Sashe 50
A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Habu shigo mana ya zaka lafe a nan." Gaba ɗayan su suka kai idanuwansu kan ƙofa jin maganar da innarsu ta yi, lokaci guda Imrana da Hamza suka ɗaure fuska ganin wanda aka kira da suna Habu, "Shigo mana mutumina." Salma ta faɗa tana masa murmushi, nufo ciki ya yi yana tafiya kamar mai jin tsoron shiga, yaro ne da ba zai wuce shekara bakwai ba, jikinsa yana sanye da wani koɗaɗɗan yadi da ba a iya tantance ainihin kalarsa saboda tsufa, daga ɗan nesa da su ya tsaya sai da Salma ta sake cewa ya zo wurin ta sannan ya ƙarasa, nuna mashi gefen ta ta yi ya zauna,
"Har an dawo daga makaranta?" Salma ta tambaye shi, kai ya girgiza mata, a hankali ya ce, "Ba mu je ba."
"Saboda me baku je makaranta ba." Kan shi a ƙasa ya ce mata ai sun daina zuwa saboda kayan makarantarsu duk sun yayyage kuma basu da littattafai shi ne baban su ya ce su zauna gida sai ya samu kuɗi zai siya masu, ɗan girgiza kai Salma ta yi, har cikin ranta tana jin tausayin halin da yaran suke ciki na rashin wadatuwa, ba kamar a baya ba lokacin da mahaifinsu ke aiki yana kula da su bakin gwargwado, tun bayan da ya aje aikinsa na ɗan sanda kuma wurin biyan shi hakkinsa na gama aiki aka samu wasu azzalumai suka zabtare masa kuɗin aka biya shi ba yadda ya kamata ba shike nan silar shigar su wahala, gashi yana da iyali matansa ukku da yara sun kai sha bakwai, yana da wata ƴar gonarsa da yake nomawa sai kuma sauran ƴan buge-bugen da yake yi don bai da wata tsayayyar sana'a, ya yi niyyar idan kudin shi suka fito lokacin ya kama ƙwaƙƙwarar sana'a, har suma matansa ya basu babban jari to sai abu ya zo ba yadda ya zata ba, tun a biyan basussukan da ake bin su kuɗin suka tafi, ya dai samu ya canza tsohon babur ɗinsa ya siya wani da yanzu har sana'ar aca6a yake duk da manyanta da ya yi.
"Salma je ki samu wuri ki zuba mashi abinci ya je ya ci shi da ƙannansa." Innarsu ta faɗa, amsawa Salma ta yi da to tana ƙoƙarin miƙewa, wani kalan tamke fuska Imrana ya yi jin za a kwashe masu abincin dare, Salma da ta kalle shi ganin yadda ya yi kicin-kicin da fuska ta nufi kicin tana mashi dariya. Bayan Salma ta zubo mashi ya amsa zai tafi, cikin tsawa Imrana ya ce, "Ba zaka ce an gode ba!"
"Imrana miye haka ne, kai ka basa abincin da zaka ce sai ya yi godiya!" Salma ta daka mashi tsawa, kallon Habu ɗin ta yi ta ce, "Je ka Habu." A hankali kamar zai yi kuka ya ce mata an gode ya tafi, yana haura tudun barandar zai nufi ƙofa Auwalu ya ɗaga kai ya kira shi, bayan ya je ya saka hannu a aljihu ya fiddo kuɗi dubu biyu ya bashi ya ce ya kai ma innarsu ya ce ta basu kuɗin aski a ciki, shima sai da ya ce mashi an gode sannan ya tafi, kallon Imrana ya yi cikin ɗaure fuska ya ce masa idan ya ƙara ganin ya hantari yaron sai ya zane shi, ya shiga kwatanta mashi kowa ma zai iya shiga irin halin da suke a ciki ba wai don Allah Ya fi son su bane ya sa su ya wadata su, idan Allah Ya buɗa ma mutum har da don ya taimaka ma wanda bashi da shi ne, Salma da innarsu nata jinjina kai cike da jin daɗin abun da Auwalun ya yi, innarsu tana alfahari da irin halin yaran nata na tausayin wanda bashi da shi, duk da irin rashin kirkin Sagir shima wani lokacin yana taimakon su da kuɗi, shima Imrana ta san har da yarinta ke damunsa.
