Sashe 23
A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"SubhanAllah! Wai Deen ɗin? To ya aka yi haka, a yadda na sani Deen yana jin maganarmu sosai har ma ya fi duk sauran ƴan'uwan shi, ba laifi yana yi mana biyayya..." Da sauri ta katse shi ta ce, "Idan ba akan ɗan lelensa ba ko? Ai ba a isa a yi mashi magana ba idan dai ta shafi Fahad ya ɗauka." Shiru dad ya yi yana kallonta, dama ya san tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi, matuƙar aka ce Fahad ya zo gidan dama aka zatai ta taƙalo abubuwa tai ta faman maganganu, yar ajiyar zuciya ya yi ya ce mata wani abu Fahad ɗin ya yi, kaman tana jira ta hau faɗa mashi ƙabli da ba'adi ta ce wai ta je ɗakin ta iske shi Deen a zaune har yana ɗan gyangyaɗi amman shi Fahad ɗin yana baje saman gadonsa sai sharar baccin shi yake, kuma ta san saboda Fahad ɗin na kwance ne yasa Deen bai kwanta ba ga gajiya a tattare da shi, shine daga ta kira shi a waje don kada ma Fahad ɗin ya ji ransa ya 6aci, ta yi mashi magana kan mi zai hana Fahad ya tafi part ɗin baƙi ya kwanta shima ya fi sakewa ya kwanta sosai, shine fa ya hau yin maganganu yana faɗin wai ta tsani Fahad bata son su a tare, shi dai ta bar su su yi zumuncin su...haka tai ta faɗi ma dad ɗin karya da gaskiya, bayan ta gama maganar shiru dad ya yi yana ɗan jinjina kai, sam bai yarda da maganganun nata ba, idan ba neman abun magana ba tun farko mi zai kaita part ɗin Deen a lokacin bayan ta san yana jiranta, sanin halinta in har bai goya mata baya ba to kuwa ba zai samu ta sauko ba har ta kula shi ya sa shi nuna mata bai ji dadin abun da Deen ya yi ba,
"Ban ji daɗin hakan da Deen ya yi ba, in baya ga abun shi ba don duk jin daɗin su saboda kada su takura ya sa kika bashi shawaran hakan ba, shine zai faɗi maganganu marasa daɗi haka. Ki ƙyale ni da shi, idan Allah Ya kaimu zan tsawatar masa kan hakan, ya kamata yana fahimtar abu yadda yake, kuma dama duk lokacin da Fahad ya zo gidan ba a part ɗin baƙin yake sauka ba..." Caraf ta amshe maganar,
"Wataƙil ai kai in ka gaya mashi ya fahimta, ni dama a koda yaushe tawa zafi take balle har a fahimce ni, kuma ni kaina ai har da ganin a can din yake sauka yasa na ce ya koma can ba wani abu ba...." Matsawa ya fara yi kusa da ita har lokacin yana riƙe da hannunta guda, ɗan janyo ta ya yi zuwa jikinsa farko ta ɗan toge, saida ya ɗan sa ƙarfi sannan ya rungumo ta ta gefe cikin kwantar da murya ya ce, "Kada ki damu gimbiyata, na ce zan tsawatar masa na san zai ji ba zai sake ba, kuma kin san Deen ba wasu shekaru ne da shi sosai ba kawai har da girman jiki, shiyasa wani abun ba zai yi nazari ba balle har ya fahimci abun da ake nuna masa." Tana jin ya faɗi haka ta samu damar amayar da wani abu daga cikin ainihin abun da ke a ranta,
