← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 211

Sashe 48

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kowa kaga ni fuskar shi d'auke da Murmushi wasu suna d'an juya kai suna bin wak'ar, lokacin da aka zo baitin da ake cewa _" kin rikirkita dukka tunani na, taimaka ki bani wurin kwana, son ki ya hana min bacci na, ina ganin ki har a mafarki na, son ki yanaiii min dad'i ban san mu rabu......"_ Laila da ke tsaye tana masu Vedio ta d'aga murya tace "Big Bro yi mata zaka rink'a yi fa" Murmushi kawae Haisam d'in yay Jidderh ma ta k'ara d'aga murya tana cewa ya saurara za'a k'ara maido mashi, baitin na k'arewa Laila tace ma Dj d'in ya maido baitin, yana maido shi duk aka maida hankali kan su Laila da Jidderh harda sauran k'annansu da wasu yan uwansu suka shiga fad'in yayi mata har saida suka ba Haisam d'in dariya Fatuu ma haka duk kunya ta rufe ta, lokacin da baitin ya kusa zuwa k'arewa kawai sai gani sukai ya bi harda nuna ta, wani irin ihu aka sa Fatuu ta 6oye fuskarta tana dariya, sosae abun yaba mutane nishad'i, Hajiya Zainab ce ta mik'e tana murmushi Momy ma ta mik'e suka nufi gaban Security detail d'inta na biye dasu hannunta ruk'e da jakar ta, wurin su suka je ta mik'a ma security d'in hannu ta bata jakarta, bandir d'in yan dubu dubu ta fiddo guda biyu haka Mom ma su ta fiddo daga cikin jakarta nan fa suka fara masu ruwan nera, ai kamar sun bud'e k'opa sauran manyan bak'in ma duk suka mik'e suka nufi gaban ai masu kid'an ganga na ganin haka ba 6ata lokaci suka hau bugun gangunan su suna wasa manyan matan nan fa Hall ya karad'e kid'a ko ta ina abun sai ya ba mutane ma dariya, Laila ce tayi ma Dj magana sannan ya kashe nashi, Laila ma lik'in ta fara masu Jidderh ma saurayinta ya fiddo bandir d'in d'ari biyar biyar ya bata taje haka su Nameer ma, daga wurin lik'in su Her Excellency da Mom dasu Aunty sauran manyan bak'in duk tafiya sukai, nan aka cigaba da rawa ana lik'i, wai ashe haka Laila da Jidderh suka iya rawa harda kama Haisam suna yin rawar, Yadikko ma saida taje ta amshi canjin yan d'ari biyu biyu tayi ma d'iyarta lik'i koda Fatuu ta ganta rungume ta tayi, gwaggo dai bata yi ba Saboda kunya tana zaune sai dariyar farin ciki take, Kawu Amadu da Tk da Nameer ma duk saida suka yi, Haulat ma saida taje tayi canjin yan d'ari biyu taje tayi haka Saude ma Hajiya dai dama bata zo ba, rud'ewa Fauzy tay tana son yin lik'in amman bata da ko sisi duka yan kud'inta dasu ta siya takalma da jaka da mayafi da zasu zo, tana ganin Aunty Mareeya ta nufo cikin hall d'in ta gama lik'in nata da sauri ta tare ta kaman zata yi kuka tace mata don Allah ta bata kud'i itama taje tayi, wani kallo ta mata tace wllh bata da kud'in da zata bata itama wanda tayi k'arfin hali ne kawai, komawa tayi ta zauna jiki a mace Zainab ce tace mata tana da yan kud'i suje suyi canjin ko d'ari biyu biyu ne, girgiza mata kai tayi tace taje tayi kawai, ba yadda bata yi ba amman tak'i k'arshe ta tashi ta tafi ita, takaici duk ya kama Fauzy abu goma da asirin, ga Vedio ta kasa yi Saboda wayarta data kwankwatse bata iya fiddo ta a wurin ga rashin kud'i, k'arshe kife kanta tayi saman table d'in jin tana niyyar yin kuka, bata dad'e da kife kan ba taji ana mata sallama, d'agowa tayi ta kalli mai sallamar wanda d'aya daga cikin ma'aikatan dake hidiman Abinci ne, gaida ita yay da d'an alamun mamaki ta amsa mashi kawai sai gani tay ya Mik'o mata kud'i bandir d'in yan dubu dubu guda biyu dubu d'ari biyu kenan, ce mata yay gashi aka ce ya kawo mata taje tayi lik'i, waro ido tay da alamun Al'ajabi ta tambayi waye yace a batan, nuna mata saitin da su Sameer suke yayi yay mata kwatance wanda ya badan don ya juya kan shi yana a Hakimce iya sumar shi kawae suke iya hangowa, jimm Fauzy tay saida ya k'ara ce mata gashi sannan a tsorace ta amsa ya juya ya tafi, bin kud'in tayi da kallo kafin ta kai duban ta kan su Aunty Mareeya dake ta hira basu ma lura da abunda ke faruwa ba, a hankali ta juya ta kai idanunta kan Sameer ta bishi da kallo ji take kamar ta je ta maida mashi saidae tsoro bazai barta ba, tana haka kwatsam ta ga ya juyo ya kalleta suka had'a ido, wani mugun kallo yay mata ya janye ido ya koma yadda yake, ba shiri ta mik'e hannun ta ruk'e da kud'in ta nufi gaban hall din a d'arare, koda tazo saitin su ta kai idon ta kanshi bai ko kalleta ba, tana zuwa ta shiga yin lik'in bayan bandir d'aya ya k'are ta bud'e d'ayan ta raba biyu ta mik'a ma Zainab data saki baki tana bin ta da kallon mamaki, cikin makad'an ne wani yazo ya tambayi sunan Fauzy ita bata san dalilin ba ashe wak'e ta zasu yi kaman daga sama taji ana angaida Hajiya Fauziyya mai ruwan naira har bata san lokacin da tasa dariya ba tana d'an kare fuska, kirarin da ake ma Fauziyyar ne ya jawo hankalin Aunty Mareeya ta Ankara da lik'in dubu dubun da Fauzyn ke yi,

