Sashe 52
A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Amman dai yakamata ki bar ma ƙannanki suna tuyar awaran nan, ko ba samari ba baki jin kunyar ƙawayen ki su gan ki kina tuyar awara?" Hajiya ta tambaya da zolaya, Salma ta yi ƴar dariya ta ce, "Ai ma duk ƙawayena sun san ina yin awaran, kuma ni bana jin komai tun da neman halak ne, ya fi ka je kana roƙon mutane." Da alamun burgewa a maganarta hajiya ta ce, "Wannan gaskiya ne Salma. Allah Ya ƙara rufa asiri." Ta amsa da Amin, duk abun nan Deen na saurarar su duk da ba za ka ce hankalinsa na a kan su ba don idanunsa na akan Tv, maganar Salma ta ƙarshe ba ƙaramin burge shi ta yi ba saidai ba alamar da ta nuna hakan. Bayan hajiya ta ƙwala ma Balaraba kira ta fito ta bata umarnin ta kawo ma Salma robar awaran ta ce ta zubo mata kayan itatuwan da aka kawo ɗazun daga lambu, after some minutes Balaraba ta kawo mata robar da lemu, mangaro, gwaba a ciki, hajiya ta ce ma Salma gashi nan su je su sha ta yi mata godiya, har za ta juya ta ji Balaraba ta ce, "Wai Salma ina fara ne, kwana biyu ko kin daina soyawa?" Tana murmushi ta ce, "Wllh anty Balaraba faran ne ta yi tsada sosai, idan na soya sai a yi ta cewa na yi tsada shi ya sa ma kawai na bari." Balaraba na murmushi ta ce, "Ai komai ma yanzu ya yi tsada abun sai dai addu'a kawai, amman idan kina fita ko ya ya ne kuma ana siya ai ya fi ki ci gaba da ki ce kin bari ɗin gaba ɗaya, tun da gaskiya kin iya soya fara ba ƙarya." Dariyar jin daɗin yabon ta yi, ta ce in sha Allah za ta ci gaba dama wasu na ta so, itama Balarabar ta ce to idan ta yi tana so ta kawo mata ta dubu ɗaya, hajiya dake sauraran su tana ta murmushi, juyawa Balaraba ta yi ta koma kicin Salma ta ƙara yi ma hajiya Sallama da godiya ta nufi hanyar barin falon, har ta kusa kai wa ƙofa ta juyo da niyyar satar kallon Deen kawai sai gani ta yi ashe idon shi na kan ta, da sauri ta juya ta tafi.
Bayan sallar magrib Deen ya fara ganin mutanen dake son ganawa da shi, yawanci duk koke ne kan halin matsin rayuwa wasu kuma abun da ya shafi ƙwallon ƙafa, a wurin parking space ya zauna ana shigo mashi da mutane a nutse da yake bakin gate ɗin akwai jami'ai, sai da aka fara kiran sallar issha ya dakata tare da ba waɗanda bai samu gani ba haƙuri ya basu lokacin da zai gan su, cikin gida ya koma wurin Fahad wanda ya dawo da magrib, tare suka tafi masallaci yin sallan issha, bayan sun dawo suna shigowa haraban gidan aka kira Deen a waya ya ce ma Fahad ya shiga ciki zai shigo idan ya gama amsa kiran, a wurin da ya zauna ɗazun da yana ganin mutane ya zauna, ya ɗan ɗauki lokaci yana yin wayar wanda wani babban abokinsa ne ɗan team ɗin su bature ya kira shi suke tattaunawa game da hutun da suke yi da kuma shirin da za su yi don tunkarar next season, bayan ya gama yin wayar zaune ya yi a wurin idanunsa na kallon wuri ɗaya kamar mai tunanin wani abu, motsin da ya ji a ta gefensa ya sa shi kai idanunsa wurin, Balaraba ce ta fito tana ruƙe da wata babbar roba ta nufi hanyar bayan gidan, juyo da kansa ya yi ya shiga latsa wayarsa, ba a ɗauki lokaci ba ya sake jin motsi ya ɗago kai, ita ce ta dawo zata koma ciki, har ta kusa kai wa ƙofa ya dakatar da ita ta hanyar yin alamar kiran ta, da sauri ta aje robar a wurin ta nufo shi, kafin ta ƙaraso wurin sa a cikin ransa ya shiga tunanin to mi ma zai ce mata da ya kira ta? Daga gefensa ta tsaya cikin ladabi ta gaishe da shi ya ɗan jinjina mata kai, shiru ya ɗan yi na wani lokaci sai kuma ya gyara zaman sa ya ce mata dama yana son tambayarta ne a kan yarinyar nan da suke