"Har da hakan ya sa ni sam ban cika son ma yana samun kusanci da Fahad ɗin ba sosai wllh, ka dai san halin Fahad na shaye-shaye tsaf zai iya jan hankalin sa kan hakan tun da Deen ɗin yana ji da shi sosai yana ɗaukar maganar shi." Shiru ya yi yana juya maganarta a cikin ransa, ya san da Fahad na shaye-shaye don a can baya lokacin yana cikin yin karatu a Malysia abun ya fi yin ƙamari sosai, akwai lokacin da har saida ya samu matsala da karatunsa saboda hakan, har ta kai sun samu sa6ani tsakanin sa da mahaifinshi ya yi fushi da shi, har da shi cikin wanda suka yi kokarin ganin komai ya daidaita, amman a tunanin shi in da Fahad ɗin zai ja ra'ayin Deen har ya koya mashi shaye-shayen da tuni hakan ya faru tun da ba yau suke a tare ba,
"Ki kwantar da hankalinki, In sha Allahu hakan ma baza ta faru ba tun da ai ba yau suke tare ba, kuma yanzu sai a dade ma basu kasance tare ba. Mu gode ma Allah, domin Deen nutsattsen yaro ne, a irin sana'ar da yake yi ta yawo ƙasashe daban daban, yana haɗuwa da mutane iri-iri daga masu tarbiya zuwa marasa tarbiya, amman babu abun da ya canza na daga kyawawan halayensa. Duk da ba a tare muke da shi ba in da halinsa ya gurbata zamu sani, har Maleek na kan yi mashi magana da ta shafi halayen Deen saboda kula, amman koda yaushe yana nuna mani halayen shi lafiya lau ba matsala kuma yana yabon Deen ɗin kan yadda ya tsare mutunci bai bari ɗaukakar da Allah Ya yi mashi ta ruɗe shi ga aikata sabon Allah ba, kamar yadda da yawa waɗanda suka ɗaukaka suke yin amfani da damar wurin gurbata rayuwarsu. Mu ci gaba da yi mashi addu'ar neman shiriyar Allah har da ma shi Fahad ɗin, saboda zumuncin Allah da ƴan'uwantaka ba zai yuwu a raba su ba." Shiru ta yi ta ɗan tura baki tana ƙara jin bacin rai ganin haƙarta bata cimma ruwa ba, a rashin tunaninta yadda ta so dad din ya goya mata baya su raba tsakanin su.
"Don't worry my queen, na ce zan tsawatar masa ba zai sake ba ehen..." Ya yi maganar yana cusa fuskarsa tsakankanin wuyanta, ganin yana ƙoƙarin haɗe fuskokinsu ta yi saurin janye tata fuskar ta fara ƙoƙarin cire jikinta daga na shi, dakatawa ya yi daga abun da yake ƙoƙarin yi ya kalle ta fuskar shi da ɗan yanayin bacin rai, a marairaice ya ce mata miyasa take haka...fuska a yamutse ta ce mashi ya yi haƙuri an 6ata mata rai she isn't in the mood ya bari wani lokacin ko zuwa gobe da safe ne,
Bin ta ya yi da kallo yana jin ran shi ya fara ƙuna, ya gaji da irin wannan halin nata, sau da yawa haka take hana shi hakkinsa idan ya nema, ba dama ai mata abun da ranta zai baci shike nan sai ta hana shi hakkin shi kuma sau tari ita ke janyo a yi abun da ran nata zai baci, da yawan lokutta yana cutuwa da hakan kawai daurewa ya ke. A can baya akwai lokacin da ya gaji da irin wannan halin nata har ta kai ya kai ƙararta wurin