ta canza shiga haka su Jidderh duk sun canza kaya ba 6ata lokaci aka shiga gabatar da buɗa kan, Sai bayan isha'i aka gama An ci an sha an yi hotuna da Vedios Sosae aka nishaɗantu, ana gama yin buɗar kan aka fara shirin kai Laila gidanta wanda shima ke anan cikin G.r.a ɗin dama duk mazan gidan masu aure anan unguwar gidajen su suke don Mahaifinsu nada gidaje a cikin unguwar sosae wasu hayar su ake, jerin motoci ne aka kawo don ɗaukar yan kai Amaryar bayan duk an shishshiga a tare motocin suka tafi, ba wata tafiya akai sosae ba aka iso gidan tun daga wajen gidan zaka shaida haɗuwarshi, gaba ɗaya motocin saida suka shige cikin harabar gidan don babbane sosae an ƙawata cikin harabar da shuke shuken fulawoyi masu kyau da tsari ga hasken fitulu sun haske ko ina, bayan duk an firfito Aunty na ruƙe da Lailar Hajiya Maryam na daga gefe suka nufi shiga cikin gidan wanda ginin bene ne, sosae su Hajiya Maryam suka yaba da tsarin gidan ita Aunty dama sun zo da aka kawo kayanta duk da basu ne suka shirya mata kayan ɗaki ba masu shirya gida aka ɗaukko suka yi aiki su kawai umarni suka rinƙa badawa, gidan Laila sai san barka an kashe naira ba ƙaɗan ba wurin yi mata kayan ɗaki sai yabawa ake, idan nace zan bayyana yadda tsarin gidan yake to kuwa ba ƙaramin lokaci zan ɗauka ba kawai dai abunda zance shine gidan Laila ƙarshe ne wurin haɗuwa Aljannar duniya ne an zuba mata kaya na gani na faɗa sai fatan Allah yasa gidan zamanta ne na har abada, tare dasu Aunty aka dawo gidansu Angon aka barota ita kaɗai anan zasu kwana gobe in Allah ya kai mu su juyo Abuja.