Wuraren ƙarfe biyar na yamma innarsu ta gama aikin awarar da hajiya ta buƙata, ƙwala ma Salma dake a cikin ɗaki kira ta yi ta amsa tare da fitowa,
"Yauwa zo ki kai ma hajiya awaran nan." Turus Salma ta yi jin in da zata je,
"Inna ko ki ba Imrana tun da ga su can suna yin kallo, ni wani assignment ne nike yi." Ta faɗa cikin rashin son zuwa. Innarsu ta ce, "Da shi zan aika, sai na tuna hajiya da kanta ta ce a baki ki kai, ai tun da ba wani nesa bane kawai miƙawa zaki ki dawo, je ki ɗauko mayafin ki." Bayan ta ɗauko mayafi ta ɗauki robar ta wuce, tun da ta tunkaro gate ɗin gidan ƙirjinta ya fara bugawa da ƙarfi, fargabarta kada ta iske su Fahad, ganin mutane a bakin gate ɗin ya ƙara saka mata fargaba don ta san wurin jikan hajiya ɗan kwallon nan suka zo da alama yana nan ke nan, bayan ta wuce gate ɗin ta nufi ciki tana ta saƙe-saƙen ko shima wannan ɗayan yana nan.
A bakin kofar shiga falon ta haÉ—e da hajiyar ta yo ma wasu magidanta su ukku rakiya da alama ziyara suka kawo mata, sai da suka gama yin sallama sannan ta dawo kan Salma da murmushi ta ce, "Salma..."
"Na'am hajiya, ina wuni." Amsa mata ta yi da lafiya lau ta ce su shiga ciki, bayan ta zauna ta nuna ma Salma kujera ta ce ta zauna, "Gashi innarmu ta ce in kawo."
"To, awaran ce an gama." Ƙwala ma Balaraba kira ta yi don ta zo ta ɗauka, bayan ta fito suka gaisa da Salma ta ɗauka ta wuce, "Salma ya makaranta, an dawo tun ɗazu ko?" Hajiya ta tambaya tana kallonta, ta amsa da eh tana wasa da yatsun hannunta, hajiya ta ji daɗin ganin yadda ta saki jiki dama saboda abun da ya faru jiya ya sa ta ce a ba Salmar awaran ta kawo, tayin abinci hajiya ta yi mata Salma ta ce mata ta ƙoshi yanzu nan ta gama ci, shiru suka yi gaba ɗaya idanunsu na akan tv, sallamar da aka yi ta sa duk suka kai idanunsu kan ƙofar shigowa........
*_✨A CIKIN RAYUWA✨_*
ZAINAB BATURE
_Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai._
18
Salma na ganin waɗanda suka shigo ta yi saurin maida idanunta ƙasa, ƙirjinta ya hau bugu da ƙarfi, ta shiga zullumin abun da zai biyo baya ganin Fahad, sam ta kasa ɗaga kai ta sake kallon saitin ƙofar yayin da suke shigowa ciki, ƙamshin turaren su ne ya karaɗe ilahirin cikin falon, cikin washe baki hajiya ke kallon Fahad da Deen da suka nufo inda suke, "Ma sha Allah angwayen hajiyar ambasada, wannan wanka dai ya yi min na yaba gaskiya." Ta faɗa tana bin su da kallo, jin furucin hajiya ya sa Salma ta ɗan ɗago kanta a hankali ta kalle su aikuwa idanunta suka shiga cikin na Fahad, ganin yadda ya ɗaure fuska ya sa ta yi saurin janye idanunta, sam ta kasa dauke idanunta daga kan Deen don ba ƙaramin kyau ya yi mata ba,
"Wannan na san bai wuce aikin Fahad ko?" Hajiya ta faɗa tana ta murmushin jin daɗin ganin yadda jikokin nata suka fito, Deen ya bata amsa da shine ya kawo masa kayan, ta ce, "Amman kuwa sun matuƙar amsar ka. Kana ma saka kaya haka kuwa a can?" Ya bata amsa da ya daɗe, "Aikuwa ka rinƙa sakawa don ba ƙaramin burge mutanen can zaka yi ba." Da ɗan murmushi ya ce mata haka daddy ya faɗa, ƙoƙarin zama ya fara a kan kujera mai mazaunin mutum ɗaya, Fahad kuwa wucewa ya yi ciki Salma ta bi bayansa da kallo, maido idonta ta yi kan Deen