Hajiyar shi wato Hajiyar ambasada domin ta bashi shawara, a lokacin ta nuna mashi zaman tare dama sai an yi haƙuri balle kuma an ɗauki shekaru ana tare an tara zuria, ta faɗi hakan ne don bata son shiga cikin sha'anin gidan yaranta amman sarai ta san yana cikin matsala a gidan shi don sam bai yi dacen mata ba, ba kamar yayansa Alhaji Sa'ad ba wato mahaifin Fahad. A lokacin ya roƙi hajiyar kan ta sama mashi wata wadda zai aura, ya yi hakan ne da tunanin idan ya je ma mom ɗin su Deen da zancen cewa mahaifiyarsa ce ta sa shi ya ƙara auren zata yi haƙuri ta bari, don ya sha yin yunƙurin cewa zai ƙara aure ƙarshe ba a wanyewa lafiya tsakanin su har sai ya janye maganar, hajiya ta so bijire ma buƙatar shi don ta san ba lalle a kwashe ta lafiya ba, ta nuna mashi idan yana son ƙara auren shi to ya je ya nemi matar da kan shi, a marairaice ya nuna mata saboda ya yi hakan da farko ya nemi auren Jameela da kansa, gashi yanzu bai jin daɗin zama da ita shiyasa yanzu yake son ta zaba mashi wataƙil ya dace, dama sai da suka ƙalubalanci auren shi da ita, tun farko saida Hajiya ta nuna mashi ga mata nan a familynsu waɗanda an san su an san asalin su amman ya bijire lokacin idon shi ya rufe mugun son Jameela yake kamar me. Aikuwa ƙarshe ba a kwashe ta lafiya ba bayan da hajiya ta nemo mashi mata a cikin family ɗinsu wadda bazawara ce haihuwarta ɗaya mijinta ya rasu, ko da mom ɗin su Deen ta ji aikuwa ta daka tsalle ta tuma ta ce wllh bai isa ba duk da ya faɗi mata hajiya ce ta sa shi, amman hakan bai sa ta saurare shi ba, ƙarshe ma sai cewa ta yi ai dama ƴan family ɗinsu sun tsane ta har da hajiyan shiyasa ta saka shi ya ƙara aure inda tana sonta baza ta sa ba Ƙarshe har Funtua ta je gidansu matar ta ja musu kunnen kada su sake su bari a yi auren in ba haka ba ta sha alwashin sai ta halaka ta in ya so itama ai mata hukunci, har gidan hajiya ta je itama ta gaggaya mata magana kan wai ta tsane ta shiyasa zata sa a yi mata kishiya, itama hajiyar sai da ta sha mata alwashin in dai aka sake aka yi auren to sai ta kashe yarinyar wllh. Lokacin jin abun da ta aikata dad ɗin ya ce ma hajiya sakinta zai yi, hajiyar ce ta hana ya yi hakan ta ce mashi ya haƙura da ƙara auren a lokacin ya bari sai ya fara gyara gidan shi tukunna. Ba don Allah Ya sa shi ɗin mai tsoron Allah bane yana tsoron aikata zina saboda sanin hukuncin ta da tuni ya afka ga aikata hakan, ba kamar yadda Allah Ya hore mashi yana da hali da matsayin da duk kalar macen da yake so za a kawo mashi har in da yake.
"Miyasa a duk lokacin da kika san ina tsananin buƙatar ki sannan zaki fara kawo wani uzuri mara dalili kina ja mani rai Jameela?" Rai a 6ace ya faɗi hakan tare da sakin jikinta, ita kanta ta san ran shi ya 6aci tun da har ya kira ta da ainihin sunanta.
