Sashe 40
A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayan shekaru huɗu tenure ɗin su ta ƙare aka sake yin za6e, jam'iyarsu ta sake samun nasarar cin zaben hakan yasa duk suka samu yin tazarce, a lokacin Deen na cikin shekara ta bakwai, sosai suke son junansu shi da Fahad in suka haɗu kamar kar su rabu, a lokacin Fahad na cikin shekara ta goma, a wani zuwa da su Deen suka yi Funtua lokacin suma su Fahad suna a Funtua, gaba ɗaya Fahad ya dawo gidan hajiya anan wurinta suke wuni tare da Deen don tun a lokacin Fahad yake fuskantar tsangwama daga wurin Jameela shiyasa yake zama wurin hajiya, lokacin da su Deen za su koma Abuja haka yaron ya dingi kuka yana cewa a tafi da Fahad shima, da ƙyar aka raba su da yake shi Fahad ya ɗan girma sai dai ya yi ta zubar da ƙwalla. Ganin irin shaƙuwar da suka yi ne ya sa Hajiya ta yi ma Ibrahim magana kan ya ɗauki Fahad hakan zai saka su taso da zumunci mai ƙarfi, koda Jameela ta ji zancen da buɗar bakinta sai cewa ta yi a bari mana idan iyayenshi sun mutu sai a ce su ɗauke shi, amman yanzu ga iyayensa a raye miye na wani cewa ya dawo wurin su in ba son ɗaura masu ɗawainiya ba yaro ai sai iyayen shi, shi dai dad a lokacin nuna mata ya yi ba zai iya musanta ma maganar hajiya ba saboda haka ta yi haƙuri, wannan ne sanadiyar komawar Fahad gidan su Deen har suka ci gaba da yin karatu a makaranta ɗaya.
A 6angaren Sapnah tuni ta kammala karatunta na medicine a india, daga baya kuma Maleek ya koma ƙasar America ya ci gaba da yin aiki da wani babban kamfanin fasaha. Sapna ba ƙaramin gata take samu a wurin Maleek ba, gaba ɗaya ta canza kana ganinta kasan hutu ya zauna mata idan ma aka ce maka a Nigeria aka haifeta anan ta taso har ta girma sai ka ƙaryata, sai dai har lokacin basu samu rabo ba ko batan wata bata ta6a yi ba, tun suna a India aka binciki lafiyar su gaba ɗaya inda aka tabbatar matsalar daga wurin Sapnah take, ba ƙaramar damuwa ta shiga ba amman shi Maleek sam bai nuna damuwar shi ba duk da yana son ya ga ya samu rabo, shine yake rarrashin ta yana nuna mata ko da a ce bazata ta6a haihuwa ba yana son ta a haka kuma za su ci gaba da rayuwa ba tare da wata matsala ba har ƙarshen rayuwar su, 6angaren danginta lokacin da suka ji zancen matsalar rashin haihuwar tata sun shiga damuwa sosai musamman Ammin su da kuma Jameela, Ammin har tambayarta ta rinƙa yi sun tabbatar an yi binciken sosai kuwa? Sapna ta tabbatar mata da ƙwararru ne suka yi binciken, sosai Ammin tasu ta shiga baƙin ciki don ba abun da ke a ranta face yanzu shike nan idan bata haihu ba Maleek na iya ƙara aure matar ta zo ta hayayyafa idan ya mutu su cinye gado, wannan dalilin ne ya saka ta damuwa sosai ta shiga bin bokaye ido rufe kan a yi mata aikin da Sapna zata samu ciki ta haihu, saidai kuma shiru Allah bai sa ta samu cikin ba.
Bayan wasu shekaru, abubuwa da dama sun faru, ciki har da yin ritaya da ambasada ya yi suka dawo gida Nigeria da zama a lokacin shima mahaifin Fahad an maido shi aiki Nigeria. Cikin iko na Allah bayan shekaru goma da auren Sapna da Maleek Allah ya azurta su da samun rabo inda ta haiho ya mace wato Basma. Bayan yin ritaya ɗin ambasada da shekara ɗaya shugaban ƙasa na lokacin ya sake bashi muƙamin ambasadan Nigeria a ƙasar Spain, yana riƙe da muƙamin ne bayan wasu shekaru ya kwanta ciwon da ya zamo ajalin shi ya rasu, ba ƙaramin alhini ahalin shi dama al'ummar garin Funtua suka shiga ba na rashin dattijon arziƙi. Rayuwa ta ci gaba da gudana yayin da arziƙin iyayen su Fahad ya ninninku, mahaifin su Deen ya ci gaba da gudanar da harkokin shi na siyasa inda daga baya ya sake tsayawa takarar kujerar ɗan majalissar tarayya ya yi nasara.
