← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 131 OF 211

Sashe 131

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"To uban me ya kawo shi nan kuma, koda yake nama ji dad'i daya zo ya gane ma idon shi komai" Aunty ta fad'a ta d'aure fuska tare da yamutsa baki can kuma sai cewa tayi bari ma a bud'e glass d'in don ya shaida da kyau itace Amaryar, duk yadda taso ta sauke glass d'in ta kasa har ta kai tace ma Fatuu wai ta bud'e tunda dai ita tafi ta sanin takan kayan masu arzuki Maganar har saida taba Fatuu yar dariya itama ta fara k'ok'arin sauke glass d'in amman ta kasa can Aunty tace bari ta tambaya tunda ai dai sun san Amaryar yar talakawa ce bazai zama sun yi k'auyanci ba, dariya Fatuu tasaka Aunty Mareeyar ta kai hannu ta d'an janye labulan dake tsakanin su da Driver ta d'an lek'a a Kusan tare su duka na gaban suka juyo suka kalleta yadda ta sak'a kan kamar mage, da d'an murmushi tace masu sannun su suka amsa kafin tace don Allah glass d'in baya za'a sauke masu su dai sun duba basu ga inda ake saukewa ba, suma murmushin ne akan fuskar su Security d'in dake gefen driver duk da shima driver d'in kamar security d'in ne daga yanayin shigar shi yace mata kodai basu iya bud'e glass d'in bane, da sauri tace "a'a wllh Yallabai mun iya indai yadda ake sauke glass d'in kowacce Mota ne tunda dai muma muna da yan motocin nan, kuma koda ma ace ni ban iya bane ai d'ayar da muke tare ita dole ace ta iya tunda matar Cousin d'in Angon ce d'an Senator Ali Zakee nasan baku rasa sanin shi" kai ya jinjina mata tace to har itama tayi tayi ta kasa sauke shi balle ace sun yi k'auyanci, yanayin yadda take Maganar ne ya basu dariya don sun fahimci yar barkwanci ce, driver d'inne yace mata basu yi k'auyanci ba ta nan gaba ake sauke glass d'in da sauri tace Yauwa koda taji to a sauke masu don Allah Security d'in yay mata alamun ta koma ciki ta janye kan nata ya sak'o nashi inda suke ya mik'a yatsa yana nuna mata wani wuri a jikin k'opar Motar da ita kanta abun kallo ce yace mata in tana son yin magana da su nan zata latsa sai kawai ta fad'i abunda take son ayi ba sai ta lek'a ba ta jinjina mashi kai kafin tace kenan kamar yanzu da take son a sauke glass tana latsa wurin sai tace ayi haka yace mata Yess zata ga glass d'in ya sauka ta washe baki tana fad'in Allahu Akbar shima yar dariyar yay sai kuma ya nuna mata screen yace ga system nan in suna so sai suyi kallo ya shiga nuna mata yadda zata kunna yace akwae Movies a ciki saidai ba masu yawa bane amman in tana so zata iya connecting da wayarta sai ta kalli duk abunda take so har internet zata iya hawa tayi chat d'inta anan yana bayanin yana nuna mata yadda zata yi k'arshe kuma ya nuna mata game yace ga kuma game nan in tana son yi tayi mashi wani kallo tace sai kace dai wata k'aramar yarinya yay yar dariya, duk abun nan idon Fauzy na akan Mujaheed Fatuu dai kallon abunda ake nuna ma Aunty take tana yar dariya, bayan ya gama nuna mata ya maida kan shi kawai sai jin Maganar shi sukai ta karad'e bayan ta cikin wata yar speaker yana tambayar glass d'in wane side za'a bud'e masu ta bashi amsa da na hagu tana rufe baki glass d'in ya fara sauka, bin Mujaheed da kallo Fauzy tay gabanta ya hau d'an fad'uwa ganin yadda yay wani iri kamar ba shi ba Aunty kuwa yamutsa mashi fuska ta shiga yi tana hararar shi Fatuu ma bin shi tayi da kallo a ranta ta d'an ji mamakin ganin shi haka don ba haka Fauzy ta bayyana mata shi ba tace mata d'an gayu ne yanzu kuwa duk gashi ya cika mashi fuska gashi ya zumbula wata jallabiya sai kace liman, ganin irin Kallon da Fauzyn ke mashi ne ya bashi k'warin gwuiwa ya tunkaro Motar da sauri, saida ya kusa isowa kawai Aunty ta danna wurin da aka nuna mata da sauri tace a rufe glass d'in sai gashi ya fara rufewa slowly, burki Mujaheed yaci ya zuba ma Fauzy ido yayin da glass d'in ke rufewa, kallon Aunty Fatuu tayi da sauri tace "Aunty wannan ne Mujaheed d'in?" Fuska a Yamutse ta kwa6e baki ta bata amsa da eh shine banzan ko uban me ma yazo yi nan sai kuma tace koda yake gara da yazo ya gane ma idanun shi, yanayin fuskar Fauzy kaman zata yi kuka dama kuma shi ta gama yi ta kalli Aunty tace "Aunty da baki mashi haka ba zai zama kaman kin wulak'anta shi...." Tun kafin ta rufe baki ta katseta a fusace "au wai ke nan baki ji dad'in abunda nayi ba kike nufi komai, naji dad'i in har hakan da nayi mashi zai zama wulak'anci a gare shi da akwae wulak'ancin ma da yafi wannan to shi zan mashi, ke har kin manta da irin wulakancin da yayi maki zaki wani ce an mashi wulakanci",

