Sashe 29
A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daga cikin wani ɗan lungu ta 6ullo, tana sanye da uniform riga da wando sai ƴar madaidaiciyar hijab wadda daga bayan saman kanta ya yi tudu sosai, tsaf-tsaf da ita duk da daga gani lokacin tashin su aka yi, amman sam ba datti a tare da kayan jikinta, a hannunta na hagu ƙatuwar baƙar jakar makaranta ce sargafe, yayin da ƙafafunta ke sanye da baƙaƙen takalma sneakers, kana ganinta ka ga ƴar makaranta mai natsuwa da tsafta. Tana ƙarasowa bakin hanyar ta tsaya tana dubawa ko akwai abun hawan da ya taho, bata hango wani abu ya taho ba bayan mashin ɗin da ya wuce daga 6angaren hagu, sai kuma motar da ta hango ta taho daga 6angaren dama, ganin kamar motar na ɗan nesa har ta tsallaka ba tare da ta ƙaraso ba ya sa ta hau hanyar da sauri a ƙoƙarinta na ta tsallaka, da alama idanunta sun hango mata ba daidai ba, don tana kaiwa tsakiyar hanyar motar da ta taho da matsakaicin gudu ta cimmata, kiɗimewa ta yi ta ruɗe ta rasa in da zata nufa tsakanin ƙarasa tsallakawa ko kuma komawa jin horn ɗin da aka shiga sakar mata a jere, ƙarar uban burkin da motar ta ci a dab da ita ne ya sa ta ƙara gigicewa ta saki jakarta tare da durƙushewa a wurin, gaba ɗaya ta saka tafukan hannuwanta ta rufe fuskarta gam, duk a tunaninta motar ta tashi da ita jikinta sai faman kerma yake, kamar yadda idanunta ke runtse haka ma Deen ya runtse idanunsa ganin haɗarin da ya kusa afkuwa, gaba ɗaya hannuwansa na riƙe da sitiyari gam, yayin da gaban shi ke ɗan faɗuwa, tun da suka taho lafiya lau yake driving ɗin shi bai haɗu da wata matsala ba sai yanzu. Da yake hanyar ba babban titi bane ba wasu ababen hawa sosai sai jefi-jefi, sai kuma wasu ƴan mutane da ke a ɗan can bakin hanya wasu a bakin shaguna, hakan ya sa ba idanun mutane sosai a kan su, sai waɗanda suka hango suka saki salati ganin abun da ya faru, horn mai ƙara da aka yi mata ya sa ta saurin ɗagowa, tana ganin gaban motar dab da ita bata ta6a ta ba ta yi saurin miƙewa, ko ta kan jakarta bata bi ba ta ƙarasa tsallakawa ta tsaya har lokacin jikinta bai bar kerma ba, cike da 6acin rai Fahad ya buɗe ƙofar motar ya fito idanun shi a kanta,
"Ke baki da hankali ne? Baki ganin abu ya taho zaki hawo saman hanya!" Cikin yar tsawa ya yi mata maganar, kikkafta idanu ta shiga yi ta fara motsa baki sam ta kasa magana sai nishi take, "Baki ji ana maki magana!" Ya kwatsa mata tsawa ganin ta kafe shi da ido,
"K...ka yi haƙuri, na yi zaton har zan tsallaka bata ƙaraso ba ne..." Katse ta ya yi a hasale ya ce, "Da yake baki da hankali, ko ke dabba ce? shiyasa kika kasa gane ko motan zai ƙaraso wurin ki?" Duk da halin da take ciki sai da ta ji maganar a cikin ranta, yanayin fuskanta ne ya sauya ta ɗan daure fuska,
"C'mon go take your stupid bag ko mu take ta mu wuce, idiot." Wannan karon É—an buÉ—e baki ta yi alamar al'ajabi, zata iya cewa tun da take ba wanda ya taba kiranta da waÉ—annan sunayen sai yau, motsa baki ta shiga yi tana É—an gunaguni tana yi mashi wani kallo mai kaman harara ba tare da ta motsa daga inda take ba,
"Zagi na kike yi??" A fusace ya tambaya, da yake rainon Sagir ce ya koya mata rashin tsoro da kuma kada a yi mata abu ta kyale, rai bace ta ce, "Ni ba zagin ka nike ba, kawai ya zaka ce mani mara hankali dabba kuma idiot bacin tun farko na baka haƙuri..." Mamaki ne shimfide akan fuskar shi jin yadda ta maida mashi magana tana yarinya ƙarama,
"To an ce maki dabban ma, da akwai abun da zaki iya yi ne? Ai gara ma dabba dake don ita ba yadda za ai ta bari har mu ƙaraso mu same ta a saman hanyan." Rai 6ace ya yi maganar dama abun ka da mai zuciya, ƙwarjini ya yi mata ta kasa ce mashi komai sai ɗan ƙunƙuni da take yi, tafiya ta fara a hankali don ta je ta ɗauko jakarta, tsoki ya ja ya ce, "Ƙaramar mara kunya kawai..." Cak ta dakata da yin tafiya ta kalle shi a ɗan harzuƙe murya na rawa kaman zata yi kuka, "Ni dai ba mara kunya bace, kuma ni ba dabba ba ce wllh, koda na yi shiru ai ba don ina jin tsoron ka bane, kawai dai na san idan mutum ya kira ka da sunan abu kuma kai ba abun bane to..." Sam ta kasa ƙarasa maganar don sosai ya yi mata ƙwarjini, ko maganganun da take yi kawai ƙarfin hali ne, kashe shi da mamaki ta yi yanzu, daga yadda yanayin fuskarsa ya canza zaka fahimci hakan, ɗan ƙanƙance ido ya yi tare da ɗan yamutsa baki irin yaro bai san wuta ba sai ya taka,
