← Book details A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 197

Sashe 21

A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Mom, in kin san a in da nike rayuwa kin san da suwa nike tarayya? Kin san inda nike shiga a cikin duniyar nan? Kin san wani kalan mutane nike haɗuwa da su? Kin san irin abubuwan da idanuwana suke gani kunnuwana suke ji mom? Duk wannan basu lalata ni ba sai ya Fahad? Mutumin da zan iya rantsuwa akan ban ta6a gani ya sha wani abu da sunan ƙwaya ko abun maye a gaban idanuna ba, kuma kema na tabbata baza ki ce kin ta6a ganin hakan da idon ki ba. Mom, don Allah ina son in tambaye ki, and I don't want you to hide the truth from me, ya Fahad ya taba maki wani laifi ne da ya sa kika tsane shi, baki son shi a kusa na?" Fuska a yamutse ya yi mata tambayar, harara ta watsa mashi ta ce, "Yaushe mu ka yi da kai cewa na tsane shi? Kawai ni ina baka kariya ne daga duk abun da na hango zai cuce ka, ni ban yarda da shi ba, ba don Allah yake tare da kai ba kuma ban son tarayyar ku don zai iya jan ra'ayinka tun da kafi jin maganarsa akan ta kowa har mu iyayenka...." Ta ƙarasa maganar tana ƴan kame-kamen rashin gaskiya, ɗan murmushi wanda ya fi kama da a kira na takaici ya yi, kafin ya furta, "To na gode da kariyar da kike bani, amman Allah shi zai kare ni daga duk wani cutarwa ina roƙonsa hakan kuma ina da yaƙinin yana amsar addu'ana, don haka ina roƙon ki da ki ƙyale mu mu yi zumuncin da Allah Ya halatta a tsakanin mu..."

Ni na tabbata ba don wani abu ya Fahad yake tare da ni ba, mutumin da tun da nike da shi bai ta6a buɗe baki ya ce na bashi kuɗi ba ko na siya mashi wani abu, ko kuma ya ga wani abu nawa ya ce na bashi. Duk abubuwan nan babu wanda ƴan'uwana basu tambayana har da ma wasu da ba ƴan'uwana ba, ke nan suma sai a ce duk cutata suke saboda ina basu abu? Dama idan Allah Ya buɗa maka don ka yi amfani kai kaɗai ya baka ne? Don ka ba wasu ne shi yasa yake ƙara baka, kuma idan kana badawa baka ta6a rasawa. If there’s nothing else you want to tell me, please allow me to go."

Ya ƙarasa idanunsa na kallon gefe ya ɗaure fuska, bin shi da kallo ta yi ta lura da ran shi ya 6aci sosai, ta san yana da sauƙin kai da kauda ido, ba kowane abu ne ke saurin 6ata mashi rai ba, amman fa yana da zuciya idan ransa ya 6aci yana iya ɗaukar lokaci bai sauko ba, kuma zai iya yanke hukuncin da kowa zai iya shiga cikin damuwa, tunanin zai iya ma ya ce zai koma ne ya zo a ranta hakan yasa ta saki fuskarta, ɗan guntun murmushin da ba har zuci ba ta yi ta ce, "Ka yi hakuri yalla6ai na ta6a ɗan lelenka, wanda ya fi kowa muhimmanci a wurin ka gashi har na 6ata maka rai, watarana na san zaka fahimci abun da nike nuna maka."

"Can I go?" Ya tambaya ba tare da ya kalle ta ba, ɗan yamutsa fuska ta yi ta ce, "Yanzu ke nan ku biyo zaku kwanta a saman gadon? Amman zaka iya takura ai, why not shi ya koma bangaren baƙi tun da akwai komai a can kowa ya fi sakewa..." Kafin ta rufe baki ya furta, "Shi ba baƙo bane, ba wani abu zamu kwanta tare. Gud nyt." Ya bata amsa a taƙaice tare da wucewa ya nufi komawa part ɗinsa yana tafiyarsa mai cike da natsuwa, bin shi da kallo ta yi ta tamke fuska tamau sai ka ce bata ta6a yin dariya ba har ya shige ciki ya maido ƙofa ya rufe, ɗan cije le6enta na ƙasa ta yi na ɗan lokaci kafin ta saki ta yi ƙwafa da ƙarfi ta furta, "Mu zuba ni da kai Deen!" Nufar sauka daga benen ta yi a cikin ranta tana saƙa cewa duk hanyar da zata bi sai ta ga ta raba tsakanin su, ba tun yanzu ba ta sha yin yunƙurin hakan lokutta daban- daban amman ta kasa yin nasarar hakan.