suka haɗa ido, shi tun da ya shigo ma bai kalle ta ba sai yanzu ya ganta, a hankali ta sauke kanta ƙasa bayan ɗan lokaci ta sake ɗagowa lokacin idanunsa na akan wayarsa, "Ina wuni..." Ta faɗa da siririyar muryarta, sai da hajiya ta ce masa ana gaishe shi ya ɗago suka sake haɗa ido, a ɗan daburce ta sake gaishe da shi ya ɗaga mata kai ba tare da ya amsa ba, daga haka ya ci gaba da latsa wayarsa ita kuwa ta bi sumar kansa dake fake a ƙasa da kallo, bayan ɗan lokaci ya ɗago kansa yana kallon abun da suke kallo a tashar arewa 24, shi rabon da ya kalli channel ɗin hausa ma har ya manta, hajiya ta kai idonta kan sumar shi da ya juyo kansa ta ce, "Amman dai ba haka ka je sallar juma'an ba da gashi a ƙulle kaman mace." Juyowa ya yi fuskarsa a sake kaman zai yi murmushi ya ce mata haka ya je, "Wannan ai sai ka ɗauke ma mutanen dake salla a kusa da kai hankali tun da ba abu ne da suka saba gani ba namiji da gashi a ƙulle." Murmushi mai ɗan faɗi ya yi ya ce ai ya saka hula yana mota ne ya cire, Fahad ne ya fito suka maida kallon su kan shi, "Ba dai har zaka tafi ba?" Hajiya ta tambaya, ya bata amsa da eh ya samu kiran gaggawa ne daga private hospital ɗin da yake aiki a nan zai je ya duba wasu marasa lafiya, hajiya ta ce, "To amman zaka dawo ko, don kun zo ko abinci baku ci ba." Ya bata amsa da ya gama zai dawo ya ce mata a ƙoshe suke sun ci abinci a gida ta gyaɗa kai, kallon Deen ya yi ya bashi hannu suka yi sallama, Deen ya ce mashi sai ya dawo Allah Ya bada sa'a ya amsa da Ameen kafin ya wuce, hajiya itama ta yi addua'ar Allah Ya taimaka ya basu lafiya, bin bayansa Salma da ko kallon 6angaren da take bai yi ba ta yi da kallo, Deen na kallonta yanayin fuskarsa kamar zai saki murmushi don ya fahimci a tsorace take da Fahad sai ka ce ba ita bace mai tsaurin idon nan.
"Wai kuwa ka ga mutanen dake ta son ganin ka tun ɗazun a bakin gate." Hajiya ta tambaya, ya bata amsa da eh sun yi magana sai zuwa dare zai yi ƙoƙarin ganawa da su.
"Har an dawo daga makaranta?" Salma ta tambaye shi, kai ya girgiza mata, a hankali ya ce, "Ba mu je ba."
"Saboda me baku je makaranta ba." Kan shi a ƙasa ya ce mata ai sun daina zuwa saboda kayan makarantarsu duk sun yayyage kuma basu da littattafai shi ne baban su ya ce su zauna gida sai ya samu kuɗi zai siya masu, ɗan girgiza kai Salma ta yi, har cikin ranta tana jin tausayin halin da yaran suke ciki na rashin wadatuwa, ba kamar a baya ba lokacin da mahaifinsu ke aiki yana kula da su bakin gwargwado, tun bayan da ya aje aikinsa na ɗan sanda kuma wurin biyan shi hakkinsa na gama aiki aka samu wasu azzalumai suka zabtare masa kuɗin aka biya shi ba yadda ya kamata ba shike nan silar shigar su wahala, gashi yana da iyali matansa ukku da yara sun kai sha bakwai, yana da wata ƴar gonarsa da yake nomawa sai kuma sauran ƴan buge-bugen da yake yi don bai da wata tsayayyar sana'a, ya yi niyyar idan kudin shi suka fito lokacin ya kama ƙwaƙƙwarar sana'a, har suma matansa ya basu babban jari to sai abu ya zo ba yadda ya zata ba, tun a biyan basussukan da ake bin su kuɗin suka tafi, ya dai samu ya canza tsohon babur ɗinsa ya siya wani da yanzu har sana'ar aca6a yake duk da manyanta da ya yi.