"Ni ne dabban ke nan?" Ya faɗa ya ɗan ɗage gira, juyar da kai ta yi tana ɗan motsa baki, ƙarasa fitowa ya yi daga jikin marfin motan yana faɗin bari ya zo sai ya ji da kyau abun da take faɗa, Deen na jin haka ya fara kiran sunan shi yana faɗin ya ƙyale ta pls amman bai bi ta kan shi ba, ya san abu mara daɗi na iya faruwa hakan ya saka shi saurin kai hannu ya buɗe motar, Fahad na zuwa kusa da ita ya ɗaga hannu zai zabga mata mari, bata yi ko gezau ba duk da ta fahimci abun da yake ƙoƙarin aikata mata, saidai ta ɗan tsorata da hakan da sauri ta runtse idanunta,
"Pls ya Fahad let her be..." Deen da ya tare hannun nashi ya faɗi, sam baya son attention ɗin mutane ya dawo kan su saboda ya lura da wasu mutanen idanunsu na akan su duk da ba lalle in sun fahimci abun da ke faruwa ba, daddaɗan sautin muryar da ta ji ya ziyarci cikin kunnanta ne ya sa ta yi saurin buɗe idanunta don ta ga waye ya yi maganar, ita bata ma san su biyu bane a cikin motar ba saboda tinted ce ba a ganin wanda ke a ciki, kuma saboda ruɗewar da ta yi tun farko da motan ta kusa buge ta ya sa bata ma iya ta tantance Fahad ko daga bangaren direba ya fito ba, bin su da ido ta yi lokacin Deen ya kama hannun Fahad sun juya, saida ya kai shi har bakin mota ya roƙe shi ya yi haƙuri kada su zamo center of attention, bayan ya Fahad din ya shiga Deen ya juyo don ya koma side ɗin shi, lokacin da suka haɗa ido da ita har saida gabanta ya yi wani irin bugu da ƙarfi ganin irin tsantsar kyawun halittar shi, kallo ɗaya ya yi mata ya ɗauke idanun shi ya wuce, tamkar rainon sakarai haka ta ɗan saki baki ta bishi da ido, ba komai ya fi jan hankalinta tattare da shi ba face sumar shi da ya faka, kokonto ta shiga yi a cikin ranta na shine ya yi maganar da ta ji ko kuwa, sai take ganin wannan ai kaman baya jin hausa ma, sai da ya kai bakin ƙofar motar ya dakata tare da kallo ta,
"Ki je ki ɗauki school bag ein ki ko mu bi ta kan shi mu wuce!" Cike da bada umarni ya yi maganar fuskarsa a ɗan ɗaure, mamaki ne ya cika ta jin da gaske shi yake yin magana da hausa, wucewa ta yi ta ɗauko jakar ta juyo suka haɗa ido ya shige cikin motar, tsaye ta yi a bakin hanyar tana bin motar da kallo har suka wuce, ita kam a rayuwar ta zata iya cewa tun da take bata ta6a ganin mutum mai kyau ba a zahiri kamar shi, sai dai ko a fina-finan ƴan ƙasar waje amman duk da haka gani take wannan kyawun na shi ma na musamman ne, tunanin ko su ɗin su waye ta shiga yi sai kuma take jin kamar ma ta ta6a ganin fuskokinsu ba kamar wanda ya kusa marin ta, wata zuciyar ce ta raya mata a ina zata ta6a ganinsu daga ganin su ba ƴan Nigeria bane ba kamar mai gashi a ƙulle, to amman suke yin magana da hausa? Ta jefa ma kanta tambayar, wataƙil suna zaune anan ne shiyasa suka iya ko kuma shi wanda ya kusa marin nata ne ɗan nan ƙasar, mai gashin a ƙulle ɗan ƙasar waje ne to sai ɗayan ya koya mashi hausar, haka ta dingi yin tunane-tunane a cikin zuciyarta tana tafiya sukuku da ita, a karon farko take jin kaman bata kyauta ba abun da ta yi masu, to amman koma miye wanccan ya ja duk da ta bashi haƙuri ya ce mata dabba, fuska a tur6une take tafiya tana raya hakan a cikin ranta. Lokacin da ta zo daidai bakin wani shago da wani ɗan magidancin mutum ke a tsaye yana kallon duk abun da ya faru ya ce mata,
"Salma lafiya, mi ya faru ne tsakanin ki da waÉ—annan mutanen da suka wuce?" Fuska a yamutse ta kalle shi ta bashi amsa da ba komai sun kusa buge ta ne, daga haka ta wuce yayin da zuciyarta ke ta tariyo mata da fuskokinsu.
