Sashe 9
A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wani lokaci ne dinner da ka ce?" Fahad ya tambaya yana kallonsa, faɗi masa lokacin ya yi tare da venue kafin Deen ya ce masa yana zuwa ya nufi cikin ɗakin, walk in closet dinsa ya shiga, bada jimawa ba ya fito hannunsa ɗaya jaye da suitcase kalar ruwan ƙasa da wata yar babbar jaka a ɗayan hannun masu kyaun gaske, gadon shi da ya sha gyara an shimfiɗa zanen gado mai kyau sai duvet mai laushin tsiya da aka rufe rabin gadon da shi gaba ɗayan su kalar kayan ɗakin ne suma wato ruwan madara, ɗaura akwatin ya yi saman gadon ya haye sama ya zauna, kallon Fahad ya yi ya ce masa ya zo ya gani, a nutse ya taso yana gyara rigarsa ya nufo shi, a ɗayan bangaren gadon ya zauna ta yadda sun saka akwatin tsakiya, buɗe akwatin ya yi wanda kayan sakawa ne cike a ciki, daddaɗan ƙamshi haɗi da na sabuntar kaya ne ya gauraye wurin, a tsanake yake fiddo da kayan yana nuna masa yana ajiyewa a gefe, bayan ya gama fiddo da kayan ɗayar jakar ya jawo itama ya buɗe ta, a ciki takalma ne ƴan ubansu tsadaddun gaske, akwai agoguna da turarurruka harda kayan shan iska da underwear na maza, bayan duk ya gama fiddo su ya kalli Fahad ya ce gasu nan nashi ne ya san duk za su yi masa tunda ya san size ɗin sa duk da ya ga kaman ya ɗan ƙara jiki ko ya daina motsa jiki ne, da murmushi Fahad ɗin ya ce masa yana yi, da zolaya Deen ya ce to cinye ma mommy abinci yake yi ke nan tun da ya ƙi ya yi aure, ƴar dariya Fahad ya yi kafin ya mayar da idanunsa kan kayan dake jibge a saman gadon ƙirar manyan kamfuna, ko ba a faɗa ba ya san kaya ne masu tsadar gaske, kallon Deen ya yi ya ce, "Miyasa zaka kashe kuɗi haka, kayan sun yi yawa ai." Shima yana murmushi ya bashi amsa,
"Ina da kuɗin ne, ko da bani da su zan nema don in siya maka." Ɗan faffaɗan murmushin jin daɗin maganarsa Fahad ya yi, har da irin hakan ke ƙara masu ƙaunar juna, shima Fahad ɗin ya na yi ma Deen alkhairi duk da ya san ya fi shi kudi sosai, ko lokacin da ya fara amsar albashinsa na farko sai da ya tura ma Deen wani kaso a ciki kuma Deen ya ji daɗin hakan. Hira suka ci gaba da yi zaune saman gadon gwanin burgewa, kana kallon su ka ga zaratan maza waɗanda hutu ya zauna a jikinsu.