11abu Fauzy ta had'iya k'walla suka zubo mata cikin karyayyar murya tace "abun da yay man d'in k'aruwa nayi ko raguwa Aunty, ni wllh na yafe mashi komai yayi man tun ma ba yanzu ba" ta6e baki Aunty tayi bata ce komai ba Fauzyn ta juya tana k'ara kallon shi yana a tsaya inda ya ja ya tsaya yana kallon Motar ya marairaice Fuska tare da had'e hannuwan shi ya d'an d'aga su sama alamar rok'o, kallon Aunty Fauzy tay tace "Aunty don Allah kisa a bud'e da alama akwae abunda yake so ya fad'a man ki bari muji miye don Allah baki ga yadda ya koma ba duk yayi wani iri kamar ba shi ba" wani uban tsoki taja rai 6ace tace "Wllh baza'a bud'e ba har yana da wani abun fad'i maki, to yace maki uban me kuma Maganar canzawa ya dad'e bai lalace ba wllh ko a kwalar vest d'ita, yanzu haka hakkin ki ne ke bibiyar shi tun ba'aje ko ina ba don haka ba abunda zance in ma hakan ne sai Allah ya k'ara in ma da k'ari ya k'ara mashi, Sakaran banza sakaran wofi" tana rufe baki Fauzy ta fashe da kuka, waro ida Aunty tay da tsananin mamaki tace "ke, mi nike gani haka, wai wanccan d'in kike ma kuka Saboda Maganganun da nayi to mi kike nufi da hakan??" Girgiza kai Fauzy tayi cikin kuka tace ita wllh ba abunda take nufi kawai dai ya bata tausayi ne don da gani yana cikin matsala mutumin da yake d'an gayu d'an Kwalisa a gan shi haka" ta6e baki Aunty tay tace ita dai ta sani, magiya Fauzy ta k'ara mata kan tasa a bud'e aikuwa a fusace Aunty tace "Wallahi tallahi baza'a bud'e ba, in kuma kikai wasa yanzun nan zan buk'aci a kirawo man Mijin naki ince ke kike son ganin shi da gaggawa yana zuwa in fad'i mashi abunda ke faruwa, kindai sani ai basai na fad'i maki ba tsaff zai kakkarya shi sai muga ta tsiyar tausayi, in ba ma yana mahaukaci ba shine zai wani jawo k'afafu kamar shebur wai zai yi magana dake wato shi ga mara ta ido ko duk abunda yay maki shine har zai wani nemi yin magana dake to kuwa yanzun nan zan sa a koya mashi kunyar da bai da ita" ta k'arasa tare da yin k'wafa, wani irin kuka mai sauti Fauzy ta saka dama k'iris take jira acikin ranta ta shiga tunano tun daga farkon had'uwarta da Mujaheed d'in yadda ya rink'a mata d'awainiya da tana Makaranta, sam lokacin ba ta tuno da sharrin shi ba sai Alkhairan shi, suna haka suka ji Muryar Security d'in ta cikin speaker d'in bayan yana tambayar lafiya wake kuka ne haka mike faruwa, zaro ido Aunty Mareeya tayi da sauri ta kai hannu ta jawo Fauzy jikinta tana k'ok'arin rufe mata baki tana fad'in ta bani kuji zata ja mata sharri taja a d'aureta, duk da yanayin da Fatuu take ciki na karyewar zuciya saida tayi yar dariya, k'ara tambayar su lafiya akai koda matsala ne da sauri Aunty ta latsa wurin Maganar ta bashi amsa da a'a ba komai amaryar ce ke kukan rabuwa da gida, wannan karon sosae ta ba Fatuu dariya, rarrashin Fauzy ta shiga yi tana fad'in Shikenan tayi hak'uri itafa duk Maganganun data yi 6acin rai ne yasa tayi su kuma bata ga amfanin tayi magana da shi ba tunda ita yanzu Matar aure ce ta rabu dashi kawai, cikin muryar kuka tace ba cewa tayi zata saka a kirawo mata Sameer ba ya kakkarya shi da sauri Aunty tace wllh duk cika baki ne ita tama fara kiran shi ta fad'i mashi haka yazo duk ya tarwatsa taron da rocket, dariya Kawai Fatuu ke yi a ranta ta raya yau Aunty ta tuno da rocket, suna haka aka ba motocin izinin tafiya a Kusan tare duk suka tashi jin haka yasa Fauzy d'agowa da sauri tana kallon Mujaheed d'in Motocin suka fara tafiya a jere gaba Motar Security ce haka k'arshe ma sannan a tsakiya ma abun dai gwanin burgewa nima dai ina a cikin ta yan jarida, tun bayan da Motocin suka fara tafiya Mujaheed yaji tamkar da jinin jikin shi suke tafiya a Hankali ya fara ganin jiri ya kai hannu ya dafe goshin shi ganin haka yasa Usman nufo shi da sauri ai ko kafin ya k'araso Mujaheed d'in ya tafi gaba d'aya zai kife cikin zafin nama ya tare shi duk wannan abun akan idon Fauzy dake ta kallon su ta glass da yake Motocin a slow suke tafiya, tana ganin haka ta juyo cikin kuka take ce ma Aunty ga Mujaheed d'in can ya fad'i kawai sai ta jawota jikin ta tana fad'in zai tashi ne in kuma ya wuce daga haka Allah ya jik'an shi.
Chapter 131 · 0% Book details