← Book details A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 197

Sashe 5

A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Ba dole ya yi missing gida ba, almost 3 years fa rabon shi da 9ja." Mom ɗinsa ce ta faɗi hakan, nufar hanyar shiga cikin gidan suka yi hannuwansa ruƙe da na Sultan da Batool, wani irin katafaren falo ne da ya gaji da haɗuwa suka shigo, falon ƙarshe ne wurin tsaruwa akwai duk wani abu da za a samu a cikin falon masu kuɗin da suka amsa sunan masu kuɗi, to uba kuɗi ɗa kuma kuɗaɗe ko ban faɗa ba an san dole gidan ya kasance aljannar duniya ne. A ɗaya daga cikin rantsattsun saitin kujerun da ke a katafaren falon suka zauna wanda akwai saitin kujeru daban-daban na gani na faɗa sun kai ukku, bayan babban falon kuma akwai wasu ƙananun faluka a wasu bangarorin cikin gidan, sannan akwai matattakalar benen hawa sama wadda ita kanta yadda ta tsaru abun tsayawa kallo ce, daga bangaren da kayan kallo da na sauti suke akwai hotunan iyalan gidan da na sauran ƴan uwansu musamman masu muhimmanci a gare su, akwai hotunan dad ɗin su da aka yi mashi wasu zaune a majalissa wasu tare da shugaban ƙasa da sauran ƴan majalissa.

Kafin Deen ya zauna saida ya fara cire jacket din jikin shi Leemah da Batool suka cire mashi takalmansa, a saman kujera mai mazaunin mutum ukku suka zauna, Deen ne a tsakiya su Leemah da Sultan suka saka shi tsakiya ya ɗaura Batool a saman kafafunsa, a kujerar gefen shi mai mazaunin mutum ɗaya ƙaninsa mai bi mashi wato Omar ya zauna, daga ɗayan gefen saman kujerar dake fuskantar su mai mazaunin mutum biyu nan mom da dad ɗin su suka zauna,

Gaba ɗaya iyalan cikin farin cikin zuwan Deen ɗin suke saboda daɗewar da ya yi bai zo Nigeria ba, saidai su in sun je can su haɗu, da yake suna yawan zuwa saboda ƙanwar mom da abokin dad dake can. Maganar abinci mom ta yi masa wanda tuni an shirya mashi a dining room, ya ce mata a ƙoshe yake ya ci a cikin jirgi sai dai zuwa anjima, umarnin akawo mashi drink ta bada ta hanyar landline ɗin cikin falon, bada jimawa ba wata ƴar babbar mace ta shigo jikinta sanye da farar apron da hula irin na chef wato masu yin aikin abinci, chef Alima ke nan wadda ƴar dattijuwar bayerabiya ce, ita ce babba a cikin ƴan aikin gidan, bayan ta gaishe da su a nutse cike da taka tsan-tsan gudun masifar uwar ɗakin nata sanin bata raina abun masifa ta ɗaura luxury tray ɗin saman ƙaramin table dake a gefen kujerun, matso da taburin ta yi fuskarta ɗauke da faffaɗan murmushi ta ɗaura idonta kan Deen ta furta, "You are highly welcome sir." Da ɗan murmushi ya jinjina mata kai ya yi mata godiya, ƙokarin zuba mashi lemun ta fara, ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu ya ce ta bari ba yanzu zai sha ba in zai sha zai zuba, ɗagowa ta yi har lokacin da murmushi akan fuskarta wanda na farin cikin ganin shi ne domin suma duk suna son shi, idan ana yin ƙwallo da kungiyarsu suna cin albarkaci su zauna tare da iyalin gidan anan cikin babban falo su kalla, duk da a bangarensu na ƴan aiki akwai kayan kallon amman ta fi masu daɗi in suna kallo tare da iyalin, godiya ta yi ma shi kafin ta juya, saida ta tambayi mom ɗin cike da ladabi ko akwai wani abu da zata ƙara yi ta ɗan girgiza mata kai alamar babu sannan ta bar falon, hira suka shiga yi cike da nishaɗi,

"Ya dad da mom É—in ka na can?" Mahaifinsa ne yake tambayar shi Maleek da Safna,

"They are all doing well, suna gaishe da ku." Ya bashi amsa cikin turancin shi na yan can, hatta hausar shi ma in ya yi zaka ji yanayin sautin kamar turanci,

"How about Basma? Da kun zo tare ai." Mom din shi ta faÉ—a, yanayin fuskarsa ne ya É—an sauya ya bata amsa da basu samu hutun school ba,

