← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 183 OF 211

Sashe 183

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Over my dead body.....!!! Wllh bazaki auri wannan dangin ƙarnin ba, anya ma kuwa kina cikin hankali ki...Not at all, Farha dana sani bazata ta6a son wani ɗan wannan Family ɗin ba so kuma na aure there must to be something behind all this..." har huci take tana Maganar cikin kuka Farhar tace ita Wllh itace kuma shi take so ai talaka da mai kuɗi duk ɗaya ne a wurin Allah aikuwa tun kafin ta rufe baki Hajiya Maryam ɗin ta yunƙura tare da kai hannu zata maketa da sauri ta goce tare da miƙewa ta nufi Dad ɗinsu ta faɗa jikinshi tare da ƙanƙame shi tana kuka tana faɗin ita Allah she will not marry Emran don bata son shi Kamal take so shi zata aura, aikuwa Mom ɗin ta ƙara yin kukan kura zata kai mata bugu Dad ɗin ya tare ta yana girgiza mata kai yace abi komai a hankali kada ta ji mata ciwo a fusace tace ai gara ta lahanta ta tunda ta raina mutane bata da hankali har su zata zo ma da wannan Maganar to in ma bata cikin hankalinta ne gara tun wuri ta dawo cikin shi don matuƙar tana raye bazata ta6a auren shi ba har taya ma aure zai yuwu tsakaninsu ai kalar zaren ba kalar yadin bane, ɗago kan Farhar Dad ɗin su yay yana kallon fuskarta da tayi jage jage da hawaye ta sigar lallashi yace mata ba gara ta auri Emran ba shida ya gina rayuwar shi yana da komai wannan da take so tace yanzu yake cikin yin karatu yaushe ya gama har ya samu aiki tunda ba yadda za'ai suyi auri bai da hanyar samun kuɗi, cikin muryar kuka tace ai yana yin business Dad ɗin ya tambayi wani irin Business tace suna da provision store a jikin gidansu tun kafin ta rufe baki cike da takaici Hajiya maryam ta kai hannu ta ciro hular kanta ta jefa mata a fuska Farha ta fashe da kuka tare da miƙewa ta nufi hanyar Bedroom tana tafiya tana bubbuga ƙafa tana faɗin ita Wllh shi zata aura itama Sis Fanan ba wanda take so aka bata ba cikin zafin nama Hajiya Maryam ta yunkura zata bi bayanta da sauri Dr ya riƙo hannunta ta juyo ta kalleshi tana huci kamar zakanya ya girgiza mata kai tare da yi mata alamar ta zauna, bayan ta koma ta zauna cikin kwantar da murya ya fara lallashinta tare da nuna mata komai a hankali yakamata a bi shi yaro ɗan lallashi ne in ta kwantar da hankalinta cikin rarrashi da kalamai sai taga tayi nasara akanta, haka ya dingi kwatanta mata har ta ɗan saukko ta miƙe tace bari ta sameta shima ya miƙe suka nufi ɗakin Farhar, lokacin da suka shiga tana saman gado ta kife fuskarta sai rizgar kuka take kai kace an faɗi mata saƙon uwarta ta mutu ne, a bakin gado duk suka zauna cikin kwantar da murya Hajiya Maryam ɗin ta kira sunanta shiru bata amsa ba saida ta ƙara sannan cikin kuka ta amsa tace ta tashi zasu yi magana ta fara ƙoƙarin ɗagowa idanunta har sunyi ja, zama tayi tana cigaba da yin kukan Mom ɗin tasu ta kai hannu tana goge mata tana faɗin ya isa, bayan ta ɗan tsagaita ne ta tambayeta yadda akai suka haɗu da Kamal ɗin cikin disashshiyar murya tace mata a wurin bikin Ya Nameer ne ta taho zata je yin liƙi shine ya bugeta bai gani ba har purse ɗinta ta faɗi ya bata haƙuri ya ɗaukko mata to tun daga nan taji ya burgeta daga baya ne tasan shi Yayan Fatuu ne har suka yi exchanging phone number suka fara gaisawa daga haka suka shaƙu shine ma dalilin daya sa taje bautar ƙasa Katsina, wani murmushin takaici Mom ɗin tayi tace "i know, wannan ba yin kan ki bane asiri ne" wani kallo Farhar tayi mata Hajiya Maryam ɗin ta ɗaga mata gira cike da tabbatarwa tace yess asiri ne ke ɗawainiya da ita Farhar tace amman shi ai bai santa ba ko sai ranar suka fara haɗuwa taya zata ce asiri yay mata tana murmushi tace mata ai su dama mutanen daji irinsu da an haifi yaro ake tsafe jikinshi don ya kasance yadda ake so to su tana jin na asirin nasara akai masu wannan dalilin ne yasa har Ƙanwarshi tayi nasarar auran Haisam ba don ta kai matsayin ya aureta ba kuma ya kasa sakinta haka Nameer ma shima abun ya faɗa kanshi yana ganin ƙanwarsu yaji yana sonta to itama kusan hakan ne, shiru Farha tay da alamun maganar ta ɗan yi tasiri a zuciyarta ta shiga tunanin ko shiyasa lokacin daya bugeta ta kasa yi mashi faɗa sai ma ji tay ya burgeta ko asirin ne ya shigeta can kuma wani bangare na zuciyarta ya shiga raya mata amman da asirin ne miyasa tunda suka haɗun bata ji tana son shi ba sai daga baya kuma koda ta furta mashi tana son shi farko bai amince ba kuma yan gidan su ma basu amince ba, koda ta faɗi ma Hajiya Maryam cewa itace fa ta fara cewa tana son shi kuma yangidan su da suka ji basu amince ba cewa sukai su haƙura gudun matsala sai cewa tay ai duk dubara ce sun san cewa sun riga sun asirce ta dole bazata iya haƙura dashi ba, shiru Farha tayi tana nazarin maganar a cikin ranta wani bangare na zuciyarta ya ƙi gasgata zancen asirin wani bangare kuma na son gasgatawa, lokaci guda ta fara ganin fuskar Kamalu ɗauke da ƙayataccen murmushin shi da maganarshi mai daɗi wata zuciyar ta raya mata yanzu shikenan sai ta haƙura dashi ƙilan ma Mom ɗin nata duk daɗin baki ne tayi mata ba wani abu ba, kamo hannunta Hajiya Maryam tay tace kada ta bari asirinsu yay tasiri akanta tazo taƙi mai sonta da gaskiya wanda zai treating ɗinta kamar Queen wanda zai mata duk abunda take so wannan kuma ƙarshe zata yi dana sani ne don ba iya ruƙeta zai yi ba kawai zai yi auren jari ne da ita don haka ta cire shi a ranta, shiru Farhar tayi tana kallonta yayin da zuciyarta ke ƙara tabbatar mata da wayau ne Mom ɗin nasu ke mata in ta rabu da Kamal kanta tayi mawa dama danginshi ba so suke ba dama, wani irin son Kamal ɗin ne taji ya taso mata cikin yamutsa fuska tace ma Mom ɗin ita ta tabbatar ba Asiri bane Allah ne ya saka mata son shi ita dai shi take so Wllh yanzu bata jin son Emran, wata uwar harara Mom ɗin ta wurga mata tare da sakin hannunta a fusace tace to tunda ita keda kanta ai sai ta aureshi ta gani daga haka ta tashi fuuu ta nufi hanyar barin ɗakin Farhar ta fashe da sabon kuka tana buga katifa Dad ɗinta ya matsa tare da jawota jikinshi ya rungumeta yana faɗin shikenan tayi shiru kada taja ma kanta ciwo cikin kuka take faɗin "Dad i love him, help me marry him pls" shiru yay yana shafa bayanta shi in don tashi ne indai har yaron yana da hali mai kyau to zai amince ta aure shi don mutum ne mai tsananin son yaranshi dama kuma haka turawa suke da son yara gashi suna ba yaran su yanci sam bai son abunda zai tada masu hankali ko ya 6ata masu rai shiyasa duk abunda suke so to yana son shi, jin ta ɗan lafa da yin kuka yasashi ɗagota yace ta kwantar da hankalinta indai har yaron baida matsala to yana tare da ita zai yi bakin ƙoƙarinshi ya ga ya taimaka mata ta samu abunda take so da sauri tace mashi wllh baida matsala ya kira Hajiya ya tambayeta yana da ilimin addini kuma yana da ƙokari gashi yana da ƙoƙarin neman na kan shi sam baida kwaɗayi don ko abu tayi mashi da ƙyar yake amsa, murmushi Dad ɗin yayi yace yayi kyau ya tambayi tana da hoton shi ya gani da sauri tace eh ta juya tana laluban wayarta, bayan ta ɗaukko ta shiga gallery ta dawo jikin Dad ɗin ta shiga nuna mashi hotunan Kamal wasu tare sukai wasu kuma shi kaɗai yana murmushi yace yana da kyau ta ɗaga kai ya sake cewa amman kamar ta girmeshi a shekaru tace a'a ya ɗan girmeta yace Ok yana son ta kwantar da hankalinta duk abunda Allah ya ƙaddaro shine zai faru ta ɗaga mashi kai,

