← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 190 OF 211

Sashe 190

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

A kwana a tashi ba wuya har gashi shekara guda da hawan su President Ali Washegarin da akayi bikin murnar cika shekarar aka buɗe katafaren Companyn Haisam wato HAIFAT TechWorld, Kamfani ne da zai rinƙa ƙera kwanfutoci da saida bangarorinta da building softwares products da kuma Internet services daban daban da Online Services tare da kuma Consulting Services, sosae ginin kamfanin ya ƙeru yana da bangarori daban daban harda elevator ke akwae da zai kai mutum can sama abun sai dai ace Ma sha Allah, Mutane da dama ne suka halarci bikin buɗe shi ciki harda Mahaifin Haisam ɗin da manyan ƙososhin Gwamnati harda na wasu ƙasashen makwabta sannan ta bangaren danginsu kowa yazo har su Gwaggo harda Baffan Fatuu da Yadikko haka yan uwansu yan Ethiopia su Hajiya Zainab da Sameer harda Fauzy tare da twins ɗinsu da suka girma abun sai dai ace tubarkallah, abokan aikin Haisam ma turawa duk sun zo ciki harda waɗanda ya ɗauka zasu yi aiki tare gaba ɗaya duk wani masoyin Haisam da Abokan shi suna a wurin harda su Abbas da Najeeb da Saleem, ba ƙaramin mutane aka haɗa ba kowa yayi shiga ta alfarma kar ma su Mom suji su Fatuu ma ansha rantsattsan leshi iri ɗaya ita da Fanan wuya da hannu sun sha danƙararrun gold Haisam ma yasha bugaggun fararen suit sai necktie baƙi haka ƙafafunshi na sanye da dakakkun baƙaƙen cover suma abokan aikin nashi duk suit ne a jikinsu, yaran su gwanin burgewa duk sun girma su Twins yanzu shekararsu ukku da watanni amman sai kace sun fi hakan don suna da tsawo da kuma kauri suma suna sanye da suit na yara Esha kuma shekarunta biyu itama tana sanye da ƙananun kaya riga da wando an raba mata baƙar sumarta biyu ta saukko har ta wuce kafaɗarta kunnanta na sanye da barimar diamond da yan hannu ba ƙaramin kyau yaran sukai ba duk wanda ya kallesu sai ya ƙara yan jarida duk sun zagaye wurin suna ta aikin ɗaukar rahoto, bayan jin bayanai da suka danganci sabon kamfanin daga bakunan wasu masu ruwa da tsaki a kamfanin ciki harda Chief Executive Officer (CEO) wato Haisam da Mr President da wasu turawa a tare Haisam ɗin da Fatuu da Fanan suka yanka ribbon ɗin da aka zagaye ƙopar shiga cikin kamfanin mutane suka sa tafi ji kake "raf...raf...raf...) wasu suka shiga faɗin "Behind every Sucessiful Man there is woman or women" duk akasa dariya kafin akai bismillah suka sa kai, ginin bene ne hawa ukku akwae Ofisoshi daban daban da bangarorin gudanar da aikin kamfanin ko ina an zuba nagartattun furniture da suka dace da wurin wani abun ma sai Office ɗin Haisam wata daula ce guda akwae kuma ɗakin taro wanda aka sa haɗaɗɗan zunguren tebur aka kewaye shi da kujeru mahaɗin shi, haka akai ta zagayawa wurare ana ɗaukar hotuna da Vedios Mutane sai yabo da sa Albarka suke yan jarida nata yi ma mutanen tambayoyi ciki harda su Fatuu aka tambayesu irin farincikin da suke ciki, bayan an gama duba ko ina saida akayi addu'o'i sannan aka fita daga nan kuma Villa aka nufa don yin lunch event, komai dai ya ƙayatar an ci an sha anyi hani'an sai fatan Allah ubangiji yasa ma kamfanin albarka ake, a ranar kusan kowacce tashar Tv saida aka nuna bikin buɗewar haka Social media Maganar sabon kamfanin kawai ake da gidajen radio ana tallata irin ayyukan da kamfanin zai rinƙa yi har da tashoshin wasu ƙasashen an nuna dasu bbc, a ranar da daddare Khalid na zaune a falon gidanshi yana kallon bikin buɗewar a NTA, lokacin da aka nuno Fatuu na magana da turanci tana murmushi shima ɗan murmushin yayi saidai nashi yafi kama dana takaici don kuwa shi yasan yayi babban rashi kuma har abada bazata fita a ranshi ba, matarshi Hafsat ce ta dawo cikin falon daga kwantar da ɗiyarsu Zarah bayan ta zauna ya nuna mata Fatuu cikin Tv ɗin yace mata wannan itace Fateema, kallon Tv ɗin tayi kafin ta juyo ta kalleshi da alamun rashin fahimta tace mashi wace Fateema yay shiru kawai tana ta kallonshi can yace mata ta garinsu yana faɗin hakan ta gane don tasan labarin da ita zai aura aka fasa saidai bata san dalilin fasawar ba, maida idonta tayi kan Tv ɗin lokaci guda taji Fatun ta burgeta ta juya da ɗan murmushi tace mashi tana da kyau sosae yay ɗan guntun murmushi kawai bai ce komai ba can sai ya miƙe ma ya nufi hanyar Bedroom ta bishi da kallo.