Tun da suka ci gaba da tafiya Fahad ke ta ɗan jan tsoki tare da yin ƙwafa, ya so Deen bai hana shi ba da ya wawwanka mata marikan da gobe bazata sake yi ma wani rashin kunya ba, haƙuri Deen dake driving ke bashi yana ce mashi ya manta kawai irin yaran haka suke basu da ɗa'a,
"Mtsww, ban san mi yasa su dad zasu bar hajja tana rayuwa a irin wannan local unguwan ba, ba komai a cikinta sai tarin illiterate mutane." Ya faɗa yana ƙara daure fuska,
"Ke baki da hankali ne? Baki ganin abu ya taho zaki hawo saman hanya!" Cikin yar tsawa ya yi mata maganar, kikkafta idanu ta shiga yi ta fara motsa baki sam ta kasa magana sai nishi take, "Baki ji ana maki magana!" Ya kwatsa mata tsawa ganin ta kafe shi da ido,
"K...ka yi haƙuri, na yi zaton har zan tsallaka bata ƙaraso ba ne..." Katse ta ya yi a hasale ya ce, "Da yake baki da hankali, ko ke dabba ce? shiyasa kika kasa gane ko motan zai ƙaraso wurin ki?" Duk da halin da take ciki sai da ta ji maganar a cikin ranta, yanayin fuskanta ne ya sauya ta ɗan daure fuska,
"C'mon go take your stupid bag ko mu take ta mu wuce, idiot." Wannan karon É—an buÉ—e baki ta yi alamar al'ajabi, zata iya cewa tun da take ba wanda ya taba kiranta da waÉ—annan sunayen sai yau, motsa baki ta shiga yi tana É—an gunaguni tana yi mashi wani kallo mai kaman harara ba tare da ta motsa daga inda take ba,
"Zagi na kike yi??" A fusace ya tambaya, da yake rainon Sagir ce ya koya mata rashin tsoro da kuma kada a yi mata abu ta kyale, rai bace ta ce, "Ni ba zagin ka nike ba, kawai ya zaka ce mani mara hankali dabba kuma idiot bacin tun farko na baka haƙuri..." Mamaki ne shimfide akan fuskar shi jin yadda ta maida mashi magana tana yarinya ƙarama,
"To an ce maki dabban ma, da akwai abun da zaki iya yi ne? Ai gara ma dabba dake don ita ba yadda za ai ta bari har mu ƙaraso mu same ta a saman hanyan." Rai 6ace ya yi maganar dama abun ka da mai zuciya, ƙwarjini ya yi mata ta kasa ce mashi komai sai ɗan ƙunƙuni da take yi, tafiya ta fara a hankali don ta je ta ɗauko jakarta, tsoki ya ja ya ce, "Ƙaramar mara kunya kawai..." Cak ta dakata da yin tafiya ta kalle shi a ɗan harzuƙe murya na rawa kaman zata yi kuka, "Ni dai ba mara kunya bace, kuma ni ba dabba ba ce wllh, koda na yi shiru ai ba don ina jin tsoron ka bane, kawai dai na san idan mutum ya kira ka da sunan abu kuma kai ba abun bane to..." Sam ta kasa ƙarasa maganar don sosai ya yi mata ƙwarjini, ko maganganun da take yi kawai ƙarfin hali ne, kashe shi da mamaki ta yi yanzu, daga yadda yanayin fuskarsa ya canza zaka fahimci hakan, ɗan ƙanƙance ido ya yi tare da ɗan yamutsa baki irin yaro bai san wuta ba sai ya taka,
"Ni ne dabban ke nan?" Ya faɗa ya ɗan ɗage gira, juyar da kai ta yi tana ɗan motsa baki, ƙarasa fitowa ya yi daga jikin marfin motan yana faɗin bari ya zo sai ya ji da kyau abun da take faɗa, Deen na jin haka ya fara kiran sunan shi yana faɗin ya ƙyale ta pls amman bai bi ta kan shi ba, ya san abu mara daɗi na iya faruwa hakan ya saka shi saurin kai hannu ya buɗe motar, Fahad na zuwa kusa da ita ya ɗaga hannu zai zabga mata mari, bata yi ko gezau ba duk da ta fahimci abun da yake ƙoƙarin aikata mata, saidai ta ɗan tsorata da hakan da sauri ta runtse idanunta,