"Salma je ki samu wuri ki zuba mashi abinci ya je ya ci shi da ƙannansa." Innarsu ta faɗa, amsawa Salma ta yi da to tana ƙoƙarin miƙewa, wani kalan tamke fuska Imrana ya yi jin za a kwashe masu abincin dare, Salma da ta kalle shi ganin yadda ya yi kicin-kicin da fuska ta nufi kicin tana mashi dariya. Bayan Salma ta zubo mashi ya amsa zai tafi, cikin tsawa Imrana ya ce, "Ba zaka ce an gode ba!"
"Imrana miye haka ne, kai ka basa abincin da zaka ce sai ya yi godiya!" Salma ta daka mashi tsawa, kallon Habu ɗin ta yi ta ce, "Je ka Habu." A hankali kamar zai yi kuka ya ce mata an gode ya tafi, yana haura tudun barandar zai nufi ƙofa Auwalu ya ɗaga kai ya kira shi, bayan ya je ya saka hannu a aljihu ya fiddo kuɗi dubu biyu ya bashi ya ce ya kai ma innarsu ya ce ta basu kuɗin aski a ciki, shima sai da ya ce mashi an gode sannan ya tafi, kallon Imrana ya yi cikin ɗaure fuska ya ce masa idan ya ƙara ganin ya hantari yaron sai ya zane shi, ya shiga kwatanta mashi kowa ma zai iya shiga irin halin da suke a ciki ba wai don Allah Ya fi son su bane ya sa su ya wadata su, idan Allah Ya buɗa ma mutum har da don ya taimaka ma wanda bashi da shi ne, Salma da innarsu nata jinjina kai cike da jin daɗin abun da Auwalun ya yi, innarsu tana alfahari da irin halin yaran nata na tausayin wanda bashi da shi, duk da irin rashin kirkin Sagir shima wani lokacin yana taimakon su da kuɗi, shima Imrana ta san har da yarinta ke damunsa.
Wuraren ƙarfe biyar na yamma innarsu ta gama aikin awarar da hajiya ta buƙata, ƙwala ma Salma dake a cikin ɗaki kira ta yi ta amsa tare da fitowa,
"Yauwa zo ki kai ma hajiya awaran nan." Turus Salma ta yi jin in da zata je,
"Inna ko ki ba Imrana tun da ga su can suna yin kallo, ni wani assignment ne nike yi." Ta faɗa cikin rashin son zuwa. Innarsu ta ce, "Da shi zan aika, sai na tuna hajiya da kanta ta ce a baki ki kai, ai tun da ba wani nesa bane kawai miƙawa zaki ki dawo, je ki ɗauko mayafin ki." Bayan ta ɗauko mayafi ta ɗauki robar ta wuce, tun da ta tunkaro gate ɗin gidan ƙirjinta ya fara bugawa da ƙarfi, fargabarta kada ta iske su Fahad, ganin mutane a bakin gate ɗin ya ƙara saka mata fargaba don ta san wurin jikan hajiya ɗan kwallon nan suka zo da alama yana nan ke nan, bayan ta wuce gate ɗin ta nufi ciki tana ta saƙe-saƙen ko shima wannan ɗayan yana nan.
A bakin kofar shiga falon ta haÉ—e da hajiyar ta yo ma wasu magidanta su ukku rakiya da alama ziyara suka kawo mata, sai da suka gama yin sallama sannan ta dawo kan Salma da murmushi ta ce, "Salma..."
"Na'am hajiya, ina wuni." Amsa mata ta yi da lafiya lau ta ce su shiga ciki, bayan ta zauna ta nuna ma Salma kujera ta ce ta zauna, "Gashi innarmu ta ce in kawo."
"To, awaran ce an gama." Ƙwala ma Balaraba kira ta yi don ta zo ta ɗauka, bayan ta fito suka gaisa da Salma ta ɗauka ta wuce, "Salma ya makaranta, an dawo tun ɗazu ko?" Hajiya ta tambaya tana kallonta, ta amsa da eh tana wasa da yatsun hannunta, hajiya ta ji daɗin ganin yadda ta saki jiki dama saboda abun da ya faru jiya ya sa ta ce a ba Salmar awaran ta kawo, tayin abinci hajiya ta yi mata Salma ta ce mata ta ƙoshi yanzu nan ta gama ci, shiru suka yi gaba ɗaya idanunsu na akan tv, sallamar da aka yi ta sa duk suka kai idanunsu kan ƙofar shigowa........
