Sashe 55
A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"....Akwai abubuwa da dama masu amfani da ya kamata a rinƙa yi wanda har da dalilin hakan Allah Ya bada wadatar, duk da na san ana yi sosai." Murmushi ne akan fuskarsa don ya fahimci akan abun da take magana, tambayarsa ta yi yanzu wannan motan zata yi nawa, ya bata amsa da 85m wato miliyan tamanin da biyar, har da ce mata ai ba wata babba bace sosai a cikin jerin avatrs, kai ta jinjina tana ƙara kallon motar ta ce ta ci kuɗinta amman dai a rage yawan son ƙyale ƙyalen duniya a fi maida hankali ga yin zubin da za a ƙwasa a lahira. Gently ya ce, "In sha Allah sweetienah, wannan ma zan ɗan yi amfani da shi ne amman ba nawa bane, Fahad na siya mawa na ga yana son irin motan." Da mamaki hajiya ta kalle sa ta maimaita Fahad ya siya ma wannan motan? kai ya ɗaga mata yana murmushi, wani irin farin ciki ne ya lullu6e ta, tana matuƙar jin daɗin yadda jikokin nata suka haɗa kan su suke kyautata ma junan su, yadda suke taimakon juna ko iyayensu ba su yin hakan, duk da kowanne a cikin iyayen nasu yana hali daidai gwargwado, amman mahaifin Deen ya fi na Fahad arziƙi saidai bai yawan yi masa alkhairi kamar yadda ɗan nasa ke ma ɗan'uwansa Fahad, sai dai ta san hakan na da nasaba da rashin dacen mata da ya yi wadda ta san har da ita ke hana shi yi ma makusantan shi alkhairi yadda ya kamata.
"Ban san ya zan misalta maka irin farin cikin da na ji ba Deeni, ina matuƙar alfahari da yadda kuke ƙaunar junan ku kuke taimakon juna. Allah Ubangiji ya ƙara haɗa kawunan ku ya sa ku ɗore da hakan ko bayan ba ran mu." Hannu ya kai ya rungumo kafaɗarta jikinsa yana murmushi ya amsa mata da, "Amin Ya Rabb. In sha Allah." Tana murmushi ta ce aikuwa ita zata yi ma Fahad wannan babban albishir ɗin, da sauri ya ce mata, "No, I wanna give him a surprise, ka da ki sanar masa cewa nashi ne yanzu." Ƴar harararsa ta yi ta ce, "Ke nan buƙulun goron albishir za ka yi mini." Yana yar dariya ya ce, "Idan wannan ne ni zan baki, ki faɗi duk abun da kike so." tana ƴar dariya ta ce, "To nima irin motan nike so."
"No problem, zan sa akawo maki naki." Sanin da gaske yana iya sakawa a kawo mata ya sa ta yi saurin ce masa, "Ni wasa nike maka, in yi yaya da wannan motan ni da ake tuƙawa, wanda ke a kwai ma sun isa." yana murmushi ya ce, "But yana da kyau ka canza zuwa sabon abu if you have the means, sai ki bada wani da kike da shi." Tana murmushi ta ce ai duk motocin da ake mata amfani da su ba su wani tsufa ba akwai ma wadda ba a daɗe da aka kawo mata ba, ta ce tun da dai ya siya ma angonta hakan ya wadatar an gode ta san kuma zata rinƙa hawa, bayan sun gama ganin motar suka koma cikin gidan.....
*_✨A CIKIN RAYUWA✨_*
_New story from the writer of 'A Sanadin Makwabtaka',_
_ZAINAB BATURE_
_Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai._
Page 20
Wararen ƙarfe ukkun rana Fahad ya dawo gidan hajiya, don bayan gama gasar ɗazun wanda da shi aka yi ta gida ya wuce ya shirya don sun yi da Deen da yamma zai je kai ma manyan garin ziyarar gaisuwa, sosai ya yaba da sabuwan motan Deen da ya iske an kawo, a ɗakin Deen suka zauna suka ɗan ƙara hutawa, ana gama sallar la'asar suka yi shirin tafiya, wani ɗanyen farin voile ne Deen ya saka da ya matuƙar amsar jikinsa, da ƙananun kaya zai saka hajiya ce ta kawo masa kayan ta ce manyan kaya yakamata ya saka, kansa ya faka sumarsa baya ba tare da ya saka hula ba don takura masa take yi duk da hajiya ta nemi ya sa hulan ya ce mata sai sun isa, shima Fahad farar shadda ce a jikinsa ya yi kyau sosai sai sakin ƙamshi suke yi, harabar gidan suka fito da wasu abokan su guda biyu da za su je tare , motoci ukku ne jere da za su yi tafiyar da su, ɗaya Deen da Fahad suka shiga, sai mota ta biyu ta abokan nasu ce, sai ta ƙarshe wasu daga cikin manya ne a harkar ƙwallon garin tare da ƴan jarida da suka zo da su, daga ƙarshe motar jami'ai ce da za su yi escorting na su, a jere motocin suka fita daga cikin gidan suka hau hanya duk idanun mutane a kan su, farko gidan ɗan majalissar jaha suka fara zuwa wanda yake a gari ya zo weekend, daga nan gidan chairman ɗin garin suka je, daga ƙarshe suka wuce fadar sarkin maskan Katsina hakimin Funtua, wanda da mahaifin kakansu ambasada da mahaifiyar hakimin yaya da ƙanwa ne, sannan hakimin shine mahaifin mommynsu Fahad. Duk in da suka je sun samu kyakkyawar tarba tare da nuna jin daɗin ziyarar ta Deen, sun yi hotuna tare da bashi lambobin yabo, shima kuma ya ba wasu kyautar jersey daga bisani suka dawo gida, nan da nan hotunan ziyarar tasa suka karaɗe shafukan sada zumunta, mutane na ta yabon halin kirkin Deen wasu kuma suna roƙon yaushe zai kawo masu ziyara suma.
