← Book details A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 197

Sashe 19

A Cikin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Bayan karrama shi shima ya yi godiya cikin turancin shi mai dadin sauraro, "....Thank you everyone for this incredible honor. I'm proud to represent Nigeria on the global stage, and I'm committed to continuing to make our country proud." Gaba ɗaya aka saka tafi, daga baya ya yi godiya ga iyayensa da ƴan'uwanshi kan goyon bayan da suke bashi da yadda suke ƙarfafa mashi guiwa ya bayyana hakan na daga cikin sirrin nasarorinsa, daga karshe ya yi godiya ta musamman ga ɗan'uwan sa mafi soyuwa a gare shi wato Fahad, ya bayyana shi a matsayin mutumin da ya fara fito mashi da baiwar shi ta ƙwallo, ya ce duk da da bai manta yadda ya sha wuya a hannunshi ba in suna yin ƙwallon a cikin compound ɗin gidansu ya yi ta sa mashi kafa yana kayar da shi wani lokacin har ya yi fushi ya ce ba zai ƙara yin ƙwallon da shi ba, ƙarshe haka zai lalla6a shi ya rarrashe shi su ƙara yi kuma hakan ba zai hana ya ƙara cutar shi ba, ya ce sai dai a yanzu ya fahimci ba cutar shi yake ba a lokacin yana molding nashi ne to become who he is today, yana bayanin yana yin ƴar dariya idanunsa akan Fahad da shima yake yin dariyar, haka ma sauran mutanen dake saurara wasu dariya ce akan fuskokinsu wasu kuma faffaɗan murmushi, idan ka cire mom da ta tsuke fuska sam bata ji daɗin yadda yake yabon Fahad ba a gaban jama'a har da wani kiran shi dan'uwan shi mafi soyuwa a gare shi, kalmar ta matuƙar ƙona mata rai. Bayan Deen ya gama jawabin nashi shima Fahad ya miƙe ya yi kalaman yabo kan irin ƙoƙari da jajircewar dan'uwan nasa tare da yi mashi fatan alkhairi, daga nan shima Deen ya ba wasu daga cikin manyan da suka haɗa mashi dinner ɗin kyautar jerseys ɗin kungiyarsu mai ɗauke da lamba 7 da yake bugawa, daga baya aka shiga ɗauke-ɗauken hotuna tare da shi.
Leemah na tsaye gefen Fahad bayan an yi masu hotuna da Deen wasu ƴan mata da suka gaji da haɗuwa suka ƙaraso wurin suna tafiya sai ka ce masu jin tausayin taka ƙasa, sun sha gayu da matsattsun dogayen rigunan lace ko mayafi babu da takalma masu uban tsini, kana ganin su ka ga ƴan mata zubin Abuja da alama ƴaƴan wasu manya ne a wurin, tun bayan da aka fara yin dinner ɗin hankalin ɗaya daga cikin su yake kan Deen don ba ƙaramin son shi take ba duk in za a yi kwallo da shi sai ta kalla, yau ne karo na farko da ta fara ganin shi a zahiri hakan yasa gaba ɗaya ya tafi da imaninta, a matuƙar ƙagare take da ta samu damar da zata yi magana da shi, ita kuwa ɗayar tun da ta ɗaura idanunta akan Fahad lokacin da Deen ke yabon shi ta ji ta afka kogin son shi, hakan ya sa suka yanke yin amfani da damar da suka samu ta yin hotuna da su sai su yi masu magana, cikin salon jan hankali budurwar dake son Deen ɗin ta ce mashi pls bari su yi hoto ya amsa mata da ok don duk wanda ya zo zai yi hoto da shi yana bashi dama duk da akwai jami'ai dake zagaye da shi don tsaron shi, lokaci guda Leemarh ta tamke fuska ganin ɗayar tana ma Fahad wani murmushi ta ce mashi tana son zata yi hoto da shi, aikuwa ba zato sai ji ya yi Leemah ta kama hannun shi ta riƙe gam, maido idanunsa ya yi kanta ya ga ta wani haɗe fuska tana farfari da idanuwa, ɗan murmushi kawai ya yi bai ce mata komai ba ya janye idanunsa, wani kallo budurwar ta yi ma Leemah don duk tana ganin abun da ke faruwa, fuskar budurwar ba yabo ba fallasa ta ce ma Leemah ta dan yi excuse nata za su yi hoto tare da Fahad, ta sakar mata wani kallo mai kamar harara ta ce mata ai bata hana ba ga wuri nan ta nuna mata gefenta, hakan ba ƙaramin ƙular da budurwar ya yi ba don sai ta ga ta ci mata fuska gashi tana ganinta ba sa'ar ta ba, ƙarshe dai dole a gefen Leemah ɗin ta tsaya aka yi masu hoton, sam Leemah ta hana kowace mace damar yin hoto da Fahad dole sai ta shiga tsakani, hakan ya sa wasu suka fara tunanin ko budurwarsa ce ita, ga shi ba yadda za a yi da ita don kana kallon fuskarta ba sai an faɗa maka ba zaka fahimci ƙanwar wanda aka yi taron domin shi ce don suna kama da Deen sosai, shi dai Fahad murmushi kawai yake ganin irin ƙarfin halinta.