"Pls ya Fahad let her be..." Deen da ya tare hannun nashi ya faɗi, sam baya son attention ɗin mutane ya dawo kan su saboda ya lura da wasu mutanen idanunsu na akan su duk da ba lalle in sun fahimci abun da ke faruwa ba, daddaɗan sautin muryar da ta ji ya ziyarci cikin kunnanta ne ya sa ta yi saurin buɗe idanunta don ta ga waye ya yi maganar, ita bata ma san su biyu bane a cikin motar ba saboda tinted ce ba a ganin wanda ke a ciki, kuma saboda ruɗewar da ta yi tun farko da motan ta kusa buge ta ya sa bata ma iya ta tantance Fahad ko daga bangaren direba ya fito ba, bin su da ido ta yi lokacin Deen ya kama hannun Fahad sun juya, saida ya kai shi har bakin mota ya roƙe shi ya yi haƙuri kada su zamo center of attention, bayan ya Fahad din ya shiga Deen ya juyo don ya koma side ɗin shi, lokacin da suka haɗa ido da ita har saida gabanta ya yi wani irin bugu da ƙarfi ganin irin tsantsar kyawun halittar shi, kallo ɗaya ya yi mata ya ɗauke idanun shi ya wuce, tamkar rainon sakarai haka ta ɗan saki baki ta bishi da ido, ba komai ya fi jan hankalinta tattare da shi ba face sumar shi da ya faka, kokonto ta shiga yi a cikin ranta na shine ya yi maganar da ta ji ko kuwa, sai take ganin wannan ai kaman baya jin hausa ma, sai da ya kai bakin ƙofar motar ya dakata tare da kallo ta,
"Ki je ki ɗauki school bag ein ki ko mu bi ta kan shi mu wuce!" Cike da bada umarni ya yi maganar fuskarsa a ɗan ɗaure, mamaki ne ya cika ta jin da gaske shi yake yin magana da hausa, wucewa ta yi ta ɗauko jakar ta juyo suka haɗa ido ya shige cikin motar, tsaye ta yi a bakin hanyar tana bin motar da kallo har suka wuce, ita kam a rayuwar ta zata iya cewa tun da take bata ta6a ganin mutum mai kyau ba a zahiri kamar shi, sai dai ko a fina-finan ƴan ƙasar waje amman duk da haka gani take wannan kyawun na shi ma na musamman ne, tunanin ko su ɗin su waye ta shiga yi sai kuma take jin kamar ma ta ta6a ganin fuskokinsu ba kamar wanda ya kusa marin ta, wata zuciyar ce ta raya mata a ina zata ta6a ganinsu daga ganin su ba ƴan Nigeria bane ba kamar mai gashi a ƙulle, to amman suke yin magana da hausa? Ta jefa ma kanta tambayar, wataƙil suna zaune anan ne shiyasa suka iya ko kuma shi wanda ya kusa marin nata ne ɗan nan ƙasar, mai gashin a ƙulle ɗan ƙasar waje ne to sai ɗayan ya koya mashi hausar, haka ta dingi yin tunane-tunane a cikin zuciyarta tana tafiya sukuku da ita, a karon farko take jin kaman bata kyauta ba abun da ta yi masu, to amman koma miye wanccan ya ja duk da ta bashi haƙuri ya ce mata dabba, fuska a tur6une take tafiya tana raya hakan a cikin ranta. Lokacin da ta zo daidai bakin wani shago da wani ɗan magidancin mutum ke a tsaye yana kallon duk abun da ya faru ya ce mata,
"Salma lafiya, mi ya faru ne tsakanin ki da waÉ—annan mutanen da suka wuce?" Fuska a yamutse ta kalle shi ta bashi amsa da ba komai sun kusa buge ta ne, daga haka ta wuce yayin da zuciyarta ke ta tariyo mata da fuskokinsu.
Tun da suka ci gaba da tafiya Fahad ke ta ɗan jan tsoki tare da yin ƙwafa, ya so Deen bai hana shi ba da ya wawwanka mata marikan da gobe bazata sake yi ma wani rashin kunya ba, haƙuri Deen dake driving ke bashi yana ce mashi ya manta kawai irin yaran haka suke basu da ɗa'a,
"Mtsww, ban san mi yasa su dad zasu bar hajja tana rayuwa a irin wannan local unguwan ba, ba komai a cikinta sai tarin illiterate mutane." Ya faɗa yana ƙara daure fuska,