Leemah na barin part ɗin Deen ƙasa ta sauka ta nufi ɗakinta ta shige, ɗakin ba laifi yana da ɗan girma akwai simple modern furniture, komai na cikin ɗakin kalar ruwan toka ne, kana ganin ɗakin kasan na ɗiyar masu hannu da shuni ne don harda tv stand kalar setin kayan dakin manne da madaidaiciyar plasma suna fuskantar gadon ɗakin. Kai tsaye toilet ta nufa don ta yi wanka bayan ta rage kayan jikinta, ba da jimawa ba ta fito ƙirjinta ɗaure da tawul da ya kawo mata tsakiyar cinyoyinta da suka bayyana jajur da su ko ɗan tabo babu, ba tare da 6ata lokaci ba ta hau shirya kanta. Bayan ta gama yin shafe-shafe ta gyara gashinta da yake da tsawo ga santsi, wurin ƙatuwar wardrobe ɗinta dake a jikin bango ta nufa don ta ɗauko kayan da zata saka, saida ta yi ruwan ido wurin zabar kayan da zata saka don kaya ne ciki gasu nan birjik iri- iri, ƙarshe wani baƙin lace mai adon fulawowi peach da ratsin golden ta dauko, kana ganin leshin ba sai ma an faɗi maka zai yi kuɗi ba yadda aikin jikinsa ya saƙu sosai, bayan ta saka kayan wanda fitted gown ce da ta kama jikinta daga ƙasa ta buɗe haka hannun rigar ma dogo ne daga ƙasan shi ya ɗan bude an yi ado da bakin leshin, wuyan rigar irin mai zagayayyar kwala ne, ta matuƙar yin kyau kayan sun amshi jikinta ta fito a ƴar matashiyar budurwa, duk da bata ida zama babbar budurwa ba alamun tana da diri mai kyau ya bayyana, dama jikin momynta ta biyo duk da a fuskarta akwai ɗan yanayin daddynsu amman ta fi kama da momynsu sosai, tana da tsawo sannan bata da jiki amman kuma ba siririya bace, daga yanayin jikinta akwai alamun da ta ƙara girma ko ta yi aure zata iya ƙara jiki, gaban madubi ta tsaya tana kallon kanta fuskarta ɗauke da murmushi ganin yadda rigar ta amshi jikinta, dama kayan sababbi ne bata ta6a saka su ba suna cikin kayan da aka yi masu saboda zuwan yayan su Deen, ko ƙananun kayan da suka je tarbar sa da su suma sababbi ne gal yau suka fara saka su, ɗan jujjuyawa ta yi ta kai hannu tana shafa hips ɗinta, ta ji daɗin ganin yadda suka fito, kai idonta ta yi kan ƙirjinta da suma sun fito ɗas duk da har da ƙarin bra da ta saka yasa suka cika, kallabin kayan ta shiga ɗaurawa bayan ta ɗaure gashinta da ribbom jelar ta sauka har wuce saitin kafaɗarta, tana cikin yin ɗaurin ta ji an buɗe ƙofar ɗakin, ta cikin madubin ta kai idonta wurin ƙofar, har sai da gabanta ya ɗan faɗi ganin mom ɗin su ce ta shigo,
Idonta akan Leemah dake ci gaba da yin ɗaurin kallabinta ta nufo cikin ɗakin, gefenta ta tsaya tana bin ta da kallo mai cike da mamaki, sai da ta kammala yin ɗaurin sannan ta juyo ta kalli mom ɗin na su da murmushin ƙarfin hali kan fuskarta ta furta, "Mom na yi kyau ko?" Bata amsa mata ba da alamun mamaki ta ce, "To wannan ɗin na minene?" Ta yi maganar tana nuna ta daga ƙasa har sama, ɗan tura bakinta da ya sha dark peach din jambaki ta yi da yanayin shagwa6a ta ce kwalliya ce kawai ta yi, wata uwar harara ta wurga mata da alamun 6acin rai ta ce, "Ke nan wanccan mutumin ki kai ma kwalliyan?" Bata rai Leemah ta yi, "Mom ni fa kawai na yi kwalliyana ne, kuma ai ba yau na fara yi ba ko."