*_✨A CIKIN RAYUWA✨_*
ZAINAB BATURE
_Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai._
18
Salma na ganin waɗanda suka shigo ta yi saurin maida idanunta ƙasa, ƙirjinta ya hau bugu da ƙarfi, ta shiga zullumin abun da zai biyo baya ganin Fahad, sam ta kasa ɗaga kai ta sake kallon saitin ƙofar yayin da suke shigowa ciki, ƙamshin turaren su ne ya karaɗe ilahirin cikin falon, cikin washe baki hajiya ke kallon Fahad da Deen da suka nufo inda suke, "Ma sha Allah angwayen hajiyar ambasada, wannan wanka dai ya yi min na yaba gaskiya." Ta faɗa tana bin su da kallo, jin furucin hajiya ya sa Salma ta ɗan ɗago kanta a hankali ta kalle su aikuwa idanunta suka shiga cikin na Fahad, ganin yadda ya ɗaure fuska ya sa ta yi saurin janye idanunta, sam ta kasa dauke idanunta daga kan Deen don ba ƙaramin kyau ya yi mata ba,
"Wannan na san bai wuce aikin Fahad ko?" Hajiya ta faɗa tana ta murmushin jin daɗin ganin yadda jikokin nata suka fito, Deen ya bata amsa da shine ya kawo masa kayan, ta ce, "Amman kuwa sun matuƙar amsar ka. Kana ma saka kaya haka kuwa a can?" Ya bata amsa da ya daɗe, "Aikuwa ka rinƙa sakawa don ba ƙaramin burge mutanen can zaka yi ba." Da ɗan murmushi ya ce mata haka daddy ya faɗa, ƙoƙarin zama ya fara a kan kujera mai mazaunin mutum ɗaya, Fahad kuwa wucewa ya yi ciki Salma ta bi bayansa da kallo, maido idonta ta yi kan Deen suka haɗa ido, shi tun da ya shigo ma bai kalle ta ba sai yanzu ya ganta, a hankali ta sauke kanta ƙasa bayan ɗan lokaci ta sake ɗagowa lokacin idanunsa na akan wayarsa, "Ina wuni..." Ta faɗa da siririyar muryarta, sai da hajiya ta ce masa ana gaishe shi ya ɗago suka sake haɗa ido, a ɗan daburce ta sake gaishe da shi ya ɗaga mata kai ba tare da ya amsa ba, daga haka ya ci gaba da latsa wayarsa ita kuwa ta bi sumar kansa dake fake a ƙasa da kallo, bayan ɗan lokaci ya ɗago kansa yana kallon abun da suke kallo a tashar arewa 24, shi rabon da ya kalli channel ɗin hausa ma har ya manta, hajiya ta kai idonta kan sumar shi da ya juyo kansa ta ce, "Amman dai ba haka ka je sallar juma'an ba da gashi a ƙulle kaman mace." Juyowa ya yi fuskarsa a sake kaman zai yi murmushi ya ce mata haka ya je, "Wannan ai sai ka ɗauke ma mutanen dake salla a kusa da kai hankali tun da ba abu ne da suka saba gani ba namiji da gashi a ƙulle." Murmushi mai ɗan faɗi ya yi ya ce ai ya saka hula yana mota ne ya cire, Fahad ne ya fito suka maida kallon su kan shi, "Ba dai har zaka tafi ba?" Hajiya ta tambaya, ya bata amsa da eh ya samu kiran gaggawa ne daga private hospital ɗin da yake aiki a nan zai je ya duba wasu marasa lafiya, hajiya ta ce, "To amman zaka dawo ko, don kun zo ko abinci baku ci ba." Ya bata amsa da ya gama zai dawo ya ce mata a ƙoshe suke sun ci abinci a gida ta gyaɗa kai, kallon Deen ya yi ya bashi hannu suka yi sallama, Deen ya ce mashi sai ya dawo Allah Ya bada sa'a ya amsa da Ameen kafin ya wuce, hajiya itama ta yi addua'ar Allah Ya taimaka ya basu lafiya, bin bayansa Salma da ko kallon 6angaren da take bai yi ba ta yi da kallo, Deen na kallonta yanayin fuskarsa kamar zai saki murmushi don ya fahimci a tsorace take da Fahad sai ka ce ba ita bace mai tsaurin idon nan.
"Wai kuwa ka ga mutanen dake ta son ganin ka tun ɗazun a bakin gate." Hajiya ta tambaya, ya bata amsa da eh sun yi magana sai zuwa dare zai yi ƙoƙarin ganawa da su.