← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 172 OF 211

Sashe 172

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

"Yauwa ka shiga ciki kace ga baƙon ya iso" ya faɗa still da murmushi akan fuskarshi, da alamun rashin Fahimta Amadun yace wa zai faɗi ma hakan Kawu Manin yace mashi ita mai gidan zaije yace ma ga baƙon da Hajiya tayi mata magana yazo da sauri ya amsa da to ya juyo ya buɗe shagon ya fito, lokacin daya shigo gidan Gwaggon na cikin ɗakinta tun bayan data yi waya da Hajiya dama tana kan abun salla ne bata tashi ba, da sallama ya shigo ta amsa tare da juyowa ta kalleshi ya sanar mata zancen zuwan baƙon tay ɗan jimm kafin a hankali tace mashi ya shigo dashi falo yace to ya juya, shiru tayi a ranta ta shiga tunanin to wane baƙo ne kuma wace irin gaisawa zasu yi kaman yadda Hajia tace, tana jin lokacin da suka shigo Kawu Manin yay sallama, bayan ya shigar dashi yazo ɗakin ya sanar mata gashi can a falo kai kawai ta ɗaga mashi ya juya ya tafi, miƙewa tayi duk tayi sukuku ganin Hijab ɗin jikinta lafiya lou dama gogagga ce ta ɗaukko tayi sallar da ita ta nufi ƙopar fita, lokacin data tunkari falon gabanta har ɗan faɗuwa yake, da sallama ta saka kai cikin falon ƙamshin turaren shi ya bugi hancinta yana zaune akan 2 seater ya ɗago yana kallonta da murmushi ya amsa mata sallamar suna haɗa ido ta gane shi ta nufi kujera mai mazaunin mutum ɗaya daga can gefen tashi ta zauna idon shi akanta yace mata "Barka da Fitowa", ɗan murmushi tayi ta amsa tare da gaishe dashi yana ta murmushi ya amsa, kanta ne ya ɗaure ganin shine don bata ta6a zaton shi zata gani ba matsayin baƙon don tunda tasan Hajiya tasan shi yana zuwa gidan matsayin ƙanin Hajiya tsawon lokacin kuma bai ta6a zuwa nan gidan ba sai yau, miƙewa tayi ta nufi Fridge ya bita da kallo bayan ta buɗe ta ɗaukko lemu da robar ruwa tare da glass cup bayan ta rufe tana juyowa suka haɗa ido ta maida nata ƙasa ta nufo inda ɗan table yake ta ɗaura sannan ta ɗaukeshi ta matsar dashi gabanshi, buɗe lemun tayi ta zuba a cikin cup ɗin ba tare data kalleshi ba tace gashi yasha yana murmushi ya furta "Shukran" ɗan murmushi tayi ta koma inda ta taso, ɗaukar cup ɗin yayi ya kai baki saida ya kur6a kamar sau uku sannan ya aje tare da furta Alhamdulillah ya ɗaura idon shi kan Gwaggo dake kallon Carpet yace "Fatan na same ki lafiya, ya gida ya yara ya aiki kuma" ɗago ido tayi ta kalleshi da ɗan murmushi ta amsa mashi da lafiya lau Alhamdulillah shima ta tambayi ya nashi iyalin da aiki yana sakin ƙayataccen murmushi ya amsa mata, shiru suka yi can ta miƙe tace bari a kawo mashi abinci da sauri ya dakatar da ita yace lemun ma ya isa a ƙoshe yake ta koma ta zauna,

"Yauwa, kamar yadda Hajjaju ta sanar maki ita ta turo ni don mu gaisa da juna kuma tunda mu ba yara bane nasan kin gane wace irin gaisawa ake nufi, ni dai na gan ki kuma kin mani don haka in an amince man Aure nike son muyi tunda duk naji duk wani abu dangane dake nima kuma in kina son sanin abunda ya dangance ni zaki iya yi ma ita Hajjaju magana da fatan za'a amince man" tunda ya fara Maganar ta sunkuyar da kanta har ya gama ta kasa ɗagowa balle tace mashi wani abu, ganin taƙi yin magana yasashi ce mata ita yake saurare ta taimaka ta bashi amsa, gaba ɗaya ya ɗaureta ta rasa amsar da zata bashi don sai taji bata iya ƙin amince ma buƙatar daya zo da ita kodan Hajiya gashi ita ta cire sake yin aure a ranta, a hankali ta ɗago suka haɗa ido tayi saurin kawar da nata kafin tace mashi tana buƙatar yin shawara ya ɗan bata lokaci, yana murmushi yace "Har sai anyi shawara kuma, to kodai ban samu kar6uwa bane?" kallon shi tayi da ɗan murmushi tace a'a kawai tana buƙatar yin shawara ne tunda tana da babban yaro, ɗan buɗa ido yay yace "dashi za'ai shawarar kenan karfa yasa aƙi amince man don kinsan wasu yaran sukan taya iyayensu maza kishi" yar dariya tayi kawai,