Bin ta da kallo mom ta yi sheƙeƙe, fuska a yamutse ta ce, "Eh ba yau kika saba yin kwalliya ba, amman ba irin wadda kika saba yi ɗin ba ce ai kika yi. Wato dai zargin da nike yi a kan ki Leemah ya zama gaskiya ko! Idan ba akwai wani abu tsakanin ki da wanccan yaron ba uban miye to na yin kwalliya haka? Ko yayanki da ya ɗau tsawon lokaci bai zo ba sai yau baki yi irin wannan kwalliyar ba don tarbar sa, soyayya kike da Fahad ko!" Ta tambaya cikin kwatsa tsawa, tura baki Leemah ta yi rai 6ace ta ce, "Wai mom sau nawa zan ce maki ni ba soyayya muke yi da shi ba, kuma in ma soyayyar muke yi ai ba haramun bane tun da akwai aure a tsakanin mu..." Uwar tsawa ta daka mata ta ce, "Kar ma ki fara wannan tunanin wllh! In ma soyayya kuke yi to tun wuri ki datse ta idan ba haka ba zan datse ta da kai na, matuƙar ina numfashi ba zan bari hakan ya faru ba wllh, ai zaren bai yi daidai da kalar yadin ba, bai kai matsayin da zai iya auren ki ba!" Ta ƙarasa tana ɗan jujjuya kanta ta ƙanƙance idanunta, cikin ƙuna-ƙuni Leemah ta ce, "In haka ne, to ai kema mom ke da daddy zaren bai yi daidai da kalan yadin ba ko kuma ya aure ki, kuma ai ya Fahad bai da wani aibu yana da kyau kuma yana da aiki mai kyau sannan danginsu masu arziƙi ne, ke kuma ai dangin ku ba masu kuɗi bane amman a hakan suka amince dad ya aure ki, sai ke kuma zaki ce ba za ki amince ma wani nasu ya auri ɗiyar ki ba." Tana maganar tana ɗan ja da baya, da alama ta kashe bakin mom ɗin nasu, tsananin al'ajabin abun da Leemah ta faɗa ne bayyane akan fuskarta,
Cikin murya mai kaushi ta furta, "Leemah ni kike faÉ—i ma wannan maganar!" Ta faÉ—a tare da nuna kanta da yatsa,
"To ai gaskiya na faɗa ko mom, ba ta inda na fi ƙarfin ya Fahad, in ma don kina ganin daddynmu mai kuɗi ne shima ai daddynsa yana da kuɗi, ko da don kina tunanin dad ya fi abbansu kuɗi ne kin manta da cewa dad ɗin namu ƙanin mahaifinsu ne?" Wani kallon takaici mom take bin ta da shi ta yamutsa baki, Leemah na kikkafta idanu ta ƙara cewa, "In dai ina son shi shima yana sona sai mun auri jun...." Da sauri ta goce ma marin da mom ta kawo mata, tana huci ta furta, "To don ubanki, ko shi ɗanɗan ƙaruna ne baza ki aure shi ba don ba ɗan shaye-shaye na haifa ma ke ba! Sannan ko wadda take iko da ubanki bata isa ta sa ya aure ki ba balle shi uban naki! Gara ki dawo cikin hayyacin ki tun wuri." Tana ƙarasa maganar ta juya ta nufi barin ɗakin, ta san Leemah ba kunya ta ishe ta ba, in ta biye mata haka zatai ta saka ta hargowa tana ƙara ƙunsa mata bacin rai,
"In har Allah Ya ƙaddara shi mijina ne sai na aure shi, ba wanda zai iya hana hakan." Ta faɗa cikin tura baki, lokacin mom ta kama ƙofa zata fita ta tsinkayi muryar Leemah, juyowa tayi cikin sakin shu'umin murmushi ta furta, "We shall seee..." Daga haka ta fuce tare da rufe ƙofar da ƙarfi ta bada sauti.
"Ina da kuɗin ne, ko da bani da su zan nema don in siya maka." Ɗan faffaɗan murmushin jin daɗin maganarsa Fahad ya yi, har da irin hakan ke ƙara masu ƙaunar juna, shima Fahad ɗin ya na yi ma Deen alkhairi duk da ya san ya fi shi kudi sosai, ko lokacin da ya fara amsar albashinsa na farko sai da ya tura ma Deen wani kaso a ciki kuma Deen ya ji daɗin hakan. Hira suka ci gaba da yi zaune saman gadon gwanin burgewa, kana kallon su ka ga zaratan maza waɗanda hutu ya zauna a jikinsu.