CIGABAN LABARI......
*_✨A CIKIN RAYUWA✨_*
_New story from the writer of 'A Sanadin Makwabtaka',_
_ZAINAB BATURE_
_Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai._
Page 14
Ƴar tafiya kaɗan Deen da Fahad suka yi daga parking space ɗin suka ƙaraso bakin babbar kofar shiga 6angaren, falo ne babba mai ɗauke da haɗaɗɗun kujeru royal kalar blue mai duhuwa, yadin kujerun na daga wurin da ake zama yana da zane-zanen kalolin blue mai haske da ruwan madara har da ɗan ratsin brown, akwai hadaddun labulaye masu inganci da babban carpet da ke shimfiɗe a tsakiyar kujerun saman tiles din da aka malala cikin falon, gaba daya komai na cikin falon kalolin su ya hau sun ƙawata cikinsa, akwai kayan kallo da na sauti da sauran na'urorin wuta da kayan ƙawata falo, akwai manyan hotunan ahalin gidan a wurare daban-daban, sosai falon ya haɗu tun daga kan ginin yadda ya tsaru kai ka ce ba falon tsohuwa ba.
Zaune a saman kujera mai mazaunin mutum biyu Hajiya Binta ce tana sanye da cotton ɗin doguwar riga irin wadda ta dace da yanayin da ake ciki na zafi, don ma akwai sanyin Ac ya karaɗe ilahirin cikin falon, kanta ta saka hula, a yanayin halitta bata da jiki sosai amman kuma ba siririya can bace, kana ganinta kasan ta manyanta sosai don a shekaru za ta yi saba'in da ɗoriya amman da gani da ɗan ƙwarinta, tana da kyawun fuska doguwa mai dauke da dogon hanci da madaidaicin baki, daga yanayin jikinta yadda yake ƙem zaka fahimci ta haɗa iri da fulani duk da yanayin fatarta ba fara ce, za a iya kiranta da wankan tarwaɗa.
Idanunta dake sanye cikin glasses na akan tv tana kallo, yayin da daga gabanta saman madaidaicin center table plate ne an yanka kankana a ciki, a hankali take ɗauka da fork tana kaiwa bakin ta, daidai zata kai kankana bakinta, sallamar da ta ji an yi ya sa ta kai idanunta saitin kofar shigowa tana amsawa, tana yin tozali da waɗanda suka shigo, da sauri ta mayar da kankanar saman plate tare da washe baki ta fara ƙoƙarin miƙewa, nufo cikin falon suka yi Deen ne a gaba yana ta sakar mata faffaɗan murmushi, yana zuwa gabanta ya ware mata hannuwa ta nufe shi da sauri ya rungumo ta yana murmushi, tare da lumshe idanuwan jin daɗin ganin kakar tashi da ya ɗauki lokaci bai gani ba, ɗagowa ta yi suna kallon juna da murmushi ta kai idanuwanta kan Fahad dake tsaye a gefe yana mata murmushi,
"Wannan wane irin zuwan bazata ne haka!" Ta faÉ—a tana washe baki,
"Yea, It's a suprise." Deen ya faɗa yana ƙoƙarin zama saman kujera tare da ita, kallon Fahad ta yi ta ce ya zauna mana ya yi tsaye, a saman kujera mai mazaunin mutum ɗaya ya zauna daga gefen su ya ɗaura duka hannuwansa a saman hannun kujeran,
"Ɗan ball, Allah Ya yi an samu an leƙo ƙasar tamu ke nan, ai na yi zaton ma sai ka ɗan kwana biyu ka huta zaka zo nan." Ta faɗa tana ta murmushin jin dadin ganin jikan nata da ta dade bata sanya shi a idanunta ba, sai dai ta waya ko a tv in tana kallon wasan shi, amsa ya bata da ba zai iya jurewa ba yana ƙasar ya bari har sai bayan wasu kwanaki sannan zai zo ya ga sweety ɗinshi da yake missing sosai, ta washe bakin jin dadin maganar.
