← Book details A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 197

Sashe 15

A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Who could resist this beauty?" Bayan ɗan lokaci ta ji Fahad ɗin ya furta, kunya ce ta kama ta don ta fahimci dalilin da ya sa ya faɗi haka, saboda maganar da ta yi masa lokacin da yake cin abinci na akwai wanda take so amman tana tsoron ya ƙi amincewa in ta sanar da shi, shine yanzu ya yabe ta ta hanyar cewa 'waye zai ƙi wannan kyawun?" Hannunta guda ta sa ta ɗan rufe fuskarta alamar kunya, ga jan lallen da aka yi mata dama na zuwan Deen mai kyau mara yawa ya bayyana ya yi ja shar gwanin burgewa.

"Kin yi kyau sosai. U look like a bride." Cire hannun da ta rufe fuskar ta yi, tana murmushi ta ce, "Thank you ya Fahad. Kai ma ai ka yi kaman ango." ÆŠage gira ya yi ya ce ango da irin shigan shi,

"Eh, kaman groom ya yi shigan dinner." Ɗan faffaɗan murmushi ya yi ya ce, "To ko angon ne? Dama gashi shigan dinner ɗin na yi, amman kuma ba bride en, ko idan muka je sai in samu a can?" Ƴar dariya ta yi ta ce, "Ya fi dai ka tafi da amaryan."

Dariya ya yi dimples dinsa suka lotsa, ya riga da ya gama fahimtar ta, da hannu ya yi mata alamar su je cikin falon, suka jera suna tafiya a nutse sai ka ce ango da amaryan yadda suka dace, duk da Leemarh ba wata babba bace amman shigar da ta yi ta ƙara mata girma. Saman kujera mai mazaunin mutum biyu suka zauna suka ɗan karkata ta yadda suke fuskantar juna, hira suka shiga yi yawanci shine ke mata tambayoyi akan karatun ta da wasu abubuwan.

Lokacin da suka ƙaraso bakin matattakalar Deen ya saki hannun mom ɗin nashi suka fara saukowa, suna kaiwa tsakiyar benen idanun mom suka sauka akan Fahad da Leemah dake ta hirar su cikin nishaɗi suna ta murmushi, wani baƙin ciki ne ya tokare mata maƙoshi ta ɗaure fuska tamkar ta ga wani mugun abu, a cikin ranta ta shiga cin alwashin sai ta raba su koda a ce ba soyayya suke ba sai ta kawo ƙarshen wannan shirin nasu don ba shi take haifa ma yaran ba da kowa zai rinƙa shiri da shi suna son shi sosai, kafin su ƙarasa safkowa ƙasa Batool ta fito daga hanyar bangaren su itama doguwar rigar material ce a jikinta ruwan madara, an yi mata makeup itama an gyara mata gashinta ya sauko har bayanta an ɗaura mata net ya yi kaman hula ta fito a yar matashiyar mace yar shekara sha biyu, tana hango su mom ɗinsu ta ambaci sunanta tare da nufar wurin su, a tare Fahad da Leemah suka juya jin sunan mom da Batool ta kira, miƙewa suka yi ganin sun nufo cikin falon, wata muguwar harara mom ta shiga wurga mata, Leemarh ta yamutsa mata fuska tana ɗan tura baki, wani irin ƙamshi ne ya gauraye wurin kasantuwar kowa da kalar abun kamshin da ya shafa, murmushi Fahad ya shiga sakar ma Deen ganin yadda ya yi kyau sosai, shi kan shi ya burge shi, hannu ya ɗan dunƙule ya miƙa ma Deen shima ya yi ma nashi hakan suka ɗan buga irin gaisuwar gayu, Fahad ya ce, "You are looking sharp! You are the GOAT, on and off the pitch!"

Yar dariya Deen ya yi jin yabon da Fahad ɗin ya yi masa har yana kiransa da suna mai matuƙar girma wanda samun sa ba ƙaramin aiki bane a duniyar ƙwallo, amsa ya bashi da, "Tukunna dai, Ya Fahad." Ya faɗa tare da ɗan jinjina kai yana murmushi.

"Ya Deen, in sha Allah you are going to break all the records, trust us you are going to be the GOAT (Greatest Of All Time)" Leemarh ta faɗa tana murmushi, ita kanta gayun na shi ya tafi da ita, dama ba tun yanzu ba sun san yayan nasu da iya ɗaukar wanka, wanda har da hakan ke ƙara mashi masoya musamman mata ba ƙaramin tafiya yake da imanin su ba, gaba ɗaya duk suka amsa ma maganar da Leemah ta yi suma suka furta in sha Allah har da mom ta furta ƙasa ƙasa, yana murmushin jin daɗi ya yi masu godiya. Suna haka sauran yan gidan su Omar da Sultan duk suka fito suma duk wankan suit suka yi sun yi kyau ma sha Allah, daga ƙarshe Dad ɗin su shima ya fito daga bangarensa ya nufo cikin falon jikinsa sanye da suit ruwan toka, sosai kayan suka amshi jikinsa ya fito a babban mutum mai ƙwarjina da haiba, duk idanunsu na akan shi fuskokinsu ɗauke da murmushi har ya ƙaraso wurin su shima yana masu murmushi,

"Wow! Gaskiya dad ka tashi kaina! Ka gan yadda ka yi kyau sosai?" Leemarh ta faɗa ta ɗan buɗe ido, yana murmushi ya yi mata godiya ya miƙo hannu ya ɗan rungumo ta ta gefe.

