← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 113 OF 211

Sashe 113

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Da daddare bayan sallar isha gaba d'aya yan gidan harda Dad nan part d'in su Fatun suka zo lokacin tuni sunyi wanka tun da yamma Fatuu na sanye da doguwar rigar Atamfa haka yaran ma anshirya su cikin set na Overall ash sai hira ake kan su ana nishadi, anan falon nasu aka ci Abincin dare sai wuraren k'arfe goma sannan Mom tasa su Yasmeen suje su kwanta Saboda zuwa school da safe itama dasu Dad duk sukai ma su Fatuu saida safe ganin Jidderh bata tashi ba yasa Mom ce mata mi take jira ta tashi su tafe sai Allah ya kaimu kuma a dasa zaman jegon cikin yar shagwaba tace ita anan zata kwana, wani kallo Mom tayi mata tace to shi Habibyn ya kwana a ina da sauri tace ba ga part d'in shi can sama ba ita kuma sai ta kwana ta taya Fatuu raino Mom tace to bazata kwana ba in don raino ne shi ya tayata,

"wayyo Mom don Allah ki barni in kwana wllh banson in yi nisa da y'ay'ana, kuma ai da ana da cikin su nima ba a dakina take kwana ba to nima yanzu zan rama ma k'ura aniyarta ne" dariya Mom tayi tace wannan kuma ai ita tasa kanta ko, dole Mom tasata ta mik'e tace daga baya ta kwana amman yau ta k'yale su suyi rainon babies d'in su da kan su tana tura baki ta bita bayan sunyi masu saida safe, babba babba ne wato da alama Mom ta fahimci Haisam d'in na buk'atar ke6ewa da matar shi ko kuma tasan zai so hakan don tun bayan da aka sallamo ta d'akin bai kasance ba mutane ba, bayan fitar su Mom bin juna sukai da kallo suna murmushi ita dashi yana zaune akan side drawer jikin shi sanye da farin voile, mik'ewa yay ya nufi gadon ya zauna daga baki gefen Fatun still da murmushi akan fuskokin su cikin cool voice d'in shi ya furta "Mai jego" dariya Fatun tay kafin tace "Na'am Angon jego" shima dariyar yayi ya maida idanun shi kan jariran dake a nad'e suna bacci asaman gadon itama kai idonta tayi kan su suka cigaba da kallon su a tare kowa dad'i ya cika mashi ranshi can Haisam d'in yay sigh ya furta "I'm forever grateful ya Rabbi" yana rufe baki Fatuu ta furta "We're forever grateful our perfect Rabb" jinjina mata kai kafin ya k'arasa hayewa saman gadon ya kai hannu ya jawota jikinshi ya d'aura habarshi a saman kanta sukai shiru suna ta sakin k'ayataccen murmushi, a hankali taji ya tambayi ya jikinta ta bashi amsa da ba abunda ke mata ciwo ya d'aga kai, shiru sukai kowa yana jin sabon son dan'uwan shi na ratsa zuciyoyin su can ta d'aga kai ta kalle shi ta tambayi yaushe Aunty Fanan zata zo ya bata amsa da jibi ta jinjina kai, kasa janye idonta tayi suka zuba ma juna ido breathing dinsu na had'uwa, sun d'an d'auki lokaci a haka can ta hura mashi iska a ido ya d'an kikkafta idanun ta saki dariya shima yar dariyar yayi ya k'ara matseta a jikin shi tare da furta "I Love You Baby, I don't even know how to tell you how much I love you" d'aga ido tay ta kalle shi tare da kashe mashi ido d'aya cikin wani irin salo ta furta "I can't get enough of Your love Hubby" tana rufe baki kawai sai gani tay ya had'e lips d'in su, da alama dai Fatuu har ta manta da nakudar da tayi shiyasa ta biye mashi, sun d'an d'auki lokaci a haka kukan jaririn daya karad'e d'akin ne ya dawo dasu hayyacin su da sauri suka saki juna suna dariya Fatun nata fad'in yanzu fa bashi kad'ai keda lokacin ta ba ya k'ara fad'ad'a dariyar tashi, Adam ne ya farka yana kukan tare da kai hannu baki yana tsotsa alamar yunwa yake ji, daukko shi tay ta shiga kiciniyar feeding nashi ganin haka yasa Haisam cewa ko ya taimaka mata tace eh ya kai hannu ya ruk'e mata shi, nursing pillow dake a ajiye gefe da d'azun tayi amfani dashi ta d'auko har ta iya yadda Aunty ta nuna mata bayan ta daidaita shi ta fara feeding d'in nashi sosae ya kama yana sha Haisam yay k'uri