Bayan sallar isha su Salma na zaune a tsakar gida da yake yau bata yi awara ba, suna cin abinci da ita da innarsu da su Imrana,
_"Duniyar nan sai da kuɗiii.. Allah Ka bamu kuɗɗiii...."_ Muryar Sagir ce ta karaɗe tsakar gida ya shigo yana rera waƙa, "Sallamar ke nan Sagir?" Innarsu ta tambaya, sai da ya zauna a bakin tudunkar baranda ya ce, "Bari innarmu, an gama tashin kaina ne qur'an, Allah dai ya yi mana arziƙi wllh dole tsiya ta ji kunya." Tana murmushi ta amsa da Amin Allah Ya bada arziƙin mai amfani, bayan ya amsa da Amin ya ce, "Wato wata arniyar mota ce Nuree Jnr ya faso da ita ɗazun, motar avatar ce wadda ake ma caji, wato innarmu sai kin ga motar nan...Innalillahi! Wallahi tallahi arziƙi ya yi, duk kuma wanda ya ce bai yi ba munafuki ne, idan ba aikin arziki ba an ce ɗazun nan aka kawo mashi motan, kuma wllh ta yi kusan miliyan ɗari." Da mamaki innarsu ta maimaita miliyan dari! Sagir ya gasgata mata haka ne. "Amman da ka ce caji ake mata kamar wai yadda ake ma waya caji?Sagir ya ce, "Eh mana, caji ake mata, dama ai an yi keke mai caji da mashin yanzu ga mota ma an yo." Imrana ya ce, "Innarmu bana baki labarin mashin mai caji ba wanda aka siya ma wani ɗan bokon mu, wllh nima ina son a siya mani irin mashin ɗin."
Sagir ya ce, "Tabb, lallai yaro waye zai siya maka wannan mashin É—in da ya yi kusan miliyan É—aya, idan ba kuÉ—in shinkafar da ake siya mana muna É—an yi ma talauci barazana kake son a tattare a siya maka ba." Tura masa baki Imrana ya yi, innarsu da ke murmushi ta ce Allah zai buÉ—a a siya masa,
"Ban san ya zan misalta maka irin farin cikin da na ji ba Deeni, ina matuƙar alfahari da yadda kuke ƙaunar junan ku kuke taimakon juna. Allah Ubangiji ya ƙara haɗa kawunan ku ya sa ku ɗore da hakan ko bayan ba ran mu." Hannu ya kai ya rungumo kafaɗarta jikinsa yana murmushi ya amsa mata da, "Amin Ya Rabb. In sha Allah." Tana murmushi ta ce aikuwa ita zata yi ma Fahad wannan babban albishir ɗin, da sauri ya ce mata, "No, I wanna give him a surprise, ka da ki sanar masa cewa nashi ne yanzu." Ƴar harararsa ta yi ta ce, "Ke nan buƙulun goron albishir za ka yi mini." Yana yar dariya ya ce, "Idan wannan ne ni zan baki, ki faɗi duk abun da kike so." tana ƴar dariya ta ce, "To nima irin motan nike so."
"No problem, zan sa akawo maki naki." Sanin da gaske yana iya sakawa a kawo mata ya sa ta yi saurin ce masa, "Ni wasa nike maka, in yi yaya da wannan motan ni da ake tuƙawa, wanda ke a kwai ma sun isa." yana murmushi ya ce, "But yana da kyau ka canza zuwa sabon abu if you have the means, sai ki bada wani da kike da shi." Tana murmushi ta ce ai duk motocin da ake mata amfani da su ba su wani tsufa ba akwai ma wadda ba a daɗe da aka kawo mata ba, ta ce tun da dai ya siya ma angonta hakan ya wadatar an gode ta san kuma zata rinƙa hawa, bayan sun gama ganin motar suka koma cikin gidan.....
