← Book details A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 197

Sashe 63

A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

"Salma ya makaranta, ko da yake weekend ne ba makaranta sai dai islamiyya ko." Maganar hajiya ta sauka a kunnanta, juyawa ta yi ta kalle ta da murmushi ta ce mata eh, ɗan jinjina kai hajiya ta yi ta ce Allah ya bada sa'a, bayan Salma ta amsa hajiya ta sake cewa, "Kin kwance kan ki ne?" Ta tambaya tana kallon kan Salma da ta saka hula bayan ya yi tudu sosai, "Eh, ɗazun na kwance." Kai hajiya ta ɗaga ta ce saura kitso ko, Salma ta ce, "Eh zan je a fara wanke mani sai a yi mani kitson." Jinjina kai hajiya ta yi tare da mayar da idanunta akan tv, bayan wani lokaci ta kalli Deen ta ce, "Saboda kai aka kawo mawa shine kuma ido guba?" Ba tare da ya kalle ta ba ya yi ɗan murmushi tare da kai awaran da ya ɗebo baki, sosai Salma ta ji daɗin yadda ya saki jiki yana cin awaran bai ma yi amfani da fork ba hannu ya saka, jinjina kai hajiya ta yi ta ce ya ci awara lafiya in dai ita ce zata rama ne, sai lokacin ya ɗan ɗago ya kalle ta still da ɗan murmushi a fuskarsa ba tare da ya ce komai ba ya maida idon shi kan awaran yana ci, sosai Salma ta shagala tana ta kallon shi don komai na shi na musamman, hatta yadda yake cin abinci da burgewa, bata ankara ba kawai ta ga ya ɗago sun haɗa idanu, da sauri ta sadda kan ta ƙasa gabanta na ɗan faɗuwa ganin ya kama ta tana kallonsa, still ya yi yana kallonta don ɗagowar da ya yi magana yake niyyar yi mata, rasa ta ya zai yi mata magana ya yi ganin ta sunnar da kai, after few seconds ta sake ɗagowa da niyyar kallonsa suka sake haɗa ido, tana niyyar kauda idonta ta ga ya yi mata alamar kira da kan sa, bin sa ta yi da kallo cikin alamun rashin tabbas ɗin idan gaske ne kiran nata ya yi, sai da ya sake yi mata alamar ta je sannan ta miƙe ta nufe shi walking slowly, tsayawa ta yi a gaban table ɗin ya ƙara ɗibar sauran awaran cikin kulan, bayan ya zuba sauce da coleslow ya ɗago ya kalli Salma ya ce mata ta ɗauki sauran ta kai ma hajiya, bayan ta yi kaman yadda ya ce hajiya na ɗan murmushi ta ce ai ta yi zaton ba zai batan ba, plate ta sa Salma ta ɗauko mata itama ta zuba mata sauran ta fara ci tana yaba daɗin awaran, bayan Deen ya gama cin awaran duba tissue ya yi a nan bai ganta ba ya tambayi hajiya, amsa ta bashi da ga ta can a dinning area ta kalli Salma ta ce ta je ta ɗauko masa, a saman table ɗin ta ɗaura tissue box ɗin bayan ta ɗauko ya yi mata godiya, ɗaukar kayan da ya yi amfani da su ta yi ta kai kitchen, sai da ta wanke su sannan ta dawo cikin falon ta koma ta zauna, after some minutes hajiya ta gama ta kalli Salma ta ce mata ta je ɗakin Balaraba ta kira ta ta zo ta wanke kayan, miƙewa Salma ta yi ta ce bari ta wanke hajiya na ɗan murmushi ta ce ta kawo masu abun daɗi kuma a barta da wanke-wanke, tana murmushi ta ɗauki kayan ta wuce kitchen, bada jimawa ba Salma ta dawo cikin falon bayan ta gama wanke kayan, hajiya ta yi mata sannu ta amsa da murmushi ta koma ta zauna, bayan ɗan lokaci hajiya ta miƙe ta ce zata ɗan shiga ciki, jin haka ya sa Salma miƙewa ta ce zata tafi, hajiya dake kallonta ta ce ba zata jira ta fito ba, tana ɗan murmushi ta ce ma hajiya ta ga dare ya yi ne, "Haka ne kuma, an gode sosai, itama maman taku ki yi mata godiya." Ta amsa da to, har zata juya ta tafi hajiya ta ce ina kayan da aka zubo awaran Salma ta ce suna a kitchen ta ce to ta je ta ɗauko ta tafi da su, wucewa ta yi zuwa kitchen ɗin hajiya kuma ta nufi hanyar shiga ciki, lokacin da ta fito Deen ne kawai a zaune idonsa na kan tv, ledan da aka sako kayan ta je ta ɗauka ta maida su ciki, kallon Deen ta yi daidai lokacin ya maido idonsa kanta, tsaye ta yi tana ƴan kifce kifcen idanu cike da ƙarfin hali ta yi ɗan murmushi a hankali ta ce masa, "Sai da safe..." Kai ya jinjina mata calmy ya ce, "Thank you, I appreciate it." Murmushi ne akan fuskarta ta ce, "Mu ma mun gode Allah Ya saka da alkhairi ya ƙara ɗaukaka." Kai ya sake jinjina mata da ɗan murmushi, juyawa ta yi ta nufi hanyar barin falon hannunta rike da ledan kayan, tana zuwa daidai bakin ƙofa ta ɗan juyo ta saci kallonsa, daidai yana ƙoƙarin miƙewa ganin haka ya sa ta yi saurin ƙarasa ficewa har ta kusa yin tuntu6e....

✨A CIKIN RAYUWA✨

_New story from the writer of 'A Sanadin Makwabtaka',_

ZAINAB BATURE

23
Chapter 63 · 0% Book details