"To ya ball ɗin, ai ina gani in kuna yi a tv, kana ƙoƙari sosai, ana ta ƙara ƙwarewa. Allah Ya ƙara taimakawa ya kuma tsare." A tare suka amsa mata da Amin,
"Kun ga da kun sanar da zuwan naku da an shirya maku sosai, yanzu ba wani shiri da aka yi maku, na san dai jiya mun yi sallama da Fahad akan zai tafi tarbarka amman ba wanda ya sanar da ni yau zaku taho nan, don haka sai ku yi haƙuri duk abun da ya samu da shi za a tarbe ku." Gaba ɗaya ɗan murmushi suka yi Deen ya ce mata no problem, mai aikinta Balaraba ta shiga ƙwala ma kira, fitowa ta yi daga cikin wata ƙofa ta nufo cikin falon, ƴar babbar mace ce jikinta sanye da riga da zane na atamfa, tana fitowa idanunta suka hango Deen nan ta shiga washe baki, ƙarasowa ta yi gaban su cike da girmamawa ta ce ma hajiya gata, kafin ta faɗi mata dalilin kiran nata ta kalli Deen cikin washe baki ta yi mashi sannu da zuwa tare da gaishe da shi, ya amsa mata da ɗan murmushi, gaishe da Fahad ta yi ya ɗaga mata kai,
A 6angaren Sapnah tuni ta kammala karatunta na medicine a india, daga baya kuma Maleek ya koma ƙasar America ya ci gaba da yin aiki da wani babban kamfanin fasaha. Sapna ba ƙaramin gata take samu a wurin Maleek ba, gaba ɗaya ta canza kana ganinta kasan hutu ya zauna mata idan ma aka ce maka a Nigeria aka haifeta anan ta taso har ta girma sai ka ƙaryata, sai dai har lokacin basu samu rabo ba ko batan wata bata ta6a yi ba, tun suna a India aka binciki lafiyar su gaba ɗaya inda aka tabbatar matsalar daga wurin Sapnah take, ba ƙaramar damuwa ta shiga ba amman shi Maleek sam bai nuna damuwar shi ba duk da yana son ya ga ya samu rabo, shine yake rarrashin ta yana nuna mata ko da a ce bazata ta6a haihuwa ba yana son ta a haka kuma za su ci gaba da rayuwa ba tare da wata matsala ba har ƙarshen rayuwar su, 6angaren danginta lokacin da suka ji zancen matsalar rashin haihuwar tata sun shiga damuwa sosai musamman Ammin su da kuma Jameela, Ammin har tambayarta ta rinƙa yi sun tabbatar an yi binciken sosai kuwa? Sapna ta tabbatar mata da ƙwararru ne suka yi binciken, sosai Ammin tasu ta shiga baƙin ciki don ba abun da ke a ranta face yanzu shike nan idan bata haihu ba Maleek na iya ƙara aure matar ta zo ta hayayyafa idan ya mutu su cinye gado, wannan dalilin ne ya saka ta damuwa sosai ta shiga bin bokaye ido rufe kan a yi mata aikin da Sapna zata samu ciki ta haihu, saidai kuma shiru Allah bai sa ta samu cikin ba.
Bayan wasu shekaru, abubuwa da dama sun faru, ciki har da yin ritaya da ambasada ya yi suka dawo gida Nigeria da zama a lokacin shima mahaifin Fahad an maido shi aiki Nigeria. Cikin iko na Allah bayan shekaru goma da auren Sapna da Maleek Allah ya azurta su da samun rabo inda ta haiho ya mace wato Basma. Bayan yin ritaya ɗin ambasada da shekara ɗaya shugaban ƙasa na lokacin ya sake bashi muƙamin ambasadan Nigeria a ƙasar Spain, yana riƙe da muƙamin ne bayan wasu shekaru ya kwanta ciwon da ya zamo ajalin shi ya rasu, ba ƙaramin alhini ahalin shi dama al'ummar garin Funtua suka shiga ba na rashin dattijon arziƙi. Rayuwa ta ci gaba da gudana yayin da arziƙin iyayen su Fahad ya ninninku, mahaifin su Deen ya ci gaba da gudanar da harkokin shi na siyasa inda daga baya ya sake tsayawa takarar kujerar ɗan majalissar tarayya ya yi nasara.
CIGABAN LABARI......
*_✨A CIKIN RAYUWA✨_*
_New story from the writer of 'A Sanadin Makwabtaka',_
_ZAINAB BATURE_
_Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai._
Page 14
Ƴar tafiya kaɗan Deen da Fahad suka yi daga parking space ɗin suka ƙaraso bakin babbar kofar shiga 6angaren, falo ne babba mai ɗauke da haɗaɗɗun kujeru royal kalar blue mai duhuwa, yadin kujerun na daga wurin da ake zama yana da zane-zanen kalolin blue mai haske da ruwan madara har da ɗan ratsin brown, akwai hadaddun labulaye masu inganci da babban carpet da ke shimfiɗe a tsakiyar kujerun saman tiles din da aka malala cikin falon, gaba daya komai na cikin falon kalolin su ya hau sun ƙawata cikinsa, akwai kayan kallo da na sauti da sauran na'urorin wuta da kayan ƙawata falo, akwai manyan hotunan ahalin gidan a wurare daban-daban, sosai falon ya haɗu tun daga kan ginin yadda ya tsaru kai ka ce ba falon tsohuwa ba.