wani jiri Fatuu taji yana niyyar kwasarta da sauri ta kai duka hannuwanta ta kama jikin Haisam, kallon ta yay ganin yadda take lumshe ido yasa shi tambayarta tana lafiya ta d'an yamutsa fuska ta kai hannu ta dafa gaban kanta a hankali tace mashi jiri take gani ba shiri ya kamata ya fara k'ok'arin barin wurin da ita wad'anda suka ankara suna tambayar lafiya yace masu eh, su Laila ne suka cigaba da yin rawar ya koma saman da ita, bayan ya zaunar da ita shima ya zauna cike da kulawa ya tambayi har yanzu tana ganin jirin, d'an murmushi tay ta girgiza mashi kai a hankali tace ya bari yace ta tabbata kodai su tafi gida still da murmushi tace mashi kada ya damu tasan tsayuwar da tayi ne yasa, Fauzy na son yin rawa amman ta kasa Saboda Sameer duk da bata san ko yana kallonta ba, bayan ta gama yin lik'in nufar komawa tay cikin hall d'in idon ta a k'asa, tana zuwa saitin Sameer ta saci kallon shi karaf suka had'a ido da sauri ta janye idon, tana zama a wurin zaman su Aunty Mareeya ta nufo ta da sauri har tana bugewa da kujera, zama tay a d'aya daga cikin kujerun ido a waje tace "Ke, ina kika samu kud'i haka da kikai lik'i har ana Wak'e ki?" murmushi tay tace mata Allah ne ya bata, wata uwar harara ta zabga mata tace zata gaya mata gidan uban wa ta same su ko kuwa, tana dariya tace mata wani ne ya bata, k'ara zabga mata harara tay tace wani wa, satar kallon Sameer tay sai sumar kan shi ta hango, maido idonta tay kan ta tace mata mutumin jiya ne ya bata, washe baki Aunty Mareeya tay a k'agare tace mata yana ina Fauzyn tay d'an jimm kafin tace mata ya fita bayan ya bata kud'in,

"Da alama dai Addu'a ta zata amsu, koma har yace yana son kin?" dariya Fauzy tay ta girgiza mata kai, tace ai duk aje a dawo in kaga kare na sunsunar takalmi to d'auka zai yi, tambayarta tayi har nawa ya bata tayi lik'in ta fad'i mata, zaro ido tay tace "ba dai duka kika lik'a ba??" Kai ta d'aga mata kafin tace duka, bud'e baki tay alamar Al'ajabi tace "amman dai ke anyi shashasha wllh taya zaki je ki lik'a duka wannan uban kud'in ba tare da kin rage ba, maimakon ma ki saka bandir d'aya a jaka ki lik'a d'aya" fuska d'aure ta k'arasa Maganar, ce mata tay ai lokacin yana kallon ta fa taya zata d'au wasu Aunty Mareeyar tace eh to gara da bata d'auka ba kada yay tunanin tana da son abun duniya gara abi komai a hankali ya shigo hannu ita dai Fauzy dariya kawai take.

Sai wuraren k'arfe sha biyu da wasu mintuna taron ya fara tashi, Kusan duk an tafi wasu daga cikin Abokan Haisam d'in ne suka rage su Abbas da Najeeb sai Na'eem Salim ya tafi haka Sameer ma tuni ya tafi, Aunty Laila bata tafi ba tana waje tana k'ok'arin ganin an maida kowa Nameer ma bai dad'e da tafiya dasu Fauzy ba, su Abbas suna tsaye a sama inda su Fatuu suka zauna Haisam ma na tsaye tare dasu suna magana, Laila ce ta lek'o cikin hall d'in ta sanar dasu kowa ya tafi fa Haisam ya d'aga mata kai, Abbas ne ya kalli Fatuu dake zaune yace "Mom Zarah an sha gajiya ko" d'an murmushi tay Najeeb ya kai idon shi kanta suka had'a ido shima d'an murmushin yayi mata, Kallonta Haisam yay yace ta tashi su tafi ta d'aga mashi kai, tana mik'ewa ta fara ganin jiri da sauri ta kai hannu ta dafe goshi bakin ta a d'an bud'e, wani irin duhu ta fara gani lokaci guda ta fara fita hayyacin ta, Abbas ne ya kai idon shi kanta yaga halin da take ciki da sauri ya furta "Mom Zarah lafiya??" gaba d'aya suka kai idon su kanta ko kafin suce mata wani abu gaba d'aya ta tafi zata fad'i cikin zafin nama Haisam ya tareta ta fad'a jikin shi, cikin tashin hankali ya shiga fad'in "Baby! Baby can you hear me? Mike faruwa?" tun tana lumshe ido tana bud'e su har ta k'arasa rufe su baki d'aya............

*ASM 083*

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
Chapter 48 · 0% Book details