yin awara a nan unguwan suke? Da sauri ta amsa mashi da eh, ta ce ai basu da ma nisa da an fita, layin da ke tsallake yana kallo bangaren nan gidan anan ciki suke gidansu ne na ukku daga dama, kai ya jinjina mata ya ce ya gode za ta iya tafiya, sam Balaraba bata kawo komai ba a ranta illa ta yanke taimakon su wataƙil zai yi ganin yadda yake ta taimaka ma mutane, bayan ɗan lokaci ya miƙe yana tafiya a nutse jikinsa sanye da ƙananun kaya ya nufi gate, ganinsa ya fito officers dake bakin gate ɗin suka shiga faɗin, "Barka da fitowa yalla6ai..." Bayan ya amsa masu, ganin yana kallon bangaren da aka faɗi mashi gidansu Salma yake wani cikin jami'an ya ƙara cewa, "Ko da wani abu ne yallabai?" Ya bashi amsa da a'a, tunanin ko ya kamata ya yi abun da zuciyarsa ke horan sa akan ya yi ya shiga yi, hannu ya kai cikin aljihun wandonsa ya fiddo takunkumin fuska, tafiya ya fara yi bayan ya gama sakawa, wani jami'i ya ce mashi ko yana buƙatar rakiya ya ɗan ɗaga masa hannu tare da faɗin ba nisa zai yi ba, suna ta mamakin in da zai je ganin yana ƙoƙarin tsallaka titi, yana shiga layin idanunsa suka hango masa wani wuri inda wuta ke ci ga wasu yara a tsugunne, daga yadda aka kwatanta masa ya fahimci nan ne inda take tuyan awaran, a nutse ya tunkari wurin fuskarsa a ƙasa, daga ɗan nesa da su ya dakata yana kallon wurin.
"Awara za a baka?" Ya ji ɗaya daga cikin yaran ya tambaya cikin ɗan ɗaga murya, hannu ya kai a hankali ya zame nosemask ɗin ganin wurin ba wadataccen haske, tambayarsu ya yi ina mai yin abun, yaron ya ce, "Yaya Salma ce ta shiga gida ta dawo, amman ko mu zamu iya saida maka." Shiru Deen ya yi daga yanayin zaƙin muryar yaron ya fahimci ɗan'uwanta ne, hannu Deen ya kai ya mayar da nose mask ɗin ganin wasu matasan samari sun nufo wurin, awaran suka siya bayan an sallame su yaron ya kalli Deen ya ce "Ka ji, ta nawa za a baka awaran?" Ɗan murmushi ya bayyana a kan fuskarsa ya ce masa bari ita mai abun ta dawo, miƙewa yaron ya yi da sauri yana faɗin to bari ya je ya kirawo ta, da ƴar sassarfa ya nufi gidan Deen ya ɗaga ido yana kallon inda yaron ya nufa, a daidai bakin zaure suka haɗe da ita har suna yin karo, ta ce, "Lafiya Hamza ka taho haka?" Da sauri ya ce, "Wani mutumi ne ya zo siyan awara na ce ta nawa za a bashi amman ya ce sai kin dawo." Da alamun mamaki ta maimaita abun da ya faɗa, ɗan leƙa kanta ta yi ta hango shi saidai bata iya gane ko wanene ba saboda ba haske ta dai hangi mutum a tsaye, "Ka san shi?" Ta tambayi Hamzan, kai ya girgiza mata ya ce, "A'a ya rufe fuskan shi, amman dai yana ta uban ƙamshi." Juya maganar Hamza ta shiga yi a ranta tana ƙoƙarin tuno wanda ta sani mai zuwa siyan awara yana ƙamshin turare sosai, fitowa suka yi tana biye da bayan Hamza jikinta sanye da hijab mai hannu ta tsaya mata daidai gwiwa, da sallama ta ƙaraso wurin ta tsaya ɗan nesa da shi tana kallonsa sai dai ta kasa tantance wanene don tana ganin kamar bata ta6a ganin wani mai irin suffar jikinsa ya zo siyan awara ba, ga shi ta gaskiyar Hamza sai baza uban ƙamshi mai ratsa zuciya yake duk ya cika mata hanci, "Ina wuni..." Ta gaishe da mutumin duk da bata san wanene ba amman ya yi mata ƙwarjini sosai, ganin bai da niyyar yi mata magana koda ta gaishe shi kai ya ɗaga mata, ta ce, "Awara za a baka ne?" Ta tambaya ta tsare shi da idanu, ta cikin mask ɗin ta ji ya ce za su yi magana tana a nan ne? ta gane yana nufin ta yi masa nisa, sam bata gane muryarsa ba saboda rufe bakinsa da ya yi, ɗan matsowa ta yi kaɗan a ranta tana mamakin wanene wannan mutumin mai aji