"Bro amman zaka daɗe ko?" Leemah ce ta tambaya, a taƙaice ya bata amsa da ba zai daɗe ba sosai yana da wasanni da zai buga, kallon Omar ya yi ya tambaye shi ya karatunsa da yake yi a ƙasar Cyprus, amsa mashi ya yi da Alhamdulillah ya kusa komawa, kai Deen ya jinjina, maida idon shi ya yi kan Sultan ya tambaye shi miyasa basu je school ba, Leemah ce ta bashi amsa da saboda suna son su tarbe shi yasa suka ƙi zuwa. Saida Mom ta yi mashi magana kan juice da aka kawo masa sannan Leemah ta zuba mashi ya sha kaɗan, Dad ne ya yi mashi magana kan yakamata ya je ya kwanta ko ya huta gajiya, ya bashi amsa da ba wani gajiya ya yi ba sosai don ya kwanta a cikin jirgi. Suna nan zaune har aka fara kiran sallar azahar, tare da Dad da sauran ƙannansa maza suka tafi masallaci wanda yake a jikin gidan. Ko a masallacin bayan gama salla haka mutane sukai ta zuwa suna gaisawa da shi tare da yabon sa da kuma yi masa fatan alkhairi, wasu ma ba masu kallon ƙwallo bane amman saboda yadda yake burge mutane ya sa suke ta zumuɗin ganin sun gaisa da shi.

Bayan dawowar su daga masallaci suka zauna zaman cin abinci a dining room wanda shima ya tsaru sosai da tsadaddan dining table da kujerun sa guda takwas, akwai kuma wasu set ɗin daban a can bangare ɗaya, abinciccika ne birjik a saman teburin cikin luxury warmers da sauran abubuwan zuba abinci na ƙawa, masu aiki biyu ne a tsaye suke serving na su yayin da suke cin abincin a nutse, gaba ɗaya idanun ƴan aikin na akan Deen yadda yake cin abincin shi cikin aji da jan hankali.

Bayan gama cin abincin gaba dayan su suka taru a bangaren Deen dake a saman bene, bangaren na da girma akwai babban falo da ya ji kujeru leathers sai kayan kallo da kayan sauti, akwai manya-manyan hotuna wanda yawanci duk na shi ne a wurin ƙwallo sai na ƴan gidan su, akwai hoton abokin mahaifinsa wanda yake wurin shi wato Maleek tare da iyalinsa, sam falon baida hayaniya amman kana kallon kayan ciki zaka san masu tsada ne kuma ba gama garin kaya ne ba da zaka iya samu a ko ina, daga wurin bangon da kayan kallo suke wani irin design ɗin gini aka yi na gidajen da za a iya saka abubuwa, a cikin gidajen wasu daga cikin lambobin yabo da kyaututtuka masu daraja ne da ya samu a ciki gwanin burgewa, duk da ba wai iya su kaɗai bane kyaututtakan akwai tarin wasu a gidansa na London.

Zazzaune suke a saman kujerun cikin falon suna ta hira, mom ɗinsu ta canza kaya zuwa doguwar riga navy blue da ta ƙara fiddo da haskenta fayau, Dad din su ma jallabiya ce a jikin shi, su Leemah dai kayan da suka je tarbar shi ne airport ƙananun kaya riga da wando, haka ma Omar da Sultan duk ƙananun kayan ne a jikinsu, shima Deen ya canza kaya zuwa na shan iska riga mara hannuwa da gajeran wandonta da ya kai mashi gwiwa, murɗaɗɗun hannuwansa sun bayyana,

"Bro, mom ta ce nima ina gama secondary school zan koma wurin Aunty Safnah a can zan ci gaba da karatu." Leemah ce ta faÉ—a tana murmushi.

"When will you be done with secondary school?"
Deen dake kishingiÉ—e ya tambaya,

"Yanzu ina a S.S 2 going to 3 nan da one year zan gama." Kai ya jinjina kawai.

"Ni ina ganin ba gara ki yi karatunki anan ba, in kika tafi nesa Batool ba za ta ji daÉ—i ba ita kaÉ—ai ba Æ´ar'uwa mace."

Dad na rufe baki Mom ɗin su ta ce, "No, can zata tafi saboda Basma ta matsa tana son ta koma can itama ta samu sister, ita Batool ai autan mom ce muna tare ko yaushe ba za ta damu ba." Ta yi maganar idonta a kan Batool dake manne da jikin Deen, ta ɗage mata gira tare da tambayarta ai ba za ta damu ba tana tare da mom ko, kai Batool ta jinjina mata tana murmushi, shiru Daddynsu ya yi ya san kawai ita ke ra'ayin Leemah din ta je can, shi kuma yana tunanin hakan kamar bai kamata ba, ganin Deen na zaune a wurin su duk da yanzu yana da gidan kansa amman ai kusan a wurin su ya taso, kuma har yanzu in dai yana a London a gidan su yake zama, bayan wannan kuma shi bai son Leemah ta kasance tare da Basma su samu kusanci sosai don ya san yarinyar bata jin magana an sangartata da yawa, duk da ya san iyayenta suna ƙoƙari wurin tarbiyarta, sai dai kasancewar ita kaɗai Allah Ya basu ya sa take samun gata sosai.
Chapter 5 · 0% Book details