yana kallon shi can ya kalli Fatuu da alamun mamaki yace k'arami dashi yana shan abu haka ta saka dariya ta shiga bashi labarin yadda tun a Asibiti ya fara sha da tsiyar da Aunty tayi mashi, yana cikin sha d'ayan ma ya farka yana kuka Haisam ya tambayeta shima ko yunwa yake ji tace k'ilan yace to yanzu ya za'ai ga wannan na sha yadda yay Maganar har saida ya bata dariya tace ya d'auke shi wannan ya gama yace Ok ya k'arasa hayewa gadon ya d'aukko shi, yana d'aukar shi yayi shiru ya shiga mamular hannu idanunshi ya bud'e su sosae yana kallon Fuskar Haisam da shima kallon shi yake yana mashi murmushi, saida Adam d'in ya gama suka yi musaya ta amshi Aliyun, ganin yadda shima yake sha sosae yasa Haisam d'in ce mata anya zata iya shayar dasu duka kuwa, tana dariya tace mi zai hana ba ita ta haife su ba yace to amman in suna sha haka ai zata rame sosae tace a'a indai tana ci tana k'oshi lafiya lou, shima saida ya k'oshi sannan ta cire shi bayan ta goge mashi bakin shi da d'an towel mai taushi ta fara kokarin canza masu diaper d'in jikinsu kamar yadda Aunty tace kar ta bari su kwana dasu, koda ta cire basuyi komai ba dama ruwan zamzam ake basu amman duk da haka saida ta canza komai da zata buk'ata na daga gefenta cikin dresser dinsu mai kyau, bayan duk ta canza masu ta feshe su da turaren su ta maida komai, ganin ta kwantar dasu a kan gadon yasa Haisam ce mata ba ga gadonsu nan ba tace tunda dare ne gara ta kwantar dasu nan koda zasu tashi da daddare yace Ok, gaba d'aya bin yaran sukai da kallo suna masu murmushi su kuma duk sun k'ura masu ido sai kace sun san su waye su abun gwanin sha'awa, sun d'an d'auki lokaci a haka kafin Haisam ya kalleta yace yasan bata rasa jin yunwa ko tace a'a bata jin wata yunwa ai taci Abinci sosae da daddaren nan kawai tea take so zata had'a tunda ga kayan nan yace Ok bari ya had'a mata ya tashi tana ta kallon shi da murmushi ta furta "You're the best husband ever" k'ayataccen murmushi ya saki tare da furta mata thanks, tea mai k'auri ya had'o mata da kanshi ya rink'a bata tana sha bayan ta gama shima ta matsa mashi saida ya had'a duk da yace mata a k'oshe yake, bayan sun gama ya tambayeta akwae abunda zai taimaka mata yana son yay wanka tace a'a yaje yayi kaya kawai zata canza, a tunaninta a nan zai wankan sai taga ya nufi k'opa yace mata bari yaje sama yayi sai ya dawo tace to, bayan fitar shi mik'ewa tayi har zata tafi ta tuna wani abu ta koma kan gadon, Addu'oi ta shiga yi masu tana tofa masu Adam har ya koma bacci sai Aliyu ne idon shi biyu tana murmushi tace mashi Mom zata je tayi shirin kwanciya ta dawo sai kace yana gane abunda ta fad'a yay mata k'uri da ido, wurin kayanta ta nufa ta fara cire kayan jikinta bayan ta gama ta d'aura towel saida ta dauki pad da pant da zata canza sannan ta nufi toilet bayan ta yafa gyale a saman kanta, bata jima sosae ba ta fito ta koma wurin kayanta, shiryawa tay cikin bakar nursing nightgown ta d'aura brown robe a sama ta saka hula akanta bayan ta gama shiryawa ta nufi gaban mirror kallon kanta ta shiga yi tana fesa turare a cikin ranta take raya wai yanzu nan ita mai jego ce tana ta murmushi har ta gama ta juya ta nufi gado shima d'ayan har ya koma baccin, hayewa tay taja duvet ta lullube su tare da kai hannu ta rungumosu su duka, bayan wasu mintuna sai gashi ya dawo shima yayi shirin kwanciya sai zuba k'amshi yake, saida ya rufe k'opar d'akin sannan ya nufi gadon ta d'ago tana kallon shi ya kunna lamp kafin ya nufi switch ya kashe hasken d'akin sannan ya nufi gadon, ta d'ayan bangaren ya hau ya fara yin Addu'a bayan ya gama ya d'an tufa bangaren su Fatun da jikinshi sannan ya kwanta yana facing Fatun ta d'an hasken da ke akwai ya hangota tana mashi murmushi shima ya fara yi mata daga baya bacci ya kwashe su.
Chapter 113 · 0% Book details