haka? Jin bai ce komai ba duk da ta matso ya sa ta shiga yin tunanin ko har yanzu ta yi masa nisa ne shiyasa ya ƙi cewa komai, ƴan kame-kame ta shiga yi ta ce, "Uh..mm jikina yana yin ƙaurin wuta ne ban so in matso ka ji..." Ita kanta bata san dalilin faɗin hakan da ta yi ba, wataƙil saboda yadda ta ji yana sakin ƙamshi ya sa ta kama kanta, steps biyu zuwa ukku ya yi shi ya matsa ta kafe shi da idanu, a hankali ya kai hannu ya zame nose mask ɗin fuskarsa, duk da bata ganin fuskar sosai sai da gabanta ya faɗi, kallon ƙurulla ta shiga yi masa tana son gane waye,
Bayan sallar magrib Deen ya fara ganin mutanen dake son ganawa da shi, yawanci duk koke ne kan halin matsin rayuwa wasu kuma abun da ya shafi ƙwallon ƙafa, a wurin parking space ya zauna ana shigo mashi da mutane a nutse da yake bakin gate ɗin akwai jami'ai, sai da aka fara kiran sallar issha ya dakata tare da ba waɗanda bai samu gani ba haƙuri ya basu lokacin da zai gan su, cikin gida ya koma wurin Fahad wanda ya dawo da magrib, tare suka tafi masallaci yin sallan issha, bayan sun dawo suna shigowa haraban gidan aka kira Deen a waya ya ce ma Fahad ya shiga ciki zai shigo idan ya gama amsa kiran, a wurin da ya zauna ɗazun da yana ganin mutane ya zauna, ya ɗan ɗauki lokaci yana yin wayar wanda wani babban abokinsa ne ɗan team ɗin su bature ya kira shi suke tattaunawa game da hutun da suke yi da kuma shirin da za su yi don tunkarar next season, bayan ya gama yin wayar zaune ya yi a wurin idanunsa na kallon wuri ɗaya kamar mai tunanin wani abu, motsin da ya ji a ta gefensa ya sa shi kai idanunsa wurin, Balaraba ce ta fito tana ruƙe da wata babbar roba ta nufi hanyar bayan gidan, juyo da kansa ya yi ya shiga latsa wayarsa, ba a ɗauki lokaci ba ya sake jin motsi ya ɗago kai, ita ce ta dawo zata koma ciki, har ta kusa kai wa ƙofa ya dakatar da ita ta hanyar yin alamar kiran ta, da sauri ta aje robar a wurin ta nufo shi, kafin ta ƙaraso wurin sa a cikin ransa ya shiga tunanin to mi ma zai ce mata da ya kira ta? Daga gefensa ta tsaya cikin ladabi ta gaishe da shi ya ɗan jinjina mata kai, shiru ya ɗan yi na wani lokaci sai kuma ya gyara zaman sa ya ce mata dama yana son tambayarta ne a kan yarinyar nan da suke yin awara a nan unguwan suke? Da sauri ta amsa mashi da eh, ta ce ai basu da ma nisa da an fita, layin da ke tsallake yana kallo bangaren nan gidan anan ciki suke gidansu ne na ukku daga dama, kai ya jinjina mata ya ce ya gode za ta iya tafiya, sam Balaraba bata kawo komai ba a ranta illa ta yanke taimakon su wataƙil zai yi ganin yadda yake ta taimaka ma mutane, bayan ɗan lokaci ya miƙe yana tafiya a nutse jikinsa sanye da ƙananun kaya ya nufi gate, ganinsa ya fito officers dake bakin gate ɗin suka shiga faɗin, "Barka da fitowa yalla6ai..." Bayan ya amsa masu, ganin yana kallon bangaren da aka faɗi mashi gidansu Salma yake wani cikin jami'an ya ƙara cewa, "Ko da wani abu ne yallabai?" Ya bashi amsa da a'a, tunanin ko ya kamata ya yi abun da zuciyarsa ke horan sa akan ya yi ya shiga yi, hannu ya kai cikin aljihun wandonsa ya fiddo takunkumin fuska, tafiya ya fara yi bayan ya gama sakawa, wani jami'i ya ce mashi ko yana buƙatar rakiya ya ɗan ɗaga masa hannu tare da faɗin ba nisa zai yi ba, suna ta mamakin in da zai je ganin yana ƙoƙarin tsallaka titi, yana shiga layin idanunsa suka hango masa wani wuri inda wuta ke ci ga wasu yara a tsugunne, daga yadda aka kwatanta masa ya fahimci nan ne inda take tuyan awaran, a nutse ya tunkari wurin fuskarsa a ƙasa, daga ɗan nesa da su ya dakata yana kallon wurin.