"Yanzu har tsawon wane lokaci zan jira Hajiya" yay Maganar yana mata wani kallo da gani shima za'a dashi ta bangaren soyayya, tana murmushi tace malama dai ya wani ɗage gira yace "Ni Hajiya na gani" shiru tay kawai tana murmushi ganin ya kafeta da ido tace mashi ko mi kenan zata sanar mashi ya furta Ok bari ya bata lambar shi amman don Allah kada a ɗauki lokaci asa ya kasa samun natsuwa tace uhmm kawai, wayarta ya tambaya yasa mata lambar tashi ta miƙe tace bari ta ɗaukko tana ɗaki, bada jimawa ba ta dawo ta miƙa mashi wayar ya amsa yana murmushi ya ɗan jujjuyata yace "amman Hajiya sai naga kamar kinfi ƙarfin wannan wayar" murmushi tayi tace tafi jin daɗin amfani da irinta ne yace to amman ga na zamani ai sai a haƙura da tsohon yayi gaskiya yakamata a canza ta tace mashi tuntuni yara keson canza mata ita ce bata so,

"To ai yanzu sai aba maigida dama ya canza" da sauri ta kalleshi ganin kallon da yake mata yasa ta kauda fuskarta yace "na cika azar6a6i ko tun ba'a sanar dani matsayi na ba har na yanke hukunci, ayi haƙuri abunda rai ke muradi ne" juyowa tay ta kalleshi tana ɗan murmushi, lambar tashi ya saka a tata ya kira kafin yayi mata saving tashi ya miƙa mata yace gashinan ya saka mata Alhaji Mani ya tambayi ita kuma Hajiya wa zai saka mata tace Dije ya ɗan yamutsa fuska yace "Wannan na zamanin da ne bari in saka na zamanin yanzu Khadija ko kuma Khadijatul Khubra" Gwaggo bata san lokacin da tayi yar dariya ba shima ita yake yi bayan ya gama saving ɗin ya ɗago ya kalleta yace "to Hajiya Khadija ni bari in zo in wuce inada wani uzuri da zan aiwatar kafin na hau hanya sai naji daga gareki ina fata kuma za'a duba man inji abunda nike fatan ji" murmushi kawai take, miƙewa yay ya zura hannu cikin yan cikin babbar rigar shi ya fiddo kuɗi masu ɗan yawa ya ɗaura akan table ɗin yace gashi nan a ba ɗan shi da jikanshi, da sauri ta kalleshi tace don Allah ya barshi yana mata wani kallo yace bata ji waɗanda yace taba bane dole tayi shiru, tafiya ya fara yi zai fita daga cikin falon ta ɗan juya tana kallonshi har ya kusa ƙopa ya tsaya ganin zai juyo yasa da sauri ta kauda idonta tana haka taji muryarshi yana faɗin bazata raka baƙon nata bane tay ɗan jimm kafin ta kalleshi suka haɗa ido yana mata murmushi, jiki a sanyaye ta miƙe ya furta yauwa ko ita fa ya juya tana biye dashi, saida suka kusa ƙopar fita ya juyo yace to ya gode ta koma kada ya wahalar da Hajiya ta ɗan yi murmushi tare da yi mashi Allah ya kiyaye hanya ya amsa, falo ta dawo ta zauna kan kujera tayi jugum ta rasa ma tunanin da zata yi ganin abun take kamar ba'a gaske ba duk da ba yau aka fara zuwa neman aurenta ba wannan sai taji yayi mata girma sosae ba kamar daya haɗa da Hajiya, tana haka Amadu ya shigo da sallama ta ɗaga ido ta kalleshi ta amsa a hankali, nufo inda take yayi ya zauna a kujerar dake gefen tata ya ɗan yi shiru yana kallonta kamar mai nazarin wani abu ita kuma ta kauda idonta daga barin kallonshi,
Chapter 172 · 0% Book details