Zaune a saman kujera mai mazaunin mutum biyu Hajiya Binta ce tana sanye da cotton ɗin doguwar riga irin wadda ta dace da yanayin da ake ciki na zafi, don ma akwai sanyin Ac ya karaɗe ilahirin cikin falon, kanta ta saka hula, a yanayin halitta bata da jiki sosai amman kuma ba siririya can bace, kana ganinta kasan ta manyanta sosai don a shekaru za ta yi saba'in da ɗoriya amman da gani da ɗan ƙwarinta, tana da kyawun fuska doguwa mai dauke da dogon hanci da madaidaicin baki, daga yanayin jikinta yadda yake ƙem zaka fahimci ta haɗa iri da fulani duk da yanayin fatarta ba fara ce, za a iya kiranta da wankan tarwaɗa.
Idanunta dake sanye cikin glasses na akan tv tana kallo, yayin da daga gabanta saman madaidaicin center table plate ne an yanka kankana a ciki, a hankali take ɗauka da fork tana kaiwa bakin ta, daidai zata kai kankana bakinta, sallamar da ta ji an yi ya sa ta kai idanunta saitin kofar shigowa tana amsawa, tana yin tozali da waɗanda suka shigo, da sauri ta mayar da kankanar saman plate tare da washe baki ta fara ƙoƙarin miƙewa, nufo cikin falon suka yi Deen ne a gaba yana ta sakar mata faffaɗan murmushi, yana zuwa gabanta ya ware mata hannuwa ta nufe shi da sauri ya rungumo ta yana murmushi, tare da lumshe idanuwan jin daɗin ganin kakar tashi da ya ɗauki lokaci bai gani ba, ɗagowa ta yi suna kallon juna da murmushi ta kai idanuwanta kan Fahad dake tsaye a gefe yana mata murmushi,
"Wannan wane irin zuwan bazata ne haka!" Ta faÉ—a tana washe baki,
"Yea, It's a suprise." Deen ya faɗa yana ƙoƙarin zama saman kujera tare da ita, kallon Fahad ta yi ta ce ya zauna mana ya yi tsaye, a saman kujera mai mazaunin mutum ɗaya ya zauna daga gefen su ya ɗaura duka hannuwansa a saman hannun kujeran,
"Ɗan ball, Allah Ya yi an samu an leƙo ƙasar tamu ke nan, ai na yi zaton ma sai ka ɗan kwana biyu ka huta zaka zo nan." Ta faɗa tana ta murmushin jin dadin ganin jikan nata da ta dade bata sanya shi a idanunta ba, sai dai ta waya ko a tv in tana kallon wasan shi, amsa ya bata da ba zai iya jurewa ba yana ƙasar ya bari har sai bayan wasu kwanaki sannan zai zo ya ga sweety ɗinshi da yake missing sosai, ta washe bakin jin dadin maganar.
"To ya ball ɗin, ai ina gani in kuna yi a tv, kana ƙoƙari sosai, ana ta ƙara ƙwarewa. Allah Ya ƙara taimakawa ya kuma tsare." A tare suka amsa mata da Amin,
"Kun ga da kun sanar da zuwan naku da an shirya maku sosai, yanzu ba wani shiri da aka yi maku, na san dai jiya mun yi sallama da Fahad akan zai tafi tarbarka amman ba wanda ya sanar da ni yau zaku taho nan, don haka sai ku yi haƙuri duk abun da ya samu da shi za a tarbe ku." Gaba ɗaya ɗan murmushi suka yi Deen ya ce mata no problem, mai aikinta Balaraba ta shiga ƙwala ma kira, fitowa ta yi daga cikin wata ƙofa ta nufo cikin falon, ƴar babbar mace ce jikinta sanye da riga da zane na atamfa, tana fitowa idanunta suka hango Deen nan ta shiga washe baki, ƙarasowa ta yi gaban su cike da girmamawa ta ce ma hajiya gata, kafin ta faɗi mata dalilin kiran nata ta kalli Deen cikin washe baki ta yi mashi sannu da zuwa tare da gaishe da shi, ya amsa mata da ɗan murmushi, gaishe da Fahad ta yi ya ɗaga mata kai,