"Dad, wllh ka yi kaman su ya Deen." Batool ta faɗa tana dariya tare da noƙe kai, itama ya janyo ta jikinsa yana yar dariya ya ce mata ke nan ya koma ɗan saurayi, ta ɗaga mashi kai tana dariya.

"Ki ce wataƙil ma wata ta yaba da wankan nawa in samo maku aunty a can ke nan." Duk suka saka dariya ban da mom da ta hade fuska, ya saci kallonta bayan ya yi maganar suka haɗa ido ta wurga mashi harara, ɗan murmushi ya yi shima yasan ya faɗa ne kawai.

"Are we good to go?" Dad ya tambaya yana kallon Deen da murmushi ganin yadda ɗan nashi ya yi kyau sosai, kallon agogon hannunsa ya yi kafin ya kalli dad din ya ce mashi zasu iya tafiya kusan lokacin ya yi, gaba ɗaya suka nufi hanyar barin falon suna tafiya cikin natsuwa, kana kallon su ka ga waɗanda hutu da jin daɗi ya zauna musu sosai. Tuni an jera motocin da za su tafi da su a gaban entryhall, bayan sun fito aka shiga bubbuɗe masu, Deen da Fahad wata haɗaɗɗiyar baƙar Mercedes S-Class ce suka shiga sai uban sheƙi take irin na sabunta, motar tashi ce ba a jima da kawo ta ba kafin ya zo, dama akwai wasu motocin da ake amfani da su a gidan waɗanda shine ya siye su, dad da mom ɗinsu suma mota ɗaya suka shiga sai sauran yaran har da Omar suka shiga cikin wata ƙatuwar baƙar jeep, tsaye Leemarh ta yi har saida ta ga mom ɗin su ta shiga cikin mota sannan ta yi saurin nufar motar su Deen ta buɗe kofar baya za ta shiga, Fahad da Deen dake zaune a bayan a tare suka kalle ta, ta ɗan yamutsa fuska ta sigar shagwaba ta ce masu a motar su take son tafiya, ɗan murmushi Deen ya yi ba tare da ya ce komai ba ya fito daga bayan ya yi mata alamar ta shiga da hannu, shi kuma ya koma kujerar gaban motan ya shiga, bayan duk sun gama shiga a tare aka tashi motocin suka nufi hanyar gate abun gwanin sha'awa, dama ga su duka motocin baƙaƙe ne sai sheƙi suke yi, daga bayan su kuma motar jami'ai ce ke take masu baya......

*_✨A CIKIN RAYUWA✨_*

_By Zainab Bature_

_Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai._

Page 6

Zaune suke a tsakar gida bayan sallar isha, da yake yanayin zafi ne ba a cikin barandar suke zaune ba, daga gaban ɗakin dake kallon barandar wanda ɗakin Salma ne a nan suka yi shimfiɗa, dama duk in ana zafi anan suke zama don ya fi iska, gaba ɗayan su suna zaune akan ƙatuwar tabarma suna cin abinci, Salma tare da innarsu suke cin tuwon gaban su sai ɗan autansu dake manne a jikin innar tana bashi a baki, daga gefen su Imrana ne tare da Hamza suma suna ci a wuri guda, gefe daga gaban su yayan su Auwalu ne zaune akan tudun baranda shima tuwon yake ci a cikin plate da cokali, sun natsu suna cin abincin jefi-jefi suke yin magana banda Auwalu da ya tattara hankalinsa akan wayar shi, da alama ya yi sabo da yana cin abinci yana latsa waya.

Suna tsaka da cin abinci suka jiyo ƙarar kwaramniyar kwanuka kaman daga cikin kicin, da dan ɗaga murya innarsu ta tambayi waye a nan.

"Ƙilan awakan gidan su Bello ne suka shigo." Imrana ya faɗa da tuwo a bakin sa.

"Ba wasu awakai, mai hankalin gidan ne, ina ganin lokacin da ya shigo daga cikin zaure ya shige kicin." Salma na faɗin haka suka fahimci Sagir take nufi, fitowa ya yi ya nufo su jikin shi daga shi sai gajeran wando ko vest babu, hannun shi ya ruƙo wata yar madaidaiciyar kular abinci, tsaye ya yi akan su fuska da alamun 6acin rai ya ce, "Wai fisabilillahi baza a yi ma mutane abinci ba sai wannan? Da me mutum zai ji, da zafin da ake kokuwa da wannan da zai danƙara ma cikinsa?" Gaba ɗaya dariya suka saka banda Auwalu da hankalinsa na akan waya, itama innarsu ɗan murmushi ta yi ta ce, "To da yake ma ba wanda aka ma dole ai sai ya ci ko?" Yamutsa fuska ya ci gaba da yi yana mitar kullum ai ta abu ɗaya sai ya kashe mutum.

"Amman yaya Sagir ai ba ko da yaushe ake yin tuwo ba da daddare, ko shekaranjiya ba taliyar hausa yaya Salma ta dafa ba muka ci da daddare..." Imrana ne ya faÉ—a tare da kai lomar tuwo bakinsa.

"To ubanwa ya tambaye ka! Kuma ba an fi yin tuwon ba, sai a jera kusan sati ana yin shi kafin a canza wani abun.
Chapter 15 · 0% Book details