Leemah na barin part ɗin Deen ƙasa ta sauka ta nufi ɗakinta ta shige, ɗakin ba laifi yana da ɗan girma akwai simple modern furniture, komai na cikin ɗakin kalar ruwan toka ne, kana ganin ɗakin kasan na ɗiyar masu hannu da shuni ne don harda tv stand kalar setin kayan dakin manne da madaidaiciyar plasma suna fuskantar gadon ɗakin. Kai tsaye toilet ta nufa don ta yi wanka bayan ta rage kayan jikinta, ba da jimawa ba ta fito ƙirjinta ɗaure da tawul da ya kawo mata tsakiyar cinyoyinta da suka bayyana jajur da su ko ɗan tabo babu, ba tare da 6ata lokaci ba ta hau shirya kanta. Bayan ta gama yin shafe-shafe ta gyara gashinta da yake da tsawo ga santsi, wurin ƙatuwar wardrobe ɗinta dake a jikin bango ta nufa don ta ɗauko kayan da zata saka, saida ta yi ruwan ido wurin zabar kayan da zata saka don kaya ne ciki gasu nan birjik iri- iri, ƙarshe wani baƙin lace mai adon fulawowi peach da ratsin golden ta dauko, kana ganin leshin ba sai ma an faɗi maka zai yi kuɗi ba yadda aikin jikinsa ya saƙu sosai, bayan ta saka kayan wanda fitted gown ce da ta kama jikinta daga ƙasa ta buɗe haka hannun rigar ma dogo ne daga ƙasan shi ya ɗan bude an yi ado da bakin leshin, wuyan rigar irin mai zagayayyar kwala ne, ta matuƙar yin kyau kayan sun amshi jikinta ta fito a ƴar matashiyar budurwa, duk da bata ida zama babbar budurwa ba alamun tana da diri mai kyau ya bayyana, dama jikin momynta ta biyo duk da a fuskarta akwai ɗan yanayin daddynsu amman ta fi kama da momynsu sosai, tana da tsawo sannan bata da jiki amman kuma ba siririya bace, daga yanayin jikinta akwai alamun da ta ƙara girma ko ta yi aure zata iya ƙara jiki, gaban madubi ta tsaya tana kallon kanta fuskarta ɗauke da murmushi ganin yadda rigar ta amshi jikinta, dama kayan sababbi ne bata ta6a saka su ba suna cikin kayan da aka yi masu saboda zuwan yayan su Deen, ko ƙananun kayan da suka je tarbar sa da su suma sababbi ne gal yau suka fara saka su, ɗan jujjuyawa ta yi ta kai hannu tana shafa hips ɗinta, ta ji daɗin ganin yadda suka fito, kai idonta ta yi kan ƙirjinta da suma sun fito ɗas duk da har da ƙarin bra da ta saka yasa suka cika, kallabin kayan ta shiga ɗaurawa bayan ta ɗaure gashinta da ribbom jelar ta sauka har wuce saitin kafaɗarta, tana cikin yin ɗaurin ta ji an buɗe ƙofar ɗakin, ta cikin madubin ta kai idonta wurin ƙofar, har sai da gabanta ya ɗan faɗi ganin mom ɗin su ce ta shigo,
Idonta akan Leemah dake ci gaba da yin ɗaurin kallabinta ta nufo cikin ɗakin, gefenta ta tsaya tana bin ta da kallo mai cike da mamaki, sai da ta kammala yin ɗaurin sannan ta juyo ta kalli mom ɗin na su da murmushin ƙarfin hali kan fuskarta ta furta, "Mom na yi kyau ko?" Bata amsa mata ba da alamun mamaki ta ce, "To wannan ɗin na minene?" Ta yi maganar tana nuna ta daga ƙasa har sama, ɗan tura bakinta da ya sha dark peach din jambaki ta yi da yanayin shagwa6a ta ce kwalliya ce kawai ta yi, wata uwar harara ta wurga mata da alamun 6acin rai ta ce, "Ke nan wanccan mutumin ki kai ma kwalliyan?" Bata rai Leemah ta yi, "Mom ni fa kawai na yi kwalliyana ne, kuma ai ba yau na fara yi ba ko."