"Ban ji daɗin hakan da Deen ya yi ba, in baya ga abun shi ba don duk jin daɗin su saboda kada su takura ya sa kika bashi shawaran hakan ba, shine zai faɗi maganganu marasa daɗi haka. Ki ƙyale ni da shi, idan Allah Ya kaimu zan tsawatar masa kan hakan, ya kamata yana fahimtar abu yadda yake, kuma dama duk lokacin da Fahad ya zo gidan ba a part ɗin baƙin yake sauka ba..." Caraf ta amshe maganar,
"Wataƙil ai kai in ka gaya mashi ya fahimta, ni dama a koda yaushe tawa zafi take balle har a fahimce ni, kuma ni kaina ai har da ganin a can din yake sauka yasa na ce ya koma can ba wani abu ba...." Matsawa ya fara yi kusa da ita har lokacin yana riƙe da hannunta guda, ɗan janyo ta ya yi zuwa jikinsa farko ta ɗan toge, saida ya ɗan sa ƙarfi sannan ya rungumo ta ta gefe cikin kwantar da murya ya ce, "Kada ki damu gimbiyata, na ce zan tsawatar masa na san zai ji ba zai sake ba, kuma kin san Deen ba wasu shekaru ne da shi sosai ba kawai har da girman jiki, shiyasa wani abun ba zai yi nazari ba balle har ya fahimci abun da ake nuna masa." Tana jin ya faɗi haka ta samu damar amayar da wani abu daga cikin ainihin abun da ke a ranta,
"Har da hakan ya sa ni sam ban cika son ma yana samun kusanci da Fahad ɗin ba sosai wllh, ka dai san halin Fahad na shaye-shaye tsaf zai iya jan hankalin sa kan hakan tun da Deen ɗin yana ji da shi sosai yana ɗaukar maganar shi." Shiru ya yi yana juya maganarta a cikin ransa, ya san da Fahad na shaye-shaye don a can baya lokacin yana cikin yin karatu a Malysia abun ya fi yin ƙamari sosai, akwai lokacin da har saida ya samu matsala da karatunsa saboda hakan, har ta kai sun samu sa6ani tsakanin sa da mahaifinshi ya yi fushi da shi, har da shi cikin wanda suka yi kokarin ganin komai ya daidaita, amman a tunanin shi in da Fahad ɗin zai ja ra'ayin Deen har ya koya mashi shaye-shayen da tuni hakan ya faru tun da ba yau suke a tare ba,
"Ki kwantar da hankalinki, In sha Allahu hakan ma baza ta faru ba tun da ai ba yau suke tare ba, kuma yanzu sai a dade ma basu kasance tare ba. Mu gode ma Allah, domin Deen nutsattsen yaro ne, a irin sana'ar da yake yi ta yawo ƙasashe daban daban, yana haɗuwa da mutane iri-iri daga masu tarbiya zuwa marasa tarbiya, amman babu abun da ya canza na daga kyawawan halayensa. Duk da ba a tare muke da shi ba in da halinsa ya gurbata zamu sani, har Maleek na kan yi mashi magana da ta shafi halayen Deen saboda kula, amman koda yaushe yana nuna mani halayen shi lafiya lau ba matsala kuma yana yabon Deen ɗin kan yadda ya tsare mutunci bai bari ɗaukakar da Allah Ya yi mashi ta ruɗe shi ga aikata sabon Allah ba, kamar yadda da yawa waɗanda suka ɗaukaka suke yin amfani da damar wurin gurbata rayuwarsu. Mu ci gaba da yi mashi addu'ar neman shiriyar Allah har da ma shi Fahad ɗin, saboda zumuncin Allah da ƴan'uwantaka ba zai yuwu a raba su ba." Shiru ta yi ta ɗan tura baki tana ƙara jin bacin rai ganin haƙarta bata cimma ruwa ba, a rashin tunaninta yadda ta so dad din ya goya mata baya su raba tsakanin su.