Alhamdulillah, dinner ta tashi lafiya kowa yana cikin farin ciki musamman masoyan Deen waÉ—anda ya kasance yau ne rana ta farko da suka fara yin tozali da shi har sun samu damar yin magana da kuma yin hotuna da shi. Kan ka ce mi tuni hotunan dinner É—in sun karaÉ—e kafofin sada zumunta mutane nata tofa albarkacin bakin su, wasu daga cikin masoyan Deen da magoya bayan club É—in shi Æ´an Nigeria nata cika bakin wllh da sun san da za a yi dinner É—in sai sun je ko da bala'e kuma sai sun shiga.....

*_✨A CIKIN RAYUWA✨_*

_By Zainab Bature_

_Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai._

Page 7

......Sanye da rigar bacci robe irin mai buɗaɗɗen gaba wadda ake ɗaurewa tsawonta iya gwiwa Deen ya fito daga cikin walk-in closet ɗin shi ya nufo cikin ɗakin yana tafiya a nutse da alama ya gama yin shirin kwanciya sai ƙamshi jikinsa ke saki, gadonsa ya nufo ya zauna daga gefe idon sa akan Fahad dake a kishingiɗe shima ya yi shirin kwanciya jikinsa sanye da pajamas, waya ce riƙe a hannunsa yana lallatsawa, a hankali ya ɗago idanunsa ya sauke su akan Deen suka yi ma juna murmushi,

"Na yi zaton zan iske ka ka yi bacci saboda gajiyan dinner." Deen ya faɗa yana gyara zaman shi ya ɗan haye saman gadon kafarsa guda na a ƙasa, idon Fahad akan shi da ɗan murmushi ya ce, "Ba wani gajiya ai, kaine ma ke da gajiya an sha fama da mutane, yakamata by now ka yi bacci ka samu hutu sosai." Hannu Deen ya kai ya shafi yalwatacciyar sumarsa dake ta salƙi da alama a daren ma sai da aka gyara ta,

"Da muka dawo ya ɗauke ni time ina duba saƙonni, amman yanzu zan kwanta ɗin." Kai Fahad ya jinjina mashi.

"Gobe zamu tafi Funtua tare ina son je in ga sweety hajjanah." Ya faÉ—a da É—an faffaÉ—an murmushi,

"Da wuri haka, na yi tunanin zaka bari sai bayan kwana biyu in ka huta sosai." Fahad ya faÉ—a yana kallon shi.

"No, gara mu tafi kawai, ko na tsaya ba wani hutun da zan yi, I received a lot of invitations from different football clubs, duk suna son in je mu tattauna game da yadda suke wasa. So, ina son in yi honour wasu daga cikin invitations ɗin kafin na koma." Kai Fahad ya jinjina masa, jin alamar shigowar mutum ya sa gaba ɗaya suka kai idanunsu kan ƙofar shigowa, mom din Deen ce ta shigo cikin ɗakin jikinta sanye da jar silky doguwar rigar bacci da ta fito da ƙirarta sosai kanta ta yafa ƙaramin baƙin gyale, nufo cikin ɗakin ta yi tana tafiya cike da isa yanayin fuskarta a ɗan ɗaure, tun kallo ɗaya da Fahad ya yi mata ya ɗauke idonsa tare da mayar da su akan wayar hannunsa, idon Deen na akanta cikin ransa yana ayyana ko miye dalilin zuwan ta ɗakin shi a irin lokacin, daga gefen shi ta tsaya ta bi Fahad da wani irin kallon rashin arziƙi wanda shi bai ma san tana yi ba idon shi na akan wayarsa,

"Mom, baki yi bacci ba?" Deen ya tambaya yana kallonta, maido idonta ta yi kansa ta ƙara ɗaure fuskarta.

"Ai kai zan ma wannan tambayar, mi kake baka yi bacci ba, kai da ka kwaso gajiya amman wani ne a kwance saman gadon kai a zaune!" Yadda ta yi magana ya bayyana ta ji haushin ganin Fahad da ta yi a kwance saman gadon, kallo Deen ya bita da shi ya ɗan yamutsa fuska ganin ta kafe shi da ido alamar amsar shi take jira, kamar bazai ce komai ba don ya ji haushin maganarta sai dai gudun kada ta ƙara kwa6o wata baƙar maganar ya sa shi cewa,
Chapter 19 · 0% Book details