"Awara za a baka?" Ya ji ɗaya daga cikin yaran ya tambaya cikin ɗan ɗaga murya, hannu ya kai a hankali ya zame nosemask ɗin ganin wurin ba wadataccen haske, tambayarsu ya yi ina mai yin abun, yaron ya ce, "Yaya Salma ce ta shiga gida ta dawo, amman ko mu zamu iya saida maka." Shiru Deen ya yi daga yanayin zaƙin muryar yaron ya fahimci ɗan'uwanta ne, hannu Deen ya kai ya mayar da nose mask ɗin ganin wasu matasan samari sun nufo wurin, awaran suka siya bayan an sallame su yaron ya kalli Deen ya ce "Ka ji, ta nawa za a baka awaran?" Ɗan murmushi ya bayyana a kan fuskarsa ya ce masa bari ita mai abun ta dawo, miƙewa yaron ya yi da sauri yana faɗin to bari ya je ya kirawo ta, da ƴar sassarfa ya nufi gidan Deen ya ɗaga ido yana kallon inda yaron ya nufa, a daidai bakin zaure suka haɗe da ita har suna yin karo, ta ce, "Lafiya Hamza ka taho haka?" Da sauri ya ce, "Wani mutumi ne ya zo siyan awara na ce ta nawa za a bashi amman ya ce sai kin dawo." Da alamun mamaki ta maimaita abun da ya faɗa, ɗan leƙa kanta ta yi ta hango shi saidai bata iya gane ko wanene ba saboda ba haske ta dai hangi mutum a tsaye, "Ka san shi?" Ta tambayi Hamzan, kai ya girgiza mata ya ce, "A'a ya rufe fuskan shi, amman dai yana ta uban ƙamshi." Juya maganar Hamza ta shiga yi a ranta tana ƙoƙarin tuno wanda ta sani mai zuwa siyan awara yana ƙamshin turare sosai, fitowa suka yi tana biye da bayan Hamza jikinta sanye da hijab mai hannu ta tsaya mata daidai gwiwa, da sallama ta ƙaraso wurin ta tsaya ɗan nesa da shi tana kallonsa sai dai ta kasa tantance wanene don tana ganin kamar bata ta6a ganin wani mai irin suffar jikinsa ya zo siyan awara ba, ga shi ta gaskiyar Hamza sai baza uban ƙamshi mai ratsa zuciya yake duk ya cika mata hanci, "Ina wuni..." Ta gaishe da mutumin duk da bata san wanene ba amman ya yi mata ƙwarjini sosai, ganin bai da niyyar yi mata magana koda ta gaishe shi kai ya ɗaga mata, ta ce, "Awara za a baka ne?" Ta tambaya ta tsare shi da idanu, ta cikin mask ɗin ta ji ya ce za su yi magana tana a nan ne? ta gane yana nufin ta yi masa nisa, sam bata gane muryarsa ba saboda rufe bakinsa da ya yi, ɗan matsowa ta yi kaɗan a ranta tana mamakin wanene wannan mutumin mai aji haka? Jin bai ce komai ba duk da ta matso ya sa ta shiga yin tunanin ko har yanzu ta yi masa nisa ne shiyasa ya ƙi cewa komai, ƴan kame-kame ta shiga yi ta ce, "Uh..mm jikina yana yin ƙaurin wuta ne ban so in matso ka ji..." Ita kanta bata san dalilin faɗin hakan da ta yi ba, wataƙil saboda yadda ta ji yana sakin ƙamshi ya sa ta kama kanta, steps biyu zuwa ukku ya yi shi ya matsa ta kafe shi da idanu, a hankali ya kai hannu ya zame nose mask ɗin fuskarsa, duk da bata ganin fuskar sosai sai da gabanta ya faɗi, kallon ƙurulla ta shiga yi masa tana son gane waye,