Hajiya Maryam na fita ɗakinta ta nufa a zuciye tana shiga ta nufi bakin gado ta zauna ta shiga cize baki abun ya matuƙar daure mata kai wai ace Farha data sani itace zata ce tana son yaron wannan dangin tabbas bata tunanin yin kanta ne, a fusace ta kai hannu ta rarumo wayarta ta shiga kiran Hajiya bayan tayi ringing Hajiyar ta ɗauka murya ciki ciki ta gaishe da ita ta amsa daga haka tayi shiru Hajiyar tace ya akai ne taji muryarta wani iri ai kaman tana jira ta miƙe tsaye yadda zata ji daɗin kora bayani ta shiga faɗin wai Farha ce tazo masu da wani banzan zance na bata son wanda ke sonta ɗan dangin shanun nan take so ashe ma dalilin zuwan ta wurinta kenan yin service duk saboda shi ne, Murmushi Hajiya tayi tace ai tasan da Maganar suna son junansu, da tsananin mamaki Hajiya Maryam ɗin tace amman shine kuma ta ƙyale su bata hana abun ba,

"To akan mi zan hana Maryam, yara suna son junansu",

"Saboda bai kai yayi soyayya da ita ba Hajjaju", yar dariya Hajiya tayi "saboda shi ba mutum bane ko mi?",
Chapter 183 · 0% Book details