Bayan buɗe kamfanin ranar Monday aka fara aiki a cikin shi, a yadda Haisam ya shirya zasu ɗan daɗe anan daga baya sai su koma America suyo parking ɗin dawowa Nigeria gaba ɗaya dama ya aje aikin kamfanin da yake acan saidai ba kwata kwata ya daina aiki dasu ba akwae wanda zai cigaba da yi masu sannan shima akwae aikin da daga can za'a rinƙa yi mashi a Companyn shi, bayan wata biyu akayi bikin Jidderh da Saurayinta Sadeeq ɗan Minister wanda bayan hawan Senator Ali kujerar shugabanci ya sake ba Mahaifin nashi muƙamin Minister, ba ƙaramin shagali aka sha ba auran ɗiyar shugaban ƙasa da kuma ɗan Minister wanda anan Abuja aka ɗaura ya kuma samu halarta manyan mutane daga ko ina ciki da wajen ƙasar nan sai fatan Allah ya bada zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba. Tuni aiki ya kankama a kamfanin Haisam anata neman aiki bayan wata ukku da buɗeshi lokacin wata guda da yin bikin Jidderh suka koma America, sati biyu sukai suka dawo acan aka baro Nameer da Mino sai sun gama karatunsu nan da shekara ɗaya da wasu watanni suma zasu baro can, Bayan dawowarsu Haisam Nigeria a yadda ya tsara zasu zauna a gidanshi ne, dama duk mazan gidansu kowa yana da gida da Dad ɗinsu ya mallaka masu saboda ba zaune suke ba dundundun yasa basu zauna acan ba suke zama a gidansu in sunzo Abuja, shi Nameer wanda yake zaune inda aka kai Mino shine nashi shima Haisam nada nashi shima a Asokoro saidai bayan dawowar tasu Dad ɗinsu yace mashi su fara zama anan gidanshi inda suka baro suka koma Villa don kar a bar gidan hakanan in aka ƙara wasu shekaru sai su koma nasu, hakan aka yi anan gidan suka zauna duk da yayi masu girma sosae, bayan dawowar su bada daɗewa ba Fanan ta samu aiki a National Hospital Fatuu kuma Haisam yay mata magana kan tafiyarta ƙasar india yin karatun Medicine amman sai tace mashi tunda anayi anan kawai ya bari sai tayi nan ba sai ta tafi wata ƙasa ba, ta yanke hakan ne don bata son yin nisa dashi yace mata amman karatun nan zai iya mata wahala tace lafiya lou in dai za'a koya mata to zata iya ya amince da hakan dama shima kawai don ya cika mata burinta ne zai barta taje India amman ba don yana son yin nisa da ita ba, cikin sa'a ta rubuta Jamb kuma points ɗinta ya kai yadda ake so don karatun likitancin, ba tare da wata wahala ba ta samu Admission a ABU Zaria Haisam ya kama mata gida mai kyau a zariar harda Security aka aje mata sannan tasa Iya ta samo mata mai aiki yar'uwarsu wadda dattijuwa ce daga can Daura suka zauna tare, lokacin data fara karatun tayi ma Haisam magana kan yasa akawo mata motarta daga Katsina amman sai yace tunda Amadu ke amfani da ita ta bari za'a kawo mata wata daga Kaduna hakan kuwa akai,
Chapter 190 · 0% Book details