*_✨A CIKIN RAYUWA✨_*
_New story from the writer of 'A Sanadin Makwabtaka',_
_ZAINAB BATURE_
_Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai._
Page 20
Wararen ƙarfe ukkun rana Fahad ya dawo gidan hajiya, don bayan gama gasar ɗazun wanda da shi aka yi ta gida ya wuce ya shirya don sun yi da Deen da yamma zai je kai ma manyan garin ziyarar gaisuwa, sosai ya yaba da sabuwan motan Deen da ya iske an kawo, a ɗakin Deen suka zauna suka ɗan ƙara hutawa, ana gama sallar la'asar suka yi shirin tafiya, wani ɗanyen farin voile ne Deen ya saka da ya matuƙar amsar jikinsa, da ƙananun kaya zai saka hajiya ce ta kawo masa kayan ta ce manyan kaya yakamata ya saka, kansa ya faka sumarsa baya ba tare da ya saka hula ba don takura masa take yi duk da hajiya ta nemi ya sa hulan ya ce mata sai sun isa, shima Fahad farar shadda ce a jikinsa ya yi kyau sosai sai sakin ƙamshi suke yi, harabar gidan suka fito da wasu abokan su guda biyu da za su je tare , motoci ukku ne jere da za su yi tafiyar da su, ɗaya Deen da Fahad suka shiga, sai mota ta biyu ta abokan nasu ce, sai ta ƙarshe wasu daga cikin manya ne a harkar ƙwallon garin tare da ƴan jarida da suka zo da su, daga ƙarshe motar jami'ai ce da za su yi escorting na su, a jere motocin suka fita daga cikin gidan suka hau hanya duk idanun mutane a kan su, farko gidan ɗan majalissar jaha suka fara zuwa wanda yake a gari ya zo weekend, daga nan gidan chairman ɗin garin suka je, daga ƙarshe suka wuce fadar sarkin maskan Katsina hakimin Funtua, wanda da mahaifin kakansu ambasada da mahaifiyar hakimin yaya da ƙanwa ne, sannan hakimin shine mahaifin mommynsu Fahad. Duk in da suka je sun samu kyakkyawar tarba tare da nuna jin daɗin ziyarar ta Deen, sun yi hotuna tare da bashi lambobin yabo, shima kuma ya ba wasu kyautar jersey daga bisani suka dawo gida, nan da nan hotunan ziyarar tasa suka karaɗe shafukan sada zumunta, mutane na ta yabon halin kirkin Deen wasu kuma suna roƙon yaushe zai kawo masu ziyara suma.
Bayan sallar isha su Salma na zaune a tsakar gida da yake yau bata yi awara ba, suna cin abinci da ita da innarsu da su Imrana,
_"Duniyar nan sai da kuɗiii.. Allah Ka bamu kuɗɗiii...."_ Muryar Sagir ce ta karaɗe tsakar gida ya shigo yana rera waƙa, "Sallamar ke nan Sagir?" Innarsu ta tambaya, sai da ya zauna a bakin tudunkar baranda ya ce, "Bari innarmu, an gama tashin kaina ne qur'an, Allah dai ya yi mana arziƙi wllh dole tsiya ta ji kunya." Tana murmushi ta amsa da Amin Allah Ya bada arziƙin mai amfani, bayan ya amsa da Amin ya ce, "Wato wata arniyar mota ce Nuree Jnr ya faso da ita ɗazun, motar avatar ce wadda ake ma caji, wato innarmu sai kin ga motar nan...Innalillahi! Wallahi tallahi arziƙi ya yi, duk kuma wanda ya ce bai yi ba munafuki ne, idan ba aikin arziki ba an ce ɗazun nan aka kawo mashi motan, kuma wllh ta yi kusan miliyan ɗari." Da mamaki innarsu ta maimaita miliyan dari! Sagir ya gasgata mata haka ne. "Amman da ka ce caji ake mata kamar wai yadda ake ma waya caji?Sagir ya ce, "Eh mana, caji ake mata, dama ai an yi keke mai caji da mashin yanzu ga mota ma an yo." Imrana ya ce, "Innarmu bana baki labarin mashin mai caji ba wanda aka siya ma wani ɗan bokon mu, wllh nima ina son a siya mani irin mashin ɗin."
Sagir ya ce, "Tabb, lallai yaro waye zai siya maka wannan mashin É—in da ya yi kusan miliyan É—aya, idan ba kuÉ—in shinkafar da ake siya mana muna É—an yi ma talauci barazana kake son a tattare a siya maka ba." Tura masa baki Imrana ya yi, innarsu da ke murmushi ta ce Allah zai buÉ—a a siya masa,