Cikin falonsa ya shigo ya nufi kujera ya zauna, ransa a 6ace ya ɗage kansa sama tare da rufe idanunsa, ya yi hakan ne don ya samu sassaucin 6acin ran da yake ji kafin ya koma cikin ɗakin gudun kada Fahad ya fahimci wani abu. A hankali ya shiga tunano lokuttan baya irin yadda ta rinƙa yi ma Fahad izaya da yana a gidan amman duk da irin abubuwan da ta yi mashi hakan bai sa ko sau ɗaya ya janye masu ba a matsayin su na ƴan'uwansa, tunanin hanyar da zai bi ya ga ya yi maganin abubuwan da take yi ma dangin mahaifinsu ya shiga yi don hakan baya mashi dadi sam, a ganin sa har da laifin dad ɗinsu, shi yakamata a ce yana taka mata burki kan hakan amman baya ɗaukar matakin da ya dace shi yasa abun nata har ya girmama haka.

Bayan ya ɗan ji sassaucin ransa ya mike ya nufi cikin ɗakin, yana shiga Fahad dake zaune a gefen gado ya jingina bayansa da jikin gadon ya ɗago idonsa ya kalle shi, nufar shi Deen ya yi yana ƙoƙarin daidaita yanayin shi gudun kada ya fahimci wani abu, a bakin gadon gefen shi ya zauna yana masa ɗan murmushi ya ce, "I thought zan iske ma ka yi bacci." Ɗan girgiza masa kai kawai Fahad ɗin ya yi ba tare da ya furta mashi komai ba, bin shi da kallo Deen ya yi ganin yadda ya yi shiru ya ɗan lumshe ido, tunanin ko ran shi ne ya 6aci kan abun da mom ta shigo ta faɗa ya shiga yi, a hankali ya kai hannu ya dafa cinyar Fahad ɗin fuska a ɗan marairaice ya ce, "Pls ya Fahad ka yi haƙuri akan abun da mom ke yi maka, na san hakan na 6ata maka rai sosai kawai kana kauda kai ne saboda zumuncin dake a tsakanin mu. Wllh sam bana jin daɗin abubuwan da mom ke yi ba tun yanzu ba, kawai na rasa yadda zan yi maganin abun, kuma ni ina ganin duk laifin dad ne, yakamata a ce yana tsawatar mata sosai..." Shiru ya yi yana kallon gaban sa fuskarsa da alamun baccin rai, sai da Fahad ɗin ya ɗan ɗauki lokaci kaman ba zai ce komai ba can ya ɗan yi yar ajiyar zuciya ya ce mashi ya daina damun kansa ai duk sun riga sun san halinta ne hakan, yadda ya yi maganar slowly ya sa Deen tunanin ko bacci yake ji, kallon shi ya yi ya ce mashi ya kwanta mana, shiru ya yi masa tare da lumshe idanunsa, kai idanunsa ya yi kan sauran lemun da ya sha ya rage, tunaninsa ya ƙoshi ne ya sa ya ajiye akan durowar, hannu Deen ya kai zai ɗauka ya ce bari ya ƙarasa shanyewa, yana kai hannu jikin robar ya ga Fahad ɗin ya yi saurin riƙe mashi hannu alamar hana shi ya ɗauka, da alamun mamaki Deen ya kalle shi sai kuma ya yi tunanin ko bai gama sha bane, fasa ɗaukar lemun ya yi ya ce mashi ya yi tunanin ya gama da shi ne tare da komawa ya zauna, bin Fahad ya yi da kallo ganin ya buɗe lemun ya kai baki, saida ya kwankwaɗe shi duka sannan ya cire robar ya maida marfin tare da mayar da ita saman durowan, a hankali yake ta lumshe idanunsa yana buɗewa, lokaci guda Deen dake kallon shi ya fara zargin kamar akwai abun da ke a cikin lemun shiyasa ma ya hana shi ɗauka kuma ya ƙi sakin jiki ya yi magana da shi sosai sai faman lumshe ido yake. Ya san da gaske ne Fahad na amfani da ƙwayoyi sai dai bai ta6a sha ba a gaban sa, haka idan ya sha bai sakin jiki sosai don kada ya gane, ya lura da irin kallon da Deen ke yi masa hakan ya sa shi ƙarasa hayewa saman gadon ya kwanta tare da ba Deen ɗin baya, jimm Deen ya yi na ɗan lokaci yana kallonsa kafin ya kai hannu ya ɗauko robar ya buɗe, kai bakinta ya yi saitin hancinsa ya ɗan sunsuna, daga ƙamshin da ya ji a ciki ya tabbatar masa da zargin da yake, mayar da robar ya yi ya juya yana kallon bayan Fahad, har cikin ransa tausayi yake bashi saboda shaye-shayen ƙwayoyin da yake yi, wanda a da sam hakan ba halinsa bane daga baya ƙaddarar ta haye mashi, hannu ya kai ya ta6a jikinsa tare da kiran shi a hankali, shiru bai amsa mashi ba ya san yana jin shi tun da bai daɗe da kwanciya ba, hakan yasa shi fara yin magana cikin kwantar da murya,
Chapter 21 · 0% Book details