Bin ta da kallo mom ta yi sheƙeƙe, fuska a yamutse ta ce, "Eh ba yau kika saba yin kwalliya ba, amman ba irin wadda kika saba yi ɗin ba ce ai kika yi. Wato dai zargin da nike yi a kan ki Leemah ya zama gaskiya ko! Idan ba akwai wani abu tsakanin ki da wanccan yaron ba uban miye to na yin kwalliya haka? Ko yayanki da ya ɗau tsawon lokaci bai zo ba sai yau baki yi irin wannan kwalliyar ba don tarbar sa, soyayya kike da Fahad ko!" Ta tambaya cikin kwatsa tsawa, tura baki Leemah ta yi rai 6ace ta ce, "Wai mom sau nawa zan ce maki ni ba soyayya muke yi da shi ba, kuma in ma soyayyar muke yi ai ba haramun bane tun da akwai aure a tsakanin mu..." Uwar tsawa ta daka mata ta ce, "Kar ma ki fara wannan tunanin wllh! In ma soyayya kuke yi to tun wuri ki datse ta idan ba haka ba zan datse ta da kai na, matuƙar ina numfashi ba zan bari hakan ya faru ba wllh, ai zaren bai yi daidai da kalar yadin ba, bai kai matsayin da zai iya auren ki ba!" Ta ƙarasa tana ɗan jujjuya kanta ta ƙanƙance idanunta, cikin ƙuna-ƙuni Leemah ta ce, "In haka ne, to ai kema mom ke da daddy zaren bai yi daidai da kalan yadin ba ko kuma ya aure ki, kuma ai ya Fahad bai da wani aibu yana da kyau kuma yana da aiki mai kyau sannan danginsu masu arziƙi ne, ke kuma ai dangin ku ba masu kuɗi bane amman a hakan suka amince dad ya aure ki, sai ke kuma zaki ce ba za ki amince ma wani nasu ya auri ɗiyar ki ba." Tana maganar tana ɗan ja da baya, da alama ta kashe bakin mom ɗin nasu, tsananin al'ajabin abun da Leemah ta faɗa ne bayyane akan fuskarta,
Cikin murya mai kaushi ta furta, "Leemah ni kike faÉ—i ma wannan maganar!" Ta faÉ—a tare da nuna kanta da yatsa,
"To ai gaskiya na faɗa ko mom, ba ta inda na fi ƙarfin ya Fahad, in ma don kina ganin daddynmu mai kuɗi ne shima ai daddynsa yana da kuɗi, ko da don kina tunanin dad ya fi abbansu kuɗi ne kin manta da cewa dad ɗin namu ƙanin mahaifinsu ne?" Wani kallon takaici mom take bin ta da shi ta yamutsa baki, Leemah na kikkafta idanu ta ƙara cewa, "In dai ina son shi shima yana sona sai mun auri jun...." Da sauri ta goce ma marin da mom ta kawo mata, tana huci ta furta, "To don ubanki, ko shi ɗanɗan ƙaruna ne baza ki aure shi ba don ba ɗan shaye-shaye na haifa ma ke ba! Sannan ko wadda take iko da ubanki bata isa ta sa ya aure ki ba balle shi uban naki! Gara ki dawo cikin hayyacin ki tun wuri." Tana ƙarasa maganar ta juya ta nufi barin ɗakin, ta san Leemah ba kunya ta ishe ta ba, in ta biye mata haka zatai ta saka ta hargowa tana ƙara ƙunsa mata bacin rai,
"In har Allah Ya ƙaddara shi mijina ne sai na aure shi, ba wanda zai iya hana hakan." Ta faɗa cikin tura baki, lokacin mom ta kama ƙofa zata fita ta tsinkayi muryar Leemah, juyowa tayi cikin sakin shu'umin murmushi ta furta, "We shall seee..." Daga haka ta fuce tare da rufe ƙofar da ƙarfi ta bada sauti.