"Don't worry my queen, na ce zan tsawatar masa ba zai sake ba ehen..." Ya yi maganar yana cusa fuskarsa tsakankanin wuyanta, ganin yana ƙoƙarin haɗe fuskokinsu ta yi saurin janye tata fuskar ta fara ƙoƙarin cire jikinta daga na shi, dakatawa ya yi daga abun da yake ƙoƙarin yi ya kalle ta fuskar shi da ɗan yanayin bacin rai, a marairaice ya ce mata miyasa take haka...fuska a yamutse ta ce mashi ya yi haƙuri an 6ata mata rai she isn't in the mood ya bari wani lokacin ko zuwa gobe da safe ne,
Bin ta ya yi da kallo yana jin ran shi ya fara ƙuna, ya gaji da irin wannan halin nata, sau da yawa haka take hana shi hakkinsa idan ya nema, ba dama ai mata abun da ranta zai baci shike nan sai ta hana shi hakkin shi kuma sau tari ita ke janyo a yi abun da ran nata zai baci, da yawan lokutta yana cutuwa da hakan kawai daurewa ya ke. A can baya akwai lokacin da ya gaji da irin wannan halin nata har ta kai ya kai ƙararta wurin Hajiyar shi wato Hajiyar ambasada domin ta bashi shawara, a lokacin ta nuna mashi zaman tare dama sai an yi haƙuri balle kuma an ɗauki shekaru ana tare an tara zuria, ta faɗi hakan ne don bata son shiga cikin sha'anin gidan yaranta amman sarai ta san yana cikin matsala a gidan shi don sam bai yi dacen mata ba, ba kamar yayansa Alhaji Sa'ad ba wato mahaifin Fahad. A lokacin ya roƙi hajiyar kan ta sama mashi wata wadda zai aura, ya yi hakan ne da tunanin idan ya je ma mom ɗin su Deen da zancen cewa mahaifiyarsa ce ta sa shi ya ƙara auren zata yi haƙuri ta bari, don ya sha yin yunƙurin cewa zai ƙara aure ƙarshe ba a wanyewa lafiya tsakanin su har sai ya janye maganar, hajiya ta so bijire ma buƙatar shi don ta san ba lalle a kwashe ta lafiya ba, ta nuna mashi idan yana son ƙara auren shi to ya je ya nemi matar da kan shi, a marairaice ya nuna mata saboda ya yi hakan da farko ya nemi auren Jameela da kansa, gashi yanzu bai jin daɗin zama da ita shiyasa yanzu yake son ta zaba mashi wataƙil ya dace, dama sai da suka ƙalubalanci auren shi da ita, tun farko saida Hajiya ta nuna mashi ga mata nan a familynsu waɗanda an san su an san asalin su amman ya bijire lokacin idon shi ya rufe mugun son Jameela yake kamar me. Aikuwa ƙarshe ba a kwashe ta lafiya ba bayan da hajiya ta nemo mashi mata a cikin family ɗinsu wadda bazawara ce haihuwarta ɗaya mijinta ya rasu, ko da mom ɗin su Deen ta ji aikuwa ta daka tsalle ta tuma ta ce wllh bai isa ba duk da ya faɗi mata hajiya ce ta sa shi, amman hakan bai sa ta saurare shi ba, ƙarshe ma sai cewa ta yi ai dama ƴan family ɗinsu sun tsane ta har da hajiyan shiyasa ta saka shi ya ƙara aure inda tana sonta baza ta sa ba Ƙarshe har Funtua ta je gidansu matar ta ja musu kunnen kada su sake su bari a yi auren in ba haka ba ta sha alwashin sai ta halaka ta in ya so itama ai mata hukunci, har gidan hajiya ta je itama ta gaggaya mata magana kan wai ta tsane ta shiyasa zata sa a yi mata kishiya, itama hajiyar sai da ta sha mata alwashin in dai aka sake aka yi auren to sai ta kashe yarinyar wllh. Lokacin jin abun da ta aikata dad ɗin ya ce ma hajiya sakinta zai yi, hajiyar ce ta hana ya yi hakan ta ce mashi ya haƙura da ƙara auren a lokacin ya bari sai ya fara gyara gidan shi tukunna. Ba don Allah Ya sa shi ɗin mai tsoron Allah bane yana tsoron aikata zina saboda sanin hukuncin ta da tuni ya afka ga aikata hakan, ba kamar yadda Allah Ya hore mashi yana da hali da matsayin da duk kalar macen da yake so za a kawo mashi har in da yake.
"Miyasa a duk lokacin da kika san ina tsananin buƙatar ki sannan zaki fara kawo wani uzuri mara dalili kina ja mani rai Jameela?" Rai a 6ace ya faɗi hakan tare da sakin jikinta, ita kanta ta san ran shi ya 6aci